< 2 Chronicles 12 >
1 After Rehoboam was in complete control of his kingdom, he and all [the other people in] Judah stopped obeying the laws of Yahweh.
Bayan mulkin Rehobowam ya kahu kamar sarki ya kuma yi ƙarfi, shi da dukan Isra’ila suka yi biris da dokar Ubangiji.
2 As a result, after Rehoboam had been king for almost five years, Yahweh sent Shishak, the king of Egypt, [with his army] to attack Jerusalem.
Domin sun yi rashin biyayya ga Ubangiji, saboda haka Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima a shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam.
3 Along with his army he brought 1,200 chariots and 60,000 soldiers riding horses and a very large number of troops from two regions in Libya, and from Ethiopia.
Da kekunan yaƙi dubu ɗaya da ɗari biyu da kuma mahayan dawakai dubu haɗe da mayaƙan Libiyawa, Sukkatawa da kuma Kushawa waɗanda suka wuce ƙidaya suka zo tare da shi daga Masar,
4 They captured many of the cities in Judah that had walls around them, and they came as far as Jerusalem.
ya ci biranen katanga na Yahuda har zuwa Urushalima.
5 Then the prophet Shemaiah came to Rehoboam and the other leaders of Judah who had gathered in Jerusalem because they were afraid of [the army of] Shishak. Shemaiah said to them, “Yahweh says this: ‘You have abandoned me; so now I am abandoning you, to [allow you to be captured by the army of] Shishak.’”
Sai annabi Shemahiya ya zo wurin Rehobowam da kuma wajen shugabannin Yahuda waɗanda suka taru a Urushalima don tsoron Shishak, ya kuma faɗa musu, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Kun yi biris da ni; saboda haka, yanzu na bashe ku ga Shishak.’”
6 Then the king and the other Israeli leaders humbled themselves and said, “What Yahweh is doing to us is fair.”
Shugabannin Isra’ila da sarki suka ƙasƙantar da kansu suka ce, “Ubangiji mai adalci ne.”
7 When Yahweh realized that they had humbled themselves, he gave this message to Shemaiah: “Because they have humbled themselves, I will not allow them to be destroyed. Instead, I will soon rescue them. I will not use Shishak’s army to completely destroy the people of Jerusalem,
Sa’ad da Ubangiji ya ga sun ƙasƙantar da kansu, sai wannan maganar Ubangiji ta zo wa Shemahiya, “Tun da yake sun ƙasƙantar da kansu, to, ba zan hallaka su ba, amma zan cece su, ba zan kwararo fushina ta hannun Shishak a kan Urushalima ba.
8 but they will conquer Jerusalem and force the people there to do what Shishak wants them to do. As a result, the people of Jerusalem will learn [that it is better] to serve me than to serve the kings of other countries.”
Duk da haka za su zama bayinsa, don su san bambanci tsakanin yin mini bauta da kuma yin wa sarakunan sauran ƙasashe bauta.”
9 When Shishak’s [army] attacked Jerusalem, they took/carried away the valuable things that were in the temple of Yahweh and the valuable things that were in the king’s palace. They took everything [that was valuable], including the gold shields that Solomon’s [workers] had made.
Da Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima, sai ya kwashi ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan sarki. Ya kwashe kome da kome, har da garkuwoyin zinariyar da Solomon ya yi.
10 So King Rehoboam’s workers made bronze shields to be used instead of the gold ones and gave the bronze shields to the commanders of the men who guarded the entrance to his palace.
Sai sarki Rehobowam ya ƙera garkuwoyin tagulla a madadin na zinariya, ya sa su a hannun shugabannin matsara na mashigin gidan sarki.
11 After that, whenever the king went to the temple, the guards went with him, carrying those bronze shields. Then [when the king left, ] they would return the shields to the guards’ room.
Duk sa’ad da sarki ya tafi haikalin Ubangiji, masu tsaron sukan tafi tare da shi, suna riƙe da garkuwoyi, daga baya kuma su mai da su a ɗakin tsaro.
12 Because Rehoboam humbled himself, Yahweh stopped being angry with him and did not get rid of him. Instead, he caused good things to happen in Judah.
Gama Rehobowam ya ƙasƙantar da kansa, fushin Ubangiji ya bar shi, ba a kuwa hallaka shi ƙaƙaf ba. Tabbatacce an yi’yan abubuwa masu kyau a Yahuda.
13 King Rehoboam again was in complete control in Jerusalem and continued to be the king [of Judah]. He was 41 years old when he became the king. He ruled for 17 years in Jerusalem, which is the city that Yahweh had chosen from all the tribes in Israel to be the place in which people were to worship him.
Sarki Rehobowam ya kafa kansa daram a Urushalima, ya kuma ci gaba a matsayin sarki. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila wanda zai sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama ce, ita mutuniyar Ammon ce.
14 Rehoboam’s mother’s name was Naamah. She was from the Ammon people-group. Rehoboam did evil things because he did not try to find out what Yahweh wanted him to do.
Ya aikata mugunta domin bai sa zuciyarsa ga neman Ubangiji ba.
15 An account of all the things that Rehoboam did while he was the king, and lists of the members of his family, are in the scrolls written by the prophets Shemaiah and Iddo. The armies of Rehoboam and Jeroboam were constantly fighting each other.
Game da ayyukan mulkin Rehobowam, daga farko zuwa ƙarshe, ba a rubuce suke a tarihin Shemahiya annabi da Iddo mai gani wanda yake zancen zuriyoyi ba? Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
16 When Rehoboam died, he was buried in [the part of Jerusalem called] ‘The City of David’. Then his son Abijah became the king.
Rehobowam ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Abiya ɗansa kuma ya gāje shi a matsayin sarki.