< 2 Chronicles 11 >

1 When Rehoboam arrived in Jerusalem, he gathered 180,000 of the best soldiers from the tribes of Judah and Benjamin. He wanted them to fight against [the northern tribes of] Israel [and defeat them], in order that he could rule [all the tribes of] the kingdom again.
Sa’ad da Rehobowam ya iso Urushalima, ya tattara mayaƙa dubu ɗari takwas daga gidan Yahuda da Benyamin, don su yi yaƙi da Isra’ila su sāke mai da mulki wa Rehobowam.
2 But Yahweh spoke to the prophet Shemaiah and said this to him:
Amma wannan maganar Ubangiji ta zo ga Shemahiya mutumin Allah.
3 “Go and tell this to [Solomon’s son] Rehoboam, the king of Judah, and to all the Israeli people of the tribes of Judah and Benjamin:
“Faɗa wa Rehobowam ɗan Solomon sarkin Yahuda da kuma dukan Isra’ilawan da suke a Yahuda da Benyamin,
4 ‘Yahweh says that you must not go to fight against [the people of Israel; they are] your distant relatives. All of you must go home. What has happened is what Yahweh wanted to happen.’” [So Shemaiah went and told that to them, ] and they all heeded what Yahweh had commanded them to do, and they did not attack Jeroboam [and his soldiers].
‘Ga abin da Ubangiji ya ce kada ku haura don ku yi yaƙi da’yan’uwanku. Ku tafi gida kowannenku, gama wannan yi na ne.’” Saboda haka suka yi biyayya ga maganar Ubangiji suka kuma koma daga takawa don yaƙi da Yerobowam.
5 Rehoboam lived in Jerusalem, and his workers built walls around several of the cities and towns in Judah to protect them [against enemy attacks].
Rehobowam ya zauna a Urushalima ya kuma gina garuruwa don kāriya a cikin Yahuda.
6 In [the area that belonged to] the tribes of Judah and Benjamin they built walls around Bethlehem, Etam, Tekoa,
Betlehem, Etam, Tekowa,
7 Beth-Zur, Soco, Adullam,
Bet-Zur, Soko, Adullam,
8 Gath, Mareshah,
Gat, Maresha, Zif,
9 Adoraim, Lachish, Azekah,
Adorayim, Lakish, Azeka,
10 Zorah, Aijalon, and Hebron.
Zora, Aiyalon da Hebron. Waɗannan su ne garuruwan katanga a cikin Yahuda da Benyamin.
11 He also appointed an army commander in each of those cities and towns, and gave them supplies of food, olive oil, and wine [to keep in storage].
Ya ƙarfafa kāriyarsu ya kuma sa shugabannin mayaƙa a cikinsu, tare da tanadin abinci, man zaitun da kuma ruwan inabi.
12 He put shields and spears in all the cities and made them well-protected. So he continued to rule the tribes of Judah and Benjamin.
Ya sa garkuwoyi da māsu a cikin dukan biranen, ya kuma sa suka zama da ƙarfi. Saboda haka Yahuda da Benyamin suka zama nasa.
13 The priests and other descendants of Levi throughout Israel supported Rehoboam.
Firistoci da Lawiyawa daga dukan yankuna ko’ina a Isra’ila suka haɗa kai da shi.
14 The descendants of Levi [who lived outside the territory of Judah and Benjamin] abandoned their property and their pastureland, and they came to Jerusalem and [to other places in] Judah, because Jeroboam and his sons would not allow them to do the work of priests of Yahweh.
Lawiyawa suka ma bar makiyayansu da mallakarsu, suka zo Yahuda da Urushalima domin Yerobowam da’ya’yansa maza sun ƙi su a matsayin firistocin Ubangiji.
15 Instead, Jeroboam appointed the priests that he wanted to work [at the altars he commanded to be built] on the hilltops, [to offer sacrifices to] the idols that he commanded to be made [that resembled] goats and calves.
Yerobowam ya naɗa firistocinsa domin masujadan kan tudu da kuma domin gumakan nan na akuya da maraƙin da ya yi.
16 And people from every tribe in Israel who wanted to worship Yahweh, the God to whom the Israelis belonged, went with the descendants of Levi to Jerusalem to live there and to offer sacrifices to Yahweh, the God whom their ancestors [worshiped].
Waɗanda suke daga kowane kabilar Isra’ila waɗanda suka sa zuciya a kan neman Ubangiji, Allah na Isra’ila, suka bi Lawiyawa zuwa Urushalima don su miƙa hadayu ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
17 They caused the kingdom of Judah to be strong, and for three years they were happy that Solomon’s son Rehoboam was the king. During that time they conducted their lives [righteously] as David and Solomon had done previously.
Suka ƙarfafa mulkin Yahuda suka kuma goyi bayan Rehobowam ɗan Solomon shekaru uku, suna tafiya a hanyoyin Dawuda da Solomon a wannan lokaci.
18 Rehoboam married Mahalath. She was the daughter of David’s son Jerimoth, and her mother was Abihail, the daughter of Eliab and granddaughter of Jesse.
Rehobowam ya auri Mahalat,’yar Yerimot ɗan Dawuda wadda Abihayil’yar Eliyab ɗan Yesse ta haifa.
19 Rehoboam and Mahalath had three sons: Jeush, Shemariah, and Zaham.
Ta haifa masa’ya’ya maza. Yewush, Shemariya da Zaham.
20 Later Rehoboam married Maacah, the daughter of Absalom, and they had four sons: Abijah, Attai, Ziza, and Shelomith.
Sa’an nan ya auri Ma’aka’yar Absalom, wadda ta haifa masa Abiya, Attai, Ziza da kuma Shelomit.
21 Rehoboam loved Maacah more than he loved any other of his wives and slave wives. Altogether he had 18 wives and 60 slave wives, and 28 sons and 60 daughters.
Rehobowam ya ƙaunaci Ma’aka’yar Absalom fiye da sauran matansa da ƙwarƙwaransa. Duka-duka dai ya auri mata goma sha takwas da ƙwarƙwarai sittin, yana da’ya’ya maza ashirin da takwas da’ya’ya mata sittin.
22 Rehoboam appointed his son Abijah to be the leader of his [older and younger] brothers, because he wanted to appoint Abijah to be the next king.
Rehobowam ya naɗa Abiya ɗan Ma’aka yă zama babba yerima a cikin’yan’uwansa, don dai yă naɗa shi sarki.
23 He very wisely sent some of his other sons to other cities in the areas of the tribes of Judah and Benjamin, and to all the other cities that had walls around them. He gave them plenty of supplies and many wives.
Ya yi hikima, ya watsar da waɗansu’ya’yansa a dukan yankunan Yahuda da Benyamin, da kuma a dukan birane masu katanga. Ya ba su tanadi mai yawa ya kuma aurar musu mata masu yawa.

< 2 Chronicles 11 >