< 1 Samuel 4 >

1 And Samuel told to all the people of Israel the messages that God gave him. At that time the Israeli army went to fight against the army of the Philistine people. The Israeli army set up their tents at Ebenezer, and the Philistine army set up their tents at Aphek.
Duk sa’ad da Sama’ila ya yi magana dukan Isra’ila sukan saurare shi. Isra’ilawa suka fita yaƙi da Filistiyawa. Isra’ilawa suka kafa sansani a Ebenezer, Filistiyawa kuma a Afek.
2 The Philistine army attacked the Israeli army, and as the battle continued, the Philistines defeated the Israelis and killed about 4,000 of their soldiers.
Filistiyawa suka tunƙuro mayaƙansu domin su sadu da Isra’ilawa, yaƙi kuwa ya yi tsanani har Isra’ilawa suka sha kashi a hannun Filistiyawa. Filistiyawa suka kashe Isra’ilawa kusan mutum dubu huɗu a bakin dāgā.
3 When the remaining Israeli soldiers returned to their camp, the Israeli elders/leaders said, “Why did Yahweh allow the Philistine army to defeat us today? We should bring the chest that contains the Ten Commandments here from Shiloh, in order that Yahweh will go with us [when we go to the battle again, and] in order that our enemies will not defeat us again!”
Lokacin da mayaƙan suka komo sansani, dattawan Isra’ilawa suka yi tambaya suka ce, “Me ya sa Ubangiji ya sa muka sha ɗibga a hannun Filistiyawa? Bari mu kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Shilo. Domin yă tafi tare da mu yă ba mu nasara kan abokan gābanmu.”
4 So the soldiers did that. They sent some men to Shiloh, and those men brought back the chest that contained the Ten Commandments. [They thought that if they did that, Yahweh would help them. They believed that] Yahweh sat on a throne between the statues of winged creatures [that were on top of] the chest that Yahweh Almighty [had given them]. The two sons of Eli, Hophni and Phinehas, went with them.
Saboda haka mutanen suka aika waɗansu maza zuwa Shilo, suka kuwa tafi suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji Maɗaukaki wanda yake zaune tsakanin Kerubobi.’Ya’yan Eli biyun nan Hofni da Finehas suna wurin tare da akwatin alkawarin Ubangiji.
5 When the Israeli people saw [the men bringing] the box into their camp, they were so happy that they shouted loudly. They shouted so loudly that they made the ground shake!
Da aka shigo da akwatin alkawarin Ubangiji a cikin sansani, sai Isra’ilawa suka tā da babbar murya har ƙasa ta jijjiga.
6 The Philistines asked, “What are the people in the Hebrew camp shouting about?” Someone told them that they were shouting because the chest that contained the Ten Commandments of Yahweh had been brought to them.
Da jin wannan, Filistiyawa suka yi tambaya suka ce, “Me ke kawo wannan ihu mai ƙarfi haka a sansanin Isra’ilawa?” Da suka gane cewa akwatin alkawarin Ubangiji ne ya shiga sansanin,
7 Then the Philistines became very afraid. They said, “One of the Israelis’ gods has come into their camp [to help them] We are in big trouble now! Nothing like this has happened to us before!
sai Filistiyawa suka ji tsoro, suka ce, “Wani allah ya shiga cikin sansanin. Mun shiga uku! Ba a taɓa yin wani abu haka ba.
8 (Who can/Can anyone) save us from their powerful gods [RHQ]? They are the gods who struck the people of Egypt with many plagues [before the Israelis left Egypt and traveled] through the desert.
Kaiton mu! Wa zai kuɓutar da mu daga hannun waɗannan manyan alloli? Su ne allolin da suka buga Masarawa da irin annoba masu yawa a jeji.
9 You Philistine men, be courageous! Fight very hard! If you do not do that, [they will defeat us, and then] you will become their slaves, just like they have been our slaves previously!”
Ku yi ƙarfin hali, ku yi mazantaka, ku Filistiyawa, domin kada ku zama bayin Ibraniyawa kamar yadda suke a gare ku. Ku yi mazantaka, ku yi yaƙi.”
10 So the Philistine men fought very hard, and they defeated the Israelis. They killed 30,000 Israeli soldiers, and the other Israeli soldiers fled and ran away to their tents.
Saboda haka Filistiyawa suka yi yaƙi, Isra’ilawa kuwa suka sha ɗibga, kowane mutum kuwa ya gudu zuwa tentinsa. Kisan kuwa ya yi muni ƙwarai. Isra’ilawa sun rasa mayaƙa dubu talatin.
11 The Philistines captured the sacred chest, and they killed Eli’s two sons, Hophni and Phinehas.
Aka ƙwace akwatin alkawarin Ubangiji. Aka kuma kashe’ya’yan Eli biyu, Hofni da Finehas.
12 On that same day, one man of the tribe [descended from] Benjamin tore his clothes and threw dirt on his head [to show that he was very sad]. He ran from the place where the armies were fighting, and he arrived at Shiloh late [that afternoon].
A wannan rana wani mutumin Benyamin ya ruga da bakin dāgā ya shigo Shilo, taguwarsa a yage, kansa kuma a rufe da ƙasa.
13 Eli was waiting beside the road. [He wanted to hear news about the battle, and] he was also very anxious to know if anything bad had happened to God’s sacred chest. When the messenger arrived and told people what had happened, everyone in the town started to cry loudly.
Da ya iso sai ga Eli zaune a kujera kusa da hanya yana kallo, domin tsoron da yake da shi saboda akwatin alkawarin Allah. Da mutumin ya shigo a garin ya ba da labarin abin da ya faru sai dukan gari ya ruɗe da ihu.
14 Eli asked, “Why are they making all that noise?” The messenger ran over to Eli and told him the news.
Eli ya ji ihun ya yi tambaya ya ce, mene ne dalilin wannan ihu? Mutumin ya rugo wurin Eli,
15 At that time, Eli was 98 years old, and he was blind.
wanda yake da shekaru tasa’in da takwas da haihuwa, idanunsa kuma ƙarfi ya ƙare, baya iya gani.
16 The messenger said to Eli, “I have just come from where the armies were fighting. I left there earlier today.” Eli asked, “What happened?”
Mutumin ya gaya wa Eli cewa, “Shigowata ke nan daga bakin dāgā. Na kuɓuce daga can yau ɗin nan.” Eli ya ce, “Me ya faru da’ya’yana?”
17 The man replied, “The Philistines defeated our Israeli army. They killed thousands of our soldiers, and the others ran away. The Philistines killed your two sons, Hophni and Phinehas. They also captured God’s sacred chest.”
Mutumin da ya kawo labarin ya ce, “Isra’ilawa sun gudu a gaban Filistiyawa, mayaƙan kuma sun sha mummunar ɗibga.’Ya’yanka Hofni da Finehas su ma sun mutu. Aka kuma ƙwace akwatin alkawarin Allah.”
18 Eli was very old, and he was very fat; and when he heard what had happened to the sacred chest, he fell backward from his chair beside the town gate. His neck was broken and he died. He had led the Israeli people for 40 years before he died.
Da ya ambaci akwatin alkawarin Allah, sai Eli ya fāɗi da baya daga kujeransa kusa da ƙofa, wuyarsa ta karye, ya kuma mutu domin ya tsufa ƙwarai. Ya yi shugabancin Isra’ila shekaru arba’in.
19 The wife/widow of Eli’s son Phinehas was pregnant, and it was almost time for her to give birth to her baby. When she heard that God’s sacred chest had been captured and that her husband and her father-in-law were dead, her labor pains suddenly began. She quickly gave birth to a boy.
Matar Finehas, ɗansa tana da ciki a lokacin ta kuma kusa haihuwa. Sa’ad da ta ji labari cewa an ƙwace akwatin alkawarin Allah, ta kuma labarin surukinta da mijinta sun mutu, sai ta shiga naƙuda, ta kuma haihu. Amma naƙuda ta sha ƙarfinta.
20 The women who were helping her tried to encourage her by saying to her, “You have given birth to a son!” But she did not pay any attention [DOU] to what they said.
Da tana mutuwa, matan da suke lura da ita suka ce, “Kada ki karaya kin haifi ɗa namiji.” Amma ba tă ba da amsa ko tă kula ba.
21 She named the boy Ichabod, which means ‘no glory’, because she said, “[God’s] glory has departed from Israel.” She said that because God’s sacred chest had been captured and because her husband and her father-in-law had died.
Ta ba wa yaron suna Ikabod, ma’ana “Ɗaukaka ta rabu da Isra’ila”, domin an ƙwace akwatin alkawarin Allah, domin kuma mutuwar surukinta da na mijinta.
22 She said, “[God’s] glory has left Israel, because God’s sacred chest has been captured!” And then she died.
Ta ce, “Ɗaukaka ta rabu da Isra’ila, gama an ƙwace akwatin alkawarin Allah.”

< 1 Samuel 4 >