< 1 Samuel 29 >

1 The Philistia army gathered at Aphek [Valley, which is near Shunem]. The Israelis set up their tents at Jezreel [city, which was in the same valley].
Filistiyawa suka tattara dukan rundunoninsu a Afek. Isra’ila kuwa suka yi sansani kusa da maɓulɓular da take Yezireyel.
2 The kings of Philistia divided their men into groups; some groups had 100 soldiers and some groups had 1,000 soldiers. David and his men were marching behind, with King Achish.
Sa’ad da sarakuna Filistiyawa suke wucewa da rundunarsu na mutum ɗari-ɗari da na dubu-dubu. Dawuda da mutanensa suna biye a baya tare da Akish.
3 But the Philistia commanders asked, “What are these Hebrews [doing here, marching with us to battle]?” Achish replied, “[Their leader is] David. [He] previously worked for King Saul of Israel, but now he has been living near me for more than a year. During all the time since he left Saul, I have not seen/found that he has any faults.”
Komandodin Filistiyawa suka ce, “Waɗannan Ibraniyawa kuma fa?” Akish ya ce, “Wannan shi ne Dawuda hafsan Shawulu, sarkin Isra’ila. Yana nan tare da ni shekara guda ke nan. Ban kuwa taɓa samunsa da wani lahani ba tun daga ranar da ya bar Shawulu.”
4 But the Philistia army commanders were angry with Achish [for allowing David’s army to be going with them]. They said to him, “Send David [and his men] back to the city that you gave to him! We do not want him to go with us into the battle. [If he goes with us, ] we will have an enemy in our own midst! He would please King Saul by killing our own soldiers [RHQ]!
Amma komandodin Filistiyawa suka yi fushi, suka ce, “Ka sa mutumin nan yă koma zuwa wurin da ka ba shi yă zauna. Ba zai bi mu zuwa wurin yaƙi ba. Yana iya juya a kanmu lokacin yaƙin. Zai iya yin amfani da wannan zarafi yă ciccire kawunanmu don yă faranta wa maigidansa rai?
5 [Have you forgotten that] David is the one about whom the Israelis dance and sing, saying, ‘Saul has killed 1000 of our enemies, but David has killed 10,000 of them!’?”
Tuna fa, ba shi ne Dawuda ɗin da ake girmama da rawa da waƙoƙi ana cewa, “‘Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa dubbun dubbai ba’?”
6 So Achish summoned David, and said to him, “Just as surely as Yahweh lives, you have been loyal to me. I would like very much for you to fight along with my army. Since the day that you came to me, I have not found/seen that you have any faults. But the other Philistia rulers do not trust you.
Saboda haka Akish ya kira Dawuda ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, na amince da kai tun daga ranar da ka zo wurina har yă zuwa yau, ban same ka da wani laifi ba, na kuma yi farin ciki in sa ka a cikin sojojina don ka yi mini aiki. Amma masu mulki nawa ba su yarda da kai ba.
7 So all of you go back home, and I hope/desire that things will go well for you. I do not want you(sg) to do anything that the other rulers of Philistia will not be pleased with.”
Sai ka juya ka koma ka isa lafiya ba tare da ɓata wa masu mulkin Filistiyawa rai ba.”
8 David replied, “What wrong have I done? Since the day that I first came to you until today, have I done anything that you think is evil? Your majesty, why will you not allow me to go and fight against your enemies?”
Dawuda ya ce wa Akish, “Me na yi? Ka taɓa samun bawanka da laifi tun daga ranar da na zo har zuwa yanzu? Ina dalilin da ba zan tafi tare da kai in yaƙi maƙiyin ranka yă daɗe, sarki ba?”
9 Achish replied, “I know that you are as just as good as an angel from God. But the commanders of my army have said, ‘We will not allow David [and his men] to go with us into the battle.’
Akish ya ce, “A ganina kai marar laifi ne kamar mala’ikan Allah, duk da haka shugabannin sojojin Filistiyawa sun ce, ‘Ba zai tafi yaƙi tare da mu ba.’
10 So early tomorrow morning you and your men must leave. Get up as soon as it is light and leave.”
Ka tashi da sassafe, kai da bayin shugabanka da suka zo tare da kai. Da gari ya waye sai ku kama hanya.”
11 So David and his men got up early the following morning and returned to the area where the Philistia people lived. And the Philistia army went up to Jezreel.
Gari na wayewa tun da sassafe Dawuda da mutanensa suka tashi suka kama hanyar komawa ƙasar Filistiyawa. Filistiyawa kuwa suka haura zuwa Yezireyel.

< 1 Samuel 29 >