< 1 Samuel 20 >

1 David ran away from [the] Naioth [section] of Ramah [city]. He went to Jonathan and asked him, “What have I done [to displease your father]? What did I do that was wrong? Why is he trying to kill me?”
Sai Dawuda ya gudu daga Nayiwot a Rama ya je wurin Yonatan ya ce, “Me na yi? Wane laifi ne na yi? Ta wace hanya ce na yi wa mahaifinka laifi har da yake neman yă kashe ni?”
2 Jonathan replied, “My father is surely not trying to kill you! He always tells me before he does anything that he is planning. He tells me about important things and unimportant things that he plans to do. (Why would he refuse to tell me [if he were planning to kill me]?/I am sure that he would not refuse to tell me [if he were planning to kill you].) [RHQ] So what you are saying cannot be true.”
Yonatan ya ce, “Faufau, ba za ka mutu ba! Ka ji nan, mahaifina ba ya yin kome ba tare da ya shawarce da ni ba. Me ya sa ya ɓoye mini wannan? Ba zai yiwu ba.”
3 Then David solemnly declared this to Jonathan: “Your father knows very well that you and I are very good friends, so he says to himself, ‘I will not tell Jonathan [what I am going to do]. If I tell Jonathan, he will be upset/distressed, [and then he will tell David].’ But just as certain as Yahweh lives and you live, I am only one step away from being killed.”
Sai Dawuda ya rantse ya ce, “Mahaifinka ya san cewa, na sami tagomashi a gare ka, domin haka ba zai sanar maka da wannan ba, don kada yă baƙanta maka rai. Na rantse da Ubangiji, da kai kuma, taki ɗaya kaɗai ya rage tsakanina da mutuwa.”
4 Jonathan said to David, “I will do whatever you tell me to do.”
Sai Yonatan ya ce, “Duk abin da kake so in yi maka zan yi.”
5 David replied, “Tomorrow we will celebrate the Festival of the New Moon. I always eat with the king at that festival. But tomorrow I will hide in the field, and I will stay there for one night. I will stay there until the evening of the day after tomorrow.
Dawuda ya ce, “Gobe fa shi ne Bikin Sabon Wata, ya kamata in ci tare da sarki amma bari in tafi fili in ɓuya har jibi da yamma.
6 If your father asks why I am not there at the festival, say to him, ‘David requested me to allow him to go to his home in Bethlehem, where his family will offer the sacrifice that they offer [during this festival] every year.’
In mahaifinka bai gan ni ba, ka gaya masa cewa, ‘Dawuda ya nemi izinina domin yă hanzarta yă tafi garinsa a Betlehem saboda ana hadaya ta shekara-shekara don dukan zuriyarsa.’
7 If your father says ‘That is okay’, then I know I will be safe. But if he becomes extremely angry, you will know that he is determined to harm me.
In ya yi na’am, to, bawanka ya tsira. Amma in ka ga ya damu, to, ka tabbata ya yi niyya yă kashe ni.
8 Please be kind to me. Yahweh heard you when you made a solemn agreement with me [that you and I will always be loyal friends]. If I deserve to be punished [MTY], kill me yourself. I do not want [RHQ] you to allow your father to punish [IDM] me.”
Kai kuma, ka nuna alheri ga bawanka, gama ka riga ka yi yarjejjeniya da ni a gaban Ubangiji, in kuwa na yi laifi ne sai ka kashe ni da kanka. Don me za ka bashe ni ga mahaifinka?”
9 Jonathan replied, “I will never do that! But if I find out that my father is determined to harm/kill you, I will certainly warn you.” [RHQ]
Yonatan ya ce, “Labudda! In na ji ƙishin-ƙishin, cewa mahaifina yana neman yă kashe ka ashe, ba zan gaya maka ba?”
10 David asked him, “How will I find out if your father answers you harshly?”
Dawuda ya ce, “Wa zai gaya mini idan mahaifinka ya amsa maka da amsa marar daɗi?”
11 Jonathan replied, “Come with me. We will go out into the field.” So they went together out into the field.
Yonatan ya ce, “Zo mu fita zuwa fili.” Sai suka tafi tare.
12 There Jonathan said to David, “I promise this while Yahweh, the God whom we Israelis [worship], is listening: At this time the day after tomorrow, I will find out what my father [is thinking about you]. If he is saying good things about you, I will certainly send a message to you to tell that to you [RHQ].
Sai Yonatan ya ce wa Dawuda, “Na yi rantse da Ubangiji, Allah na Isra’ila cewa war haka jibi, zan yi ƙoƙari in ji daga mahaifina, idan ya yi magana mai kyau game da kai, zan gaya maka.
13 But if he is planning to hurt/kill you, I will enable you to know [IDM] that, and enable you to go away safely. I desire that Yahweh will punish me severely if I do not do that [for you]. I desire/hope that Yahweh will be with you [and help you] like he has helped my father.
Amma in mahaifina ya sa zuciya yă cuce ka, Ubangiji yă hukunta ni da hukunci mai tsanani in ban gaya maka ba, in kuma sa ka ka tafi lafiya. Ubangiji yă kasance tare da kai kamar yadda ya kasance da mahaifina.
14 But while I am still alive, please be kind to me in the same way that Yahweh is kind to me, and do not kill me [when you become king].
Amma ka nuna mini alheri marar ƙarewa iri ta Ubangiji dukan rayuwata don kada a kashe ni.
15 But [if I die, ] never stop being kind to my family, [even] after Yahweh has gotten rid of all your enemies all over the earth.”
Kada kuma ka yanke alherinka ga iyalina ko da Ubangiji ya hallaka dukan maƙiyin Dawuda a duniya.”
16 [David agreed]. So Jonathan made a solemn agreement with David. And he said, “I hope/desire that Yahweh will get rid of all your enemies.”
Saboda haka Yonatan ya yi yarjejjeniya da gidan Dawuda cewa Ubangiji yă kawo dukan maƙiyin Dawuda ga mutuwa.
17 And Jonathan requested David to repeat his solemn promise to be his close friend, because Jonathan loved David as much as he loved himself.
Yonatan kuwa ya sa Dawuda ya sāke tabbatar masa rantsuwansa game da abokantakarsa da shi, gama yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
18 Then Jonathan said, “Tomorrow we will celebrate the Festival of the New Moon. When you are not sitting at your place when we eat, my father will (miss you/see that you are not there).
Sai Yonatan ya gaya wa Dawuda cewa, “Gobe ne Bikin Sabon Wata, za a rasa ka, da yake kujerarka za tă kasance ba kowa a kai.
19 The day after tomorrow, in the evening, go to the place where you hid before. Wait by the pile of stones.
Jibi wajajen yamma, ka tafi wurin da ka ɓuya lokacin da wannan matsala ta fara, ka tsaya kusa da dutsen Etsel.
20 I will come out and shoot three arrows as though I were trying to shoot at a target. [The arrows will hit the ground] close to the pile of stones.
Zan harbi kibiya uku ta wajen, sai ka ce dai ina harbin baka.
21 Then I will send a boy to bring the arrows back to me. If you hear me say to him, ‘They are closer to me’, then as surely as Yahweh lives, you will know that everything is fine, [and that Saul will not kill you].
Sa’an nan zan aiki yaro in ce masa, ‘Je ka nemo kibiyoyin.’ In na ce masa, ‘Duba, kibiyoyin suna wannan gefen da kake, kawo su,’ sai ka fito, wato, tabbatacce muddin Ubangiji yana raye, ka tsira, ba wani hatsari.
22 But if I tell him, ‘The arrows are farther away’, you will know that you must leave immediately, because Yahweh wants you to run away.
Amma in na ce wa yaron, ‘Duba, kibiyoyin suna gaba da kai,’ sai ka tafi, gama Ubangiji ya sallame ka.
23 I hope/desire that Yahweh will watch you and me and enable us to never forget what we have promised each other.”
Game da al’amarin da muka tattauna da ni da kai kuwa, ka tuna fa Ubangiji ne shaida tsakanina da kai har abada.”
24 So David went and hid in the field. When the Festival of the New Moon started, the king sat down to eat.
Dawuda ya tafi ya ɓuya a fili. Sa’ad da ranar Bikin Sabon Wata ta zo, sarki ya zauna don yă ci.
25 He sat where he usually sat, close to the wall. Jonathan sat across from him, and Abner [the army commander] sat next to Saul. But no one was sitting in the place where David [usually sat].
Ya zauna a kujeransa inda ya saba zama kusa da bango yana fuskantar Yonatan, Abner kuma ya zauna kusa da sarki. Amma kujeran Dawuda ba kowa.
26 On that day, Saul did not say anything about David, because he was thinking, “Something must have happened that caused David to become unacceptable [to worship God].”
Shawulu bai ce kome ba a ranar domin ya yi tsammani wataƙila wani abu ya faru da Dawuda ya mai da shi marar tsarki, tabbatacce ba shi da tsarki.
27 But the next day, when David was not sitting at the place where he usually sat, Saul asked Jonathan, “Why has that son of Jesse not been here to eat with us yesterday and today?”
Amma kashegari, rana ta biyu ga wata, kujeran Dawuda kuma ba kowa, sai Shawulu ya ce wa ɗansa Yonatan, “Me ya sa ɗan Yesse bai zo cin abinci, jiya da yau ba?”
28 Jonathan replied, “David earnestly requested me that I permit him to go to Bethlehem.
Yonatan ya ce, “Dawuda ya nemi izinina don yă tafi Betlehem.
29 He said, ‘Please allow me to go, because our family is going to offer a sacrifice. My [older] brother insisted that I be there. So please allow me to go to be with my [older] brothers.’ [I allowed David to go], and that is the reason that he is not here eating with you.”
Ya ce, ‘Bari in tafi gama iyalinmu suna miƙa hadaya a gari,’yan’uwana kuwa sun gayyace ni in kasance a can. In na sami yardarka, bari in tafi in ga’yan’uwana.’ Dalilin ke nan da bai zo ci da sarki ba.”
30 Saul was (furious/very angry) with Jonathan. He yelled at him, “You stupid bastard [EUP]! I know that you are being loyal to that son of Jesse. By doing that, you will bring shame to yourself and to your mother.
Fushin Shawulu ya ƙuna a kan Yonatan, sai ya ce masa, “Kai shege ne, haihuwar banzan mace; ai, na san kana goyon bayan ɗan Yesse don ka wulaƙantar da kanka da mahaifinka.
31 As long as Jesse’s son is living, you will never become the king, and you will never rule over a kingdom! So now, summon David, and bring him to me. He must be executed!”
Muddin ɗan Yesse yana da rai a duniya, ba za ka kahu ba. Sarautarka kuma ba za tă kahu ba. Yanzu sai ka je ka kawo mini shi. Dole yă mutu.”
32 Jonathan asked his father, “Why should David be executed? What wrong has he done?”
Yonatan ya ce wa mahaifinsa, “Me ya sa zai mutu? Me ya yi?”
33 Then Saul threw his spear at Jonathan in order to kill him, [but the spear did not hit him]. So Jonathan knew that his father really wanted to kill David.
Amma Shawulu ya jefe shi da māshi don yă kashe shi. A nan ne Yonatan ya san lalle mahaifinsa ya yi niyya yă kashe Dawuda.
34 Jonathan was very angry, and he left the room. On that second day of the festival, he refused to eat anything. He was disgusted about what his father had done, and he was worried about David.
Yonatan ya tashi daga tebur cin abincin da fushi. A rana ta biyun kuwa bai ci abinci ba, gama yana baƙin ciki game da rashin kunyar mahaifinsa game da Dawuda.
35 The following morning Jonathan went out to the field to give a message to David, like he had agreed that he would do. He took a young boy with him.
Da safe Yonatan ya tafi domin yă sadu da Dawuda a fili. Ya tafi tare da wani ƙaramin yaro.
36 Jonathan said to the boy, “Run and find the arrows that I shoot.” The boy started running, and Jonathan shot an arrow ahead of the boy.
Ya ce wa yaron, “Yi ruga da gudu ka nemo kibiyoyin da na harba.” Da yaron ya ruga sai ya harba kibiya a gaba da shi.
37 When the boy ran to the place where the arrow hit the ground, Jonathan called out, “The arrow is further away!” [RHQ]
Da yaron ya isa wurin da kibiyan Yonatan ya fāɗi, Yonatan ya kira shi ya ce, “Kibiyan na gabanka fa.”
38 Then he shouted to the boy, “Act quickly; do not wait! Do not stop!” The boy picked up the arrow and brought it back to Jonathan.
Sai ya tā da murya ya ce, “Maza, yi sauri kada ka tsaya.” Yaron ya ɗauko kibiya ya kawo wa maigidansa.
39 But the boy did not understand the meaning of what Jonathan had said; only Jonathan and David knew.
(Yaron kuwa bai san kome game da wannan abu ba, sai Yonatan da Dawuda kawai.)
40 Then Jonathan gave his bow and arrows to the boy and told him, “Go back to the town.”
Yonatan ya ba wa yaron makaman ya ce, “Ka ɗauka ka koma gari.”
41 When the boy left, David came out from the south side of the pile of stones behind which he had been hiding. He went to Jonathan and bowed [in front of Jonathan] three times, with his face touching the ground. Then David and Jonathan kissed each other [on the cheek/neck], and they cried together. But David cried more than Jonathan.
Da yaron ya tafi, sai Dawuda ya tashi daga inda ya ɓuya kusa da tarin duwatsu, ya rusuna har sau uku. Sa’an nan suka sumbaci juna, suka yi kuka, Dawuda kuwa ya yi kuka sosai.
42 Jonathan said to David, “May things go well for you as you go. Yahweh has heard what we solemnly promised to always do for each other, and what we said that our descendants must do for each other.” Then David left, and Jonathan went back to the town.
Yonatan ya ce wa Dawuda, “Sauka lafiya, mun riga mun yi rantsuwar abokantaka da juna a cikin sunan Ubangiji cewa, ‘Ubangiji ne shaida tsakanina da kai, tsakanin zuriyarka da zuriyata har abada.’” Sai Dawuda ya tafi, Yonatan kuwa ya koma gari.

< 1 Samuel 20 >