< 1 Samuel 12 >
1 Then Samuel said this to all the Israeli people: “I have done everything that you told me to do, and I have given/appointed a king to rule you.
Sama’ila ya ce wa Isra’ilawa duka, “Na saurari abubuwan da kuka faɗa mini, na kuma naɗa muku sarki.
2 My own sons [are grown up and] with you now, but I have appointed Saul [instead of one of them], and he is now your leader. I am now old, and my hair is gray. I have been your leader ever since I was a boy.
Yanzu kuna da sarki a matsayin shugaba, ni kuwa na tsufa har da furfura, yarana maza kuma suna tare da ku. Na yi shugabancinku tun ina yaro.
3 Now tell me, while Yahweh is listening, and while the king whom he has chosen is listening: whose ox or donkey have I stolen [during all those years]? Whom have I cheated? Whom have I oppressed/treated badly? From whom have I accepted a bribe, in order that I would ignore [the evil things he had done]? If I have done any of those things, tell me, and I will pay back what I owe.”
Ga ni a gabanku. Idan na yi wani abin da ba daidai ba sai ku faɗa a gaban Ubangiji, da gaban sarkin da ya keɓe. Ko na taɓa ƙwace saniya ko jakin wani? Ko na taɓa cuce wani, ko in danne hakkinsa? Ko na taɓa cin hanci daga hannun ɗayanku? Idan na taɓa yi ɗaya daga cikin waɗannan, sai ku faɗa mini, zan kuwa mayar masa.”
4 They replied, “[No, ] you have never cheated anyone or oppressed anyone or accepted a bribe from anyone.”
Suka ce, “Ba ka cuci ko danne hakkin kowa ba, ba ka ƙwace kome daga hannun kowa ba.”
5 Then Samuel said, “Today Yahweh can testify, and the king whom you chose can testify, that I have not taken a bribe from anyone.” They replied, “Yes, Yahweh can say that he knows that is true.”
Sama’ila ya ce musu, “Ubangiji yă zama shaida a kanku, shafaffensa kuma yă zama shaida a wannan rana cewa ba ku same ni da wani laifin kome ba.” Suka ce, “I, shi ne shaida.”
6 Samuel continued by saying, “Yahweh is the one who appointed Moses and Aaron [to lead] our ancestors. He is the one who brought them out of Egypt. [And he is the one who will testify that what I am saying is true].
Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutane, Ubangiji ne ya naɗa Musa da Haruna suka fitar da kakanninku daga Masar.
7 Now while Yahweh is listening, stand here quietly while I accuse you [and tell you that your requesting a king instead of trusting Yahweh to lead you was wrong]. I will do that by reminding you of all the great miracles that Yahweh performed for you and your ancestors.
Yanzu ku tsaya nan zan yi fito-na-fito da ku da shaida a gaban Ubangiji kan dukan ayyuka masu alherin da Ubangiji ya aikata saboda ku da kakanninku.
8 [“Many years] after Jacob went to Egypt, our ancestors pleaded to Yahweh to help them. So Yahweh sent Moses and Aaron to them, and they led our ancestors out of Egypt, and eventually they settled in this land.
Bayan da Yaƙub da’ya’yansa suka shiga Masar suka yi kukan neman taimako daga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya aika musu da Musa da Haruna. Su ne suka kawo kakanni-kakanninku daga Masar suka zauna a nan.
9 “But our ancestors soon forgot about Yahweh, their God. So he allowed Sisera, the commander of the army from Hazor, to defeat them. He also allowed the Philistines and the army of the king of Moab to fight our ancestors and defeat them.
Amma suka manta da Ubangiji Allahnsu, shi kuma ya bashe su a hannun Sisera shugaban rundunar Hazor da kuma hannun Filistiyawa da sarkin Mowab wanda suka yi yaƙi da su.
10 Then our ancestors pleaded with Yahweh again to help them. They admitted, ‘Yahweh, we have sinned, and we have forsaken you. We have worshiped [idols that represent the god] Baal and [the goddess] Astarte. But if you rescue us from our enemies, we will worship you only.’
Suka yi kuka a gaban Ubangiji suka ce, “Mun yi zunubi mun bar Ubangiji, muka bauta wa Ba’al da Ashtarot. Amma ka cece mu yanzu daga hannun abokan gābanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
11 So Yahweh sent men such as Gideon, Barak, Jephthah, and me to save you. And as a result, you did not have to worry about any enemies attacking you.
Sai Ubangiji ya aiki Yerub-Ba’al da Bedan da Yefta da Sama’ila, ya cece ku daga hannun abokan gābanku a kowane gefe domin ku sami cikakken zaman lafiya.
12 “But now, when king Nahash of Ammon came [with his army] to attack you, [you were afraid. So], you [came to me, and] said, ‘We want a king to rule us,’ even though Yahweh was already your king!
Amma da kuka ga Nahash sarkin Ammonawa yana matsowa yă yaƙe, sai kuka ce mini, “Sam, muna so sarki yă shugabance mu.” Ko da yake Ubangiji Allahnku ne yake mulkinku.
13 So now, look, here is the king whom you have chosen. You asked for a king, and Yahweh has now appointed a king for you.
Yanzu ga sarkinku da kuka zaɓa wanda kuka nema, ga shi Ubangiji ya naɗa muku sarki.
14 If you will revere Yahweh and if you serve him, and if you listen to what he says and obey what he commands, and if you and the king who rules over you do what Yahweh your God wants you to do, [(things will go well for you all/Yahweh will bless you)].
In kuka ji tsoron Ubangiji, kuka bauta masa, kuka yi masa biyayya, ba ku kuwa ƙi bin umarninsa ba, in kuma ku da sarkin da yake mulkinku kun bi Ubangiji Allahnku, to, za ku zauna lafiya.
15 But if you do not listen to what Yahweh says, if you disobey what he commands, then he will punish [MTY] you all, just as he punished our ancestors.
Amma in ba ku yi biyayya ga Ubangiji ba, in kuma kuka ƙi bin umarnansa, fushinsa zai zauna a kanku.
16 “Now stand here quietly and see the great thing that Yahweh is about to do.
Yanzu ku tsaya tsit ku ga abin da Ubangiji ke dab da yi a gabanku.
17 You know that [RHQ] [it does not rain at this time of the year], during the time when you harvest wheat. But I will ask Yahweh to send thunder [and lightning] and rain today. When he does that, you will realize that Yahweh considers that you have done a very wicked thing by requesting a king.”
Ba lokacin yankan alkama ke nan ba? Zan roƙi Ubangiji yă aiko da tsawa da ruwan sama, za ku kuwa gane wace irin mugunta kuka yi a gaban Ubangiji sa’ad da kuka roƙa a ba ku sarki.
18 Then Samuel prayed to Yahweh, and Yahweh caused it to thunder [and lightning] and rain. So all the people became very afraid of Yahweh and of Samuel.
Sai Sama’ila ya roƙi Ubangiji, a ranar kuwa Ubangiji ya aiko da tsawa da ruwan sama. Dukan mutane suka ji tsoron Ubangiji da kuma Sama’ila.
19 They cried out to Samuel, “Pray for us! We have added to our previous sins by requesting a king! Pray to Yahweh, your God, in order that we will not die [because of having done that]!”
Dukan mutane suka ce wa Sama’ila, “Ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda bayinka, domin kada mu mutu, gama mun ƙara wa kanmu zunubi da muka roƙa a yi mana sarki.”
20 Samuel replied, “Do not be afraid! You have done this evil thing, but do not turn away from doing the things that Yahweh wants you to do. Instead, serve Yahweh wholeheartedly.
Sama’ila ya ce, “Kada ku ji tsoro.” Kun yi waɗannan mugunta duk da haka kada ku bar bin Ubangiji, amma ku bauta wa Ubangiji da dukan zuciyarku.
21 Do not abandon [Yahweh] and worship useless idols. They cannot help you or save you [from your enemies], because they are truly useless.
Kada ku bi alloli marasa amfani. Ba za su iya yi muku kome nagari ba, ba kuwa za su iya cece ku ba, gama ba su da amfani.
22 Yahweh decided to make us his people. So he will not abandon us people whom he has chosen, because he would injure his own reputation [of being completely faithful] if he did that.
Saboda suna mai girma da Ubangiji yake da shi, ba zai taɓa ƙin mutanensa ba. Gama Ubangiji ya ji daɗi da ya yi ku mutanensa.
23 But as for me, I have solemnly promised that I will not sin against Yahweh by ceasing to pray for you. And I will continue to teach you what things are good and right [for you to do].
Ni kam ba zai taɓa yiwu in yi wa Ubangiji zunubi ta wurin ƙin yin addu’a dominku ba. Zan koya muku hanyar da tana da kyau da ta kuma cancanta.
24 But you must revere Yahweh and serve him wholeheartedly. Never forget all the great things that he has done for you.
Amma ku amince za ku ji tsoron Ubangiji, ku bauta masa da aniya da dukan zuciyarku, kuna da manyan abubuwan da ya yi muku.
25 But if you keep doing wicked things, he will get rid of you and your king!”
Amma in kuka duƙufa cikin aikin mugunta da ku da sarkinku za a hallaka ku.