< 1 Kings 8 >

1 Solomon then summoned to Jerusalem all the elders of Israel, all the leaders of the tribes, and the leaders of the clans. He wanted them to join in bringing Yahweh’s Sacred Chest from Zion [Hill to the temple], where it was in the part of the city called ‘The City of David’.
Sai Sarki Solomon ya tattara dattawan Urushalima a gabansa, da dukan shugabannin kabilu, da shugabannin iyalan Isra’ilawa, domin su kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Sihiyona, Birnin Dawuda.
2 So all the Israeli leaders came to King Solomon during the Festival of [Living in Temporary] Shelters, in October.
Dukan mutanen Isra’ila suka tattaru a gaban Sarki Solomon a lokacin biki, a watan Etanim, wato, wata na bakwai.
3 When they had all arrived, the priests lifted up the Sacred Chest
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka iso, sai firistoci suka ɗauki akwatin alkawarin,
4 and brought it to the temple. The descendants of Levi [who assisted the priests] helped them to carry to the temple the Sacred Tent and all the sacred things that had been in the tent.
suka haura da akwatin alkawarin Ubangiji da kuma Tentin Sujada, da dukan kayayyaki masu tsarkin da suke cikinsa. Firistoci da Lawiyawa suka ɗauko su,
5 Then King Solomon and many of the Israeli people who had gathered in front of Yahweh’s Sacred Chest sacrificed a huge amount of sheep and oxen. No one was able to count the sacrifices [because there were so many].
sai Sarki Solomon da dukan taron Isra’ila da suka tattaru kewaye da shi a gaban akwatin alkawari, suka yi ta miƙa hadayar tumaki da bijimai masu yawa da ba a iya lissaftawa, ko ƙirgawa.
6 The the priests then brought the Sacred Chest into the Very Holy Place in the temple, and they placed it under the wings of the [statues of the] winged creatures.
Sa’an nan firistoci suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji inda aka shirya masa, can ciki cikin haikali, a Wuri Mafi Tsarki, aka kuma sa shi a ƙarƙashin fikafikan kerubobin.
7 The wings of those statues spread out over the Sacred Chest and over the poles by which it was carried.
Kerubobin sun buɗe fikafikansu a bisa wurin da akwatin alkawarin yake, suka inuwartar da akwatin alkawarin da sandunan ɗaukansa.
8 The poles were so long that the ends of the poles could be seen [by people who were standing] at the entrance to the Most Holy Place, but they could not be seen [by people standing] outside the temple. Those poles are still there.
Waɗannan sandunan sun yi tsawo har ana iya ganin bakinsu daga Wuri Mai Tsarki a gaban wuri mai tsarki na can ciki, amma ba a iya ganinsu daga waje na Wuri Mai Tsarki ba. Suna nan kuwa a can har wa yau.
9 The only things that were in the Sacred Chest were the two stone tablets that Moses had put there at Sinai [Mountain], where Yahweh made an agreement with the people after they left Egypt.
Ba kome a cikin akwatin alkawarin, sai dai alluna na dutse guda biyu waɗanda Musa ya ajiye a ciki tun a Horeb, inda Ubangiji ya yi alkawari da Isra’ilawa bayan sun fito Masar.
10 When the priests came out of the temple, [suddenly] it was filled with a cloud.
Sa’ad da firistoci suka janye daga Wuri Mai Tsarki, sai girgije ya cika haikalin Ubangiji.
11 It was the glory/radiance of Yahweh that filled the temple, with the result that the priests were not able to continue their work.
Firistocin kuwa ba su iya yin hidimarsu ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika haikalinsa.
12 Then Solomon prayed this: “Yahweh, you have placed the sun in the sky, but you have decided that you would live in very dark [clouds].
Sai Solomon ya ce, “Ubangiji ya ce zai zauna a gizagizai masu duhu;
13 I have built for you a magnificent temple, a place for you to live in forever.”
ga shi na gina haikali mai daraja dominka, inda za ka zauna har abada.”
14 Then, while all the people stood there, the king turned around and faced them, and he [asked God to] bless them.
Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsattsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
15 He said, “Praise Yahweh, the God whom we Israelis belong! By his own power he has done what he promised to give to my father David. What he promised was this:
Sa’an nan ya ce, “Ku yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannunsa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
16 ‘From the time that I brought my people out of Egypt, I have never chosen any city in Israel in which a temple should be built for my people to worship me there. But I chose you, David, to rule my people.”
‘Tun ran da na fitar da mutanena Isra’ila daga Masar, ban zaɓi wani birni a cikin wata kabilar Isra’ila a gina haikali domin Sunana yă kasance a can ba, amma na zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
17 [Then Solomon said], “My father David wanted to build a temple in order that we Israeli people could worship Yahweh our God there.
“Mahaifina Dawuda ya yi niyya a cikin zuciyarsa yă gina haikali saboda Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
18 But Yahweh said to him, ‘You have wanted to build a temple for me, and what you wanted to do was good.
Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Saboda yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka yi niyyar wannan a zuciyarka.
19 However, you are not the one [who I want] to build it. It is one of your sons, who [I want to] build a temple for me.’
Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikali, amma ɗanka, wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
20 And now Yahweh has done what he promised to do. I have become the king of Israel to succeed my father, and I am ruling my people, like Yahweh promised. I have [arranged for] this temple [to be] built for us Israelis to worship Yahweh, the God, to whom we Israelis belong.
“Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina, yanzu kuma ga shi na zauna a kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya yi alkawari, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
21 I have also provided a place [in the temple] for the Sacred Chest in which are the two stone tablets [on which are engraved the Ten Commandments of] the agreement that Yahweh made with our ancestors when he brought them out of Egypt.”
Na tanada wuri saboda akwatin alkawari, akwatin da ya ƙunshi alkawarin da Ubangiji ya yi da kakanninmu sa’ad da ya fitar da su daga Masar.”
22 Then Solomon stood in front of the altar which was facing the Israeli people who had gathered there. He spread out his arms toward heaven,
Sai Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji, a gaban dukan taron Isra’ila, ya ɗaga hannuwansa sama,
23 and he prayed, “Yahweh, the God whom we Israeli people [belong to/worship], there is no god like you up in heaven or down here on the earth. You solemnly promised that you would faithfully love us. And that is what you have done for us who earnestly do what you want us to do.
ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama can bisa, ko a ƙasa can ƙarƙashi, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna ga bayinka waɗanda suke cin gaba a hanyarka da dukan zuciyarsu.
24 You have done the things that you promised my father David, who served you [very well], that you would do. Truly, you promised to do these things for him, and today we see that by your power you have done them.
Ka kiyaye alkawarinka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina. Da bakinka ka yi alkawari, da hannunka kuma ka cika shi, yadda yake a yau.
25 So now, Yahweh, the God whom we Israelis [belong to/worship], please do the things that you promised my father that you would do. You told him that there would always be some of his descendants who would rule Israel, if they would conduct their lives as he did.
“Yanzu, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari ka cika wa bawanka Dawuda mahaifina alkawaran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza sun yi hankali cikin dukan abubuwan da suke yi, don su yi tafiya a gabana kamar yadda ka yi.’
26 So now, God of us Israeli people, cause what you promised to do for my father David, who served you [well], to happen.
Yanzu fa, ya Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi wa bawanka Dawuda mahaifina tă cika.
27 But God, you cannot really live on the earth. There is surely not enough space for you in the sky, or even in the heaven. So there is surely not enough space for you to live in this temple that my workers have built.
“Amma anya, Allah, za ka zauna a duniya? Sammai, har ma da saman sammai ba za tă iya riƙe ka ba, balle wannan haikalin da na gina!
28 But Yahweh, my God, please listen to me while I am praying to you this day,
Duk da haka ka ji addu’ar bawanka da kuma roƙonsa don jinƙai, ya Ubangiji Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka a wannan rana.
29 Please keep protecting this temple night and day. This is the place about which you have said, ‘I will always be there.’ I request that you listen to me whenever I turn toward this temple and pray.
Bari idanunka su buɗe, su fuskanci wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce, ‘Sunana zai kasance a can,’ saboda ka ji addu’ar bawanka in yana fuskantar wannan wuri.
30 I request that when I pray to you and your people pray to you while they turn toward this place, that in your home in heaven you will hear us and forgive us [for the sins that we have committed].
Ka ji roƙon bawanka da kuma na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a, suka fuskanci wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka, kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
31 If someone is accused of doing something wrong to another person, and they bring him to your altar outside this holy temple, and if he says, ‘I did not do that; may God punish me if I am not telling the truth,’
“Sa’ad da mutum ya yi abin da ba daidai ba ga maƙwabcinsa, an kuma bukace shi yă yi rantsuwa, sai ya zo ya rantse a gaban bagade a cikin haikalin nan,
32 then you listen from heaven, and decide who is telling the truth. Then punish the person who is guilty as he deserves to be punished, and declare that the other person is innocent.
sai ka ji daga sama, ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, ka hukunta mai laifi, ka mai da laifinsa a kansa, mai gaskiya kuma ka nuna shi marar laifi ne bisa ga gaskiyarsa.
33 And when your Israeli people are defeated by their enemies [in a battle] because they have sinned against you, [and if they are forced to go to some distant country, ] if they turn away from their sinful behavior and turn toward this temple and admit that you [have justly punished them], and if they plead [that you will forgive them],
“Sa’ad da abokan gāba suka ci mutanenka Isra’ila a yaƙi saboda sun yi maka zunubi, sa’ad da kuma suka dawo gare ka don su furta sunanka, suna addu’a suna roƙo gare ka a wannan haikali,
34 listen to them from heaven, and forgive your Israeli people for the sins that they [have committed], and bring them back to this land that you gave to our ancestors.
ka ji daga sama, ka gafarta zunubin mutanenka, ka kuma dawo da su ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
35 And when you do not allow any rain to fall on the land because your people have sinned against you, if they turn toward this temple and admit that you [have justly punished them], if they turn away from their sinful behavior and [humbly] pray to you,
“Sa’ad da sammai sun kulle, babu kuma ruwan sama domin mutane sun yi maka zunubi, sa’ad da suka yi addu’a suna fuskantar wannan wuri, suka kuma furta sunanka, suka juye daga zunubinsu domin ka hore su,
36 listen to them from heaven, and forgive your Israeli people for the sins [that they have committed]. Teach them the right way to conduct their lives. Then send rain on this land that you have given to your people to belong to them [permanently].
ka ji daga sama, ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace ta rayuwa, ka kuma aika da ruwan sama a ƙasar da ka ba wa mutanenka gādo.
37 And when the people of this land experience famines, or if there is a plague/illness that causes many people to become sick, or if [their crops are destroyed by] very hot winds or [by] mildew or [by] locusts or grasshoppers, or when their enemies surround any of their cities [in order to attack them], if any of those bad things happen to them,
“Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko burtuntuna, ko fumfuna, ko fāri, ko tsutsa, ko kuwa abokan gāba sun yi musu kwanto, a wani daga cikin biranensu, duk wata cuta, ko ciwon da ya zo,
38 when your Israeli people earnestly plead with you knowing that they are suffering because they [have sinned], and if they stretch out their arms toward this temple and pray,
in suka yi addu’a ko roƙo ta wurin wani daga cikin mutanenka Isra’ila, kowa ya san wahalar zuciyarsa, ya kuma buɗe hannuwansa yana fuskantar wannan haikali,
39 listen to them from your home in heaven, and forgive them, and help them. You are the only one who knows what people are thinking, so act toward everyone as they deserve,
sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi wani abu. Ka yi da kowane mutum bisa ga dukan abin da ya yi, tun da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan dukan mutane),
40 in order that your people may then have an awesome respect for you, all the years that they live in this land that you gave to our ancestors.
saboda su ji tsoronka a kowane lokacin da suke zaune a ƙasar da ka ba wa kakanninmu.
41 There will be some foreigners who do not belong to your Israeli people who have come here from countries far away because they have heard that you are very great and that you perform great miracles. If they come here to this temple to worship you and pray,
“Game da baƙo kuwa wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba, amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka,
gama mutane za su ji game da girman sunanka, da ƙarfin hannunka, da kuma hannunka mai iko, sa’ad da ya zo, ya yi addu’a yana fuskantar wannan haikali,
43 in your home in heaven, listen to their prayers, and do for them what they request you to do. Do that so that all the people-groups in the world will know about you and revere you, like we your Israeli people do. And then they will know that this temple that I have [caused to be] built to honor you, is where you [should be worshiped].
ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi dukan abin da baƙon ya tambaye ka, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka, su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, bari kuma su san cewa wannan gidan da na gina, ya amsa Sunanka.
44 And if you send your people to go to fight against their enemies, if they pray to you, wherever they are, if they turn toward this city that you have chosen and toward this temple that I have caused to be built for you,
“Sa’ad da mutanenka suka tafi yaƙi da abokan gābansu, a duk inda ka aike su, sa’ad da kuma suka yi addu’a ga Ubangiji suna fuskantar birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka,
45 listen in heaven to their prayers; listen to what they plead for you to do, and assist them.
ka ji addu’arsu da roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatansu.
46 [It is true that] everyone sins. So, if your people sin against you, and you become angry with them, you may allow their enemies to defeat them and capture them and take them away to their enemies’ country, even to countries that are far away.
“Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su, ka kuma ba da su ga abokin gāba, wanda ya kwashe su kamammu zuwa ƙasarsa, nesa ko kusa;
47 If that happens, while they are in those countries to which they were forced to go, if they sincerely repent and plead with you there saying ‘We have sinned and have done things that are very wicked,’
in suka canja zuciyarsu a ƙasar da aka riƙe su kamammu, suka tuba, suka kuma roƙe ka a ƙasar waɗanda suka ci su da yaƙi, suka ce, ‘Mun yi zunubi, mun yi abin da ba daidai ba, mun yi mugunta’;
48 if they very sincerely repent, and turn toward this land that you gave to our ancestors, and toward this city that you have chosen [to be the place where we should worship you], and toward this temple that I have [caused to be] built for you, and if they pray,
in sun juye gare ka da dukan zuciyarsu, da dukan ransu a ƙasar abokan gābansu waɗanda suka kwashe kamammu, suka yi addu’a gare ka, suka fuskanci wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, waje birnin da ka zaɓa, da kuma haikalin da na gina domin Sunanka;
49 then from your home in heaven listen to them while they plead [for your help], and assist them.
sai ka ji daga sama, mazauninka, ka ji addu’a da roƙonsu, ka kuma biya musu bukatansu.
50 Forgive them for all the sins that they [have committed] against you, and cause their enemies to be kind to them.
Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi; ka gafarta dukan laifofin da suka yi maka, ka kuma sa waɗanda suka ci su a yaƙi su ji tausayinsu.
51 Do not forget that the Israelis are your people; they are your special possession; you brought [our ancestors] out of Egypt where [they were greatly suffering as though] they were in a blazing furnace.
Gama su mutanenka ne, abin gādonka, waɗanda ka fitar daga Masar, daga tanderu mai narken ƙarfe.
52 I request that you always listen to your Israeli people and to me, their king, and heed their prayers whenever they call out to you [to help them].
“Bari idanunka su buɗe ga roƙon bawanka, ga roƙon mutanenka Isra’ila, bari kuma ka saurare su sa’ad da suka yi kuka gare ka.
53 You chose them from all the other people-groups in the world to belong to you, which is what you told Moses to tell them when you brought our ancestors out of Egypt.”
Gama ka ware su daga dukan al’umman duniya su zama abin gādonka, kamar yadda aka furta ta wurin bawanka Musa sa’ad da kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka ka fitar da kakanninmu daga Masar.”
54 After Solomon had finished praying and pleading to Yahweh [for his help], he stood up in front of the altar where he had been kneeling. He lifted up his arms.
Da Solomon ya gama dukan waɗannan addu’o’i da roƙe-roƙe ga Ubangiji, sai ya tashi daga gaban bagaden Ubangiji, inda ya durƙusa da hannuwansa a buɗe waje sama.
55 Then he [asked God to] bless all the Israeli people. [He prayed] loudly, saying,
Ya tashi ya kuma albarkaci dukan taron Isra’ila da babbar murya, yana cewa,
56 “Praise Yahweh, who has given us his people peace, like he promised that he would do. He has done every one of the good things that he promised to Moses, the man who served him [very well].
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda ya ba wa mutanensa hutu kamar dai yadda ya yi alkawari. Babu magana guda da ta kāsa cika cikin dukan alkawaransa masu kyau da ya yi ta wurin bawansa Musa.
57 I pray that our God will be with us like he was with our ancestors, and that he will never abandon us.
Bari Ubangiji Allah yă kasance tare da mu kamar yadda ya kasance da kakanninmu; kada yă taɓa rabu da mu, ko yă yashe mu.
58 I pray that he will cause us to loyally serve him, to conduct our lives as he wants us to, and to obey all his commandments and statutes and laws that he gave to our ancestors.
Bari yă juye zukatanmu gare shi, don mu yi tafiya a cikin dukan hanyoyinsa, mu kuma kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa, da kuma farillan da ya ba wa kakanninmu.
59 I pray that Yahweh our God will never forget these words that I have prayed, pleading for his help; I pray that he will think about them by day and by night. I pray that he will always help [us] Israeli people and me, giving us the things that we need day by day.
Bari kuma waɗannan kalmomina, waɗanda na yi addu’a a gaban Ubangiji, su yi kusa da Ubangiji Allahnmu, dare da rana, don yă biya bukatan bawansa da na mutanensa Isra’ila, bisa ga bukatan kowa,
60 If he does that, all the people-groups in the world will know that he is the only one who is God, and that there is no other one who is God.
saboda dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji, shi ne Allah, babu kuma wani.
61 I pray that you, [his people, ] will always be fully committed to Yahweh, and that you will obey all his statutes and commands, like you are doing now.”
Amma dole ku miƙa zukatanku ga Ubangiji Allahnmu, don ku rayu, ta wurin bin ƙa’idodinsa, ku kuma yi biyayya da umarnansa, kamar yadda kuke yi a wannan lokaci.”
62 Then the king and all the Israeli people who were there offered sacrifices to Yahweh.
Sai sarki da dukan Isra’ila, suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
63 They sacrificed 22,000 cattle and 120,000 sheep to maintain fellowship with Yahweh. Then the king and all the people dedicated the temple.
Solomon ya miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, shanu dubu ashirin da biyu, tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan Isra’ilawa suka keɓe haikalin Ubangiji.
64 On that day, the king also dedicated/set apart the middle part of the courtyard that was in front of the temple. Then he offered sacrifices that would be completely burned [in the courtyard], the offerings of grain and the fat of the animals that were sacrificed to maintain fellowship with Yahweh. They sacrificed them there because the bronze altar was not big enough for all those sacrifices to be burned on it [that day].
A wannan rana sarki ya tsarkake sashe na tsakiyar fili a gaban haikalin Ubangiji, a can kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa, hadaya ta gari, da kitsen hadaya ta salama, gama bagaden tagulla a gaban Ubangiji ya yi ƙanƙanta sosai da za a miƙa hadayun ƙonawa, hadayun hatsi, da kuma kitsen hadayun salama.
65 Then Solomon and all the Israeli people celebrated the Festival of [Living in Temporary] Shelters for seven days. There was a huge crowd of people there, some of whom had come from [distant places like] Hamath [in the far north] and the border of Egypt [in the far south].
Ta haka Solomon da dukan Isra’ila, wato, babban taro, suka yi bikin a lokacin. Mutane suka zo, tun daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar. Suka yi biki a gaban Ubangiji Allahnmu, kwana bakwai. Suka kuma ƙara kwana bakwai, kwanaki goma sha huɗu gaba ɗaya.
66 On the eighth day, Solomon sent the people to their homes. They all praised him and went home happy because of all the things that Yahweh had done to bless [King] David and his Israeli people.
A rana ta biye sai ya sallame mutane. Suka sa wa sarki albarka, sa’an nan suka watse zuwa gida, da farin ciki, da murna a zukatansu saboda kyawawan abubuwan da Ubangiji ya yi domin bawansa Dawuda, da kuma mutanensa Isra’ila.

< 1 Kings 8 >