< 1 Kings 4 >

1 Solomon was the king who ruled all of Israel,
Sai Sarki Solomon ya yi mulki a bisa dukan Isra’ila.
2 and these were his most important officials: Zadok’s son Azariah was the priest.
Waɗannan su ne manyan shugabanninsa. Azariya ɗan Zadok shi ne firist;
3 Shisha’s sons Elihoreph and Ahijah were the [official] secretaries. Ahilud’s son Jehoshaphat was the one who announced to the people the king’s decisions.
Elihoref da Ahiya,’ya’yan Shisha maza, su ne marubuta. Yehoshafat ɗan Ahilud, shi ne mai lura da takardu.
4 Benaiah was the commander of the army. Zadok and Abiathar were also priests.
Benahiya ɗan Yehohiyada, shi ne shugaban mayaƙa. Zadok da Abiyatar, su ne firistoci.
5 Nathan’s son Azariah was the administrator of the governors. Another of Nathan’s sons, Zabud, was a priest and the king’s chief advisor.
Azariya ɗan Natan, shi ne mai lura da shugabannin yanki. Zabud ɗan Natan, shi ne firist da kuma mai wa sarki shawara.
6 Ahishar supervised the servants who worked in the palace. Abda’s son Adoniram supervised the men who were forced to do work [for the government].
Ahishar, shi ne sarkin fada. Adoniram ɗan Abda, shi ne mai lura da aikin gandu.
7 Solomon appointed twelve men, one to govern [each of the regions] in Israel. They also were required to provide food for the king and all the others who lived and worked in the palace. Each man was required to provide from his own region the food for one month each year.
Solomon yana da gwamnoni yankuna goma sha biyu a bisa dukan Isra’ila, waɗanda suke tanaji abinci domin sarki da kuma gidan sarauta. Kowanne yakan tanada abinci na wata ɗaya a shekara.
8 Their names were: Ben-Hur, for the hilly area of the tribe of Ephraim.
Ga sunayensu, Ben-Hur, shi ne a ƙasar tudun Efraim;
9 Ben-Deker, for Makaz, Shaalbim, Beth-Shemesh, and Elon-Bethhanan [cities];
Ben-Deker, shi ne a Makaz, Sha’albim, Bet-Shemesh da Elon Bet-Hanan;
10 Ben-Hesed, for Arubboth and Socoh [towns] and the area near Hepher [town];
Ben-Hesed, shi ne a Arubbot (Soko da dukan ƙasar Hefer);
11 Ben-Abinadab, who was married to Solomon’s daughter Taphath, for all the Dor district;
Ben-Abinadab, shi ne a Nafot Dor (ya auri Tafat’yar Solomon);
12 Ahilud’s son Baana, for Taanach and Megiddo [towns], and all the region near Zarethan [city], and from Beth-Shan [city] south of Jezreel as far as Abel-Meholah [town] and Jokmeam [city];
Ba’ana ɗan Ahilud, shi ne a Ta’anak da Megiddo, da kuma dukan Bet-Sheyan biye da Zaretan ƙasa da Yezireyel, daga Bet-Sheyan zuwa Abel-Mehola a ƙetaren Yokmeyam;
13 Ben-Geber, for Ramoth [city] in [the] Gilead [region], and for the villages in Gilead that belonged to Jair, who was a descendant of Manasseh, and the Argob area in [the] Bashan [region]. There were 60 large towns in that region altogether, each town with a wall around it and bronze bars across the gates.
Ben-Geber, shi ne a Ramot Gileyad (Mazaunan Yayir ɗan Manasse a Gileyad suna a ƙarƙashinsa, haka ma yankin Argob a Bashan tare da manyan biranen sittin masu katanga da suke da ƙyamare na tagulla);
14 Iddo’s son Ahinadab, for Mahanaim [city east of the Jordan River];
Ahinadab ɗan Iddo, shi ne a Mahanayim;
15 Ahimaaz, who had married Solomon’s daughter Basemath, for [the territory of the tribe of] Naphtali;
Ahimawaz, shi ne a Naftali (ya auri Basemat’yar Solomon);
16 Hushai’s son Baana, for [the territory of the tribe of] Asher and for Aloth [town];
Ba’ana ɗan Hushai, shi ne a Asher da Bayelot;
17 Paruah’s son Jehoshaphat, for [the territory of the tribe of] Issachar;
Yehoshafat ɗan Faruwa, shi ne a Issakar;
18 Ela’s son Shimei, for [the territory of the tribe of] Benjamin;
Shimeyi ɗan Ela, shi ne a Benyamin;
19 Uri’s son Geber, for the Gilead region, the land that Sihon the king of the Amor people-group [formerly ruled], and the Bashan [area], which was the area that Og [formerly ruled]. [In addition to all those], Solomon appointed one governor for the [territory of the] tribe of Judah.
Geber ɗan Uri, shi ne a Gileyad (ƙasar Sihon sarkin Amoriyawa da kuma Og sarkin Bashan). Shi ne kaɗai gwamna a bisa yankin.
20 There were as many people in Judah and Israel as there are grains of sand [HYP] on the seashore. They [had plenty to] eat and drink and they were happy.
Mutanen Yahuda da na Isra’ila sun yi yawa sai ka ce yashi a bakin teku. Suka ci, suka sha, suka kuma yi farin ciki.
21 Solomon’s kingdom extended from the Euphrates [River in the northeast] to the Philistia area [in the west] and to the border of Egypt [in the south]. The [conquered] people in those areas paid taxes and were under Solomon’s control for the rest of his life.
Solomon kuwa ya yi mulki a bisa dukan masarautai daga Kogi zuwa ƙasar Filistiyawa, har zuwa iyakar Masar. Waɗannan ƙasashe sun yi ta kawo haraji, suka kuma zama bayin Solomon dukan kwanakin ransa.
22 [To feed the people in his palace and his guests] Solomon needed people to bring to him every day 150 bushels of fine flour and 300 bushels of wheat,
Tanajin Solomon na kowace rana su ne, garwa talatin na garin abinci,
23 ten cattle that were kept in stalls/barns, 20 cattle that were kept in pastures, 100 sheep, and (deer and gazelles and roebucks/three kinds of deer), and poultry.
shanun da aka yi kiwo a gida guda goma, shanu ashirin da suka ƙoshi daga kiwo, tumaki da awaki ɗari; ban da ƙishimai, bareyi, batsiyoyi, da kaji masu ƙiba.
24 Solomon ruled over all the area west of the Euphrates [River], from Tiphsah [city in the northeast] to Gaza [city in the southwest]. He ruled over all the kings in that area. And there was peace between his [government] and the [governments of] nearby countries.
Gama ya yi mulki a bisa dukan masarautai yamma da Kogi, daga Tifsa zuwa Gaza, aka kuwa sami zaman lafiya a kowane gefe.
25 All during the years that Solomon ruled, the people of Judah and Israel lived safely. Each family had its own grapevines and fig trees.
A kwanakin da Solomon yake raye, Yahuda da Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba, sun zauna lafiya, kowane mutum ya zauna a ƙarƙashin itacen inabi da na ɓaurensa.
26 Solomon had 4,000 stalls for the horses [that pulled] his chariots and 12,000 men who rode on horses (OR, in the chariots).
Solomon yana da rumfunan dawakai masu jan kekunan yaƙi, dubu huɗu, da kuma dawakai dubu goma sha biyu
27 His twelve governors supplied the food that King Solomon needed for himself and for all those who ate in the palace. Each governor supplied food for one month each year. They provided everything [LIT] that Solomon required.
Shugabannin yankuna, kowanne a watansa yakan yi tanajin abinci domin Sarki Solomon da kuma duk wanda ya zo teburin sarki. Sun tabbatar ba a rasa kome ba.
28 They also brought [stalks of] barley and wheat for the fast horses [that pulled the chariots] and for the [other work] horses. They brought it to the places where the horses were kept.
Kowa a cikinsu, bisa ga lokacin da aka ba shi, yakan kai hatsin sha’ir da ciyawa domin dawakan-kekunan yaƙi, da sauran dawakai a inda aka ajiye su.
29 God enabled Solomon to be extremely wise and to have great insight/understanding. He understood about more things than the number of grains of sand on the seashore [HYP].
Allah ya ba Solomon hikima da hangen nesa mai girma, da kuma fāɗin fahimta marar iyaka, kamar yashi a bakin teku.
30 He was wiser than all the wise men in Arabia and Mesopotamia and all the wise men in Egypt.
Hikimar Solomon ta fi hikimar mutanen Gabas, ta kuma fi dukan hikimar Masar girma.
31 Ethan from Ezrah and Heman and Calcol and Darda and the sons of Mahol were [considered to be] very wise, but Solomon was wiser than all of them. People in all the nearby countries heard about Solomon.
Ya fi kowane mutum hikima, har da Etan dangin Ezra ma. Yana da hikima fiye da Heman, Kalkol da Darda,’ya’yan Mahol maza. Sunansa ya bazu ko’ina a ƙasashen da suke kewaye.
32 He composed/wrote 3,000 (proverbs/wise sayings) and more than 1,000 songs.
Ya yi karin magana dubu uku. Waƙoƙinsa kuwa sun kai dubu ɗaya da biyar.
33 He talked about various kinds of plants, from the [huge] cedar trees in Lebanon to the [tiny] hyssop plants that grow in cracks in walls. He also talked about wild animals and birds and reptiles and fish.
Ya yi magana a kan rayuwar itatuwa, daga al’ul na Lebanon zuwa hizzob da yake girma a bangaye. Ya kuma yi koyarwa game da dabbobi, da tsuntsaye, da abubuwa masu rarrafe, da kuma kifi.
34 People came from all over the world to hear the wise things that Solomon said. Many kings sent men to listen to him [and then return and tell them what Solomon said].
Mutane suka yi ta zuwa daga ƙasashe dabam-dabam don su ji hikimar Solomon. Sarakuna daga ko’ina a duniya, sun ji labarin hikimarsa, suka kuma aika da mutane don su ji shi.

< 1 Kings 4 >