< 1 Kings 22 >

1 For almost three years there was no war between Syria and Israel.
Aka yi shekaru uku ba a yi yaƙi tsakanin Aram da Isra’ila ba.
2 Then King Jehoshaphat, who ruled Judah, went to [visit] King Ahab, who ruled Israel.
Amma a shekara ta uku, Yehoshafat sarkin Yahuda ya gangara don yă ga sarki Isra’ila.
3 [While they were talking, ] Ahab said to his officials, “Do you realize that the Syrians are still occupying our city of Ramoth in [the] Gilead [region]? And we are doing nothing to retake that city!”
Sarkin Isra’ila ya ce wa shugabanninsa, “Ba ku san cewa Ramot Gileyad namu ne ba, duk da haka ba mu yi kome ba don mu sāke karɓanta daga sarkin Aram?”
4 Then he turned to Jehoshaphat and asked, “Will your [army] join my [army] to fight against the people of Ramoth [and retake that city]?” Jehoshaphat replied, “[Certainly] I [will do whatever] you [want], and you may command my troops. You may take my horses into battle, also.”
Saboda haka ya tambayi Yehoshafat, ya ce, “Za ka tafi tare da ni don in yi yaƙi da Ramot Gileyad?” Yehoshafat ya amsa wa sarkin Isra’ila, ya ce, “Ni ma kamar ka ne, mutanena kuwa kamar mutanenka, dawakaina kamar dawakanka.”
5 Then he added, “But we should ask Yahweh first, to find out what he wants us to do.”
Amma Yehoshafat ya ce wa sarkin Isra’ila, “Da farko mu nemi nufin Ubangiji.”
6 So Ahab summoned about 400 of his prophets together, and he asked them, “Should my [army] go to fight the people in Ramoth and retake that city, or not?” They answered, “Yes, go [and attack them], because God will enable your [army] to defeat them.”
Saboda haka sarkin Isra’ila ya tattara annabawa, kamar ɗari huɗu, ya tambaye su, “In kai yaƙi a kan Ramot Gileyad, ko kada in kai?” Suka amsa, “Ka tafi, gama Ubangiji zai ba ka ita a hannunka.”
7 But Jehoshaphat asked, “Is there no prophet of Yahweh here whom we can ask?”
Amma Yehoshafat ya yi tambaya, ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu tambaya?”
8 The King of Israel replied, “There is one man we can talk to. We can ask him if he can find out what Yahweh wants. His name is Micaiah; he is the son of Imlah. But I hate him, because when he (prophesies/tells what God says to him) he never says [that] anything good [will happen] to me. He always predicts [that] bad things [will happen to me].” Jehoshaphat replied, “King Ahab, you should not say that!”
Sarkin Isra’ila ya amsa wa Yehoshafat, ya ce, “Akwai mutum guda har yanzu wanda ta wurinsa za mu iya nemi nufin Ubangiji, amma na ƙi jininsa domin bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni ba, sai dai mummuna kullum. Shi ne Mikahiya ɗan Imla.” Yehoshafat ya ce, “Kada sarki ya ce haka.”
9 So the king of Israel told one of his officers to summon Micaiah immediately.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya kira ɗaya daga cikin shugabanninsa ya ce, “Kawo Mikahiya ɗan Imla nan take.”
10 The king of Israel and the king of Judah were wearing their (royal robes/robes that showed that they were kings). They were sitting on thrones at the place where people threshed grain, near the gate of Samaria [city]. All of Ahab’s prophets were standing in front of the kings, (prophesying/predicting what was going to happen).
Saye da rigunansu na sarauta, sarkin Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suna zama a kujerun sarautarsu a masussuka ta mashigin ƙofar Samariya, tare da dukan annabawa suna ta annabci a gabansu.
11 One of them, whose name was Zedekiah, the son of Kenaanah, had made from iron [something that resembled] horns of a bull. Then he proclaimed [to Ahab], “This is what Yahweh says: ‘With horns like these your [army] will keep attacking the Syrians [like a bull attacks another animal] [MET], until you completely destroy them!’”
Zedekiya ɗan Kena’ana kuwa ya yi ƙahonin ƙarfe ya kuma furta, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Da waɗannan za ka tunkuyi Arameyawa har su hallaka.’”
12 All the [other] prophets [of Ahab] agreed. They said, “Yes! If you go up to attack Ramoth [city] in [the] Gilead [region], you will be successful, because Yahweh will enable you to defeat them!”
Dukan sauran annabawan suka yi annabci iri abu ɗaya. Suka ce, “Ka yaƙi Ramot Gileyad, ka kuma yi nasara, gama Ubangiji zai ba da ita cikin hannun sarki.”
13 Meanwhile, the messenger who went to summon Micaiah said to him, “Listen to me! All the other prophets are predicting that the king’s army will defeat the Syrians. So be sure that you agree with them and say (what will be favorable/that the king’s army will be successful).”
Ɗan aikan da ya je yă kawo Mikahiya, ya ce masa, “Duba, sauran annabawa suna maganar nasara wa sarki, sai ka ce mutum guda. Bari maganarka tă yarda da tasu, ka kuma yi maganar alheri.”
14 But Micaiah replied, “As surely as Yahweh lives, I will tell him only what Yahweh tells me to say.”
Amma Mikahiya ya ce, “Na rantse da Ubangiji mai rai, zan faɗa masa kawai abin da Ubangiji ya faɗa mini.”
15 When Micaiah came to Ahab, Ahab asked him, “Micaiah, should we go to fight against [the people of] Ramoth, or not?” Micaiah replied, “Sure, go! Yahweh will enable your army to defeat them!”
Da suka kai, sai sarki ya tambaye shi, ya ce, “Mikahiya, mu kai yaƙi a kan Ramot Gileyad, ko kada mu kai?” Ya amsa ya ce, “Yaƙe ta, za ka kuwa yi nasara, gama Ubangiji zai ba da ita cikin hannun sarki.”
16 But King Ahab [realized that Micaiah was (lying/being sarcastic), so he] said to Micaiah, “I have told you [RHQ] many times that you must always tell only the truth when you say what Yahweh [has revealed to you]!”
Sai sarki ya ce masa, “Sau nawa ne zan sa ka rantse cewa ba za ka faɗa mini kome ba sai dai gaskiya a cikin sunan Ubangiji?”
17 So Micaiah said to him, “[The truth is that] in a vision I saw all the troops of Israel scattered on the mountains. They seemed to be like sheep that did not have a shepherd. And Yahweh said, ‘Their master has been killed. So tell them all to go home peacefully.’”
Sa’an nan Mikahiya ya amsa, “Na ga dukan Isra’ila a warwatse a kan tuddai kamar tumakin da ba su da makiyayi, kuma Ubangiji ya ce, ‘Waɗannan mutane ba su da maigida. Bari kowa yă tafi gida cikin salama.’”
18 Ahab said to Jehoshaphat, “I told you [RHQ] that he never predicts [that] anything good [will happen to me]! He [always] predicts [that] bad things [will happen to me].”
Sai sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Ban faɗa maka cewa bai taɓa yin annabci wani abu mai kyau game da ni, sai mummuna kawai ba?”
19 But Micaiah continued, saying, “Listen to what Yahweh showed to me! [In a vision] I saw Yahweh sitting on his throne, with all the armies of heaven surrounding him, on his right side and on his left side.
Mikahiya ya ci gaba, “Saboda haka ka ji maganar Ubangiji. I, na ga Ubangiji zaune a kursiyinsa tare da dukan rundunar sama tsaye kewaye da shi a dama da hagunsa.
20 And Yahweh said, ‘Who can persuade Ahab to go to fight against the people of Ramoth, in order that he may be killed there?’ Some suggested one thing, and others suggested something else.
Kuma Ubangiji ya ce, ‘Wa zai ruɗi Ahab zuwa yaƙi da Ramot Gileyad, yă kuma kai shi mutuwarsa a can?’ “Wani ya ce wannan, wani ya ce wancan.
21 Finally one [evil] spirit came to Yahweh and said, ‘I can do it!’
A ƙarshe, wani ruhu ya zo gaba, ya tsaya a gaban Ubangiji ya ce, ‘Zan ruɗe shi.’
22 Yahweh asked him, ‘How will you do it?’ The spirit replied, ‘I will go and inspire all of Ahab’s prophets to tell lies.’ Yahweh said, ‘You will be successful; go and do it!’
“Ubangiji ya yi tambaya ‘Ta wace hanya?’ Ya ce, “‘Zan tafi in zama ruhun ƙarya a bakunan dukan annabawansa.’ “Ubangiji ya ce, ‘Za ka yi nasara a ruɗinsa. Ka tafi, ka yi haka.’
23 So now [I tell you that] Yahweh has caused all of your prophets to lie to you. Yahweh has decided that something terrible will happen to you.”
“Saboda haka yanzu Ubangiji ya sa ruhun ƙarya a bakunan dukan annabawanka. Ubangiji ya zartar maka da masifa.”
24 Then Zedekiah walked over to Micaiah and slapped him on his face. He said, “Do you think that Yahweh’s Spirit left me in order to speak to you?” [RHQ]
Sai Zedekiya ɗan Kena’ana ya hau ya mari Mikahiya a fuska. Ya yi tambaya, “A wace hanya ce ruhu daga Ubangiji ya bar ni ya yi maka magana?”
25 Micaiah replied, “You will find out for yourself [which of us Yahweh’s Spirit has truly spoken to] on the day when you go into a room of some house to hide [from the Syrian troops]!”
Mikahiya ya amsa, “Za ka gane a ranar da ka je ka ɓuya a ciki cikin ɗaki.”
26 King Ahab commanded [his soldiers], “Seize Micaiah and take him to Amon, the governor of this city, and to my son Joash.
Sa’an nan sarkin Isra’ila ya umarta, “Ku kama Mikahiya, ku kai shi wurin Amon, shugaban birnin, da wurin Yowash ɗan sarki.
27 Tell them that I have commanded that they should put this man in prison and give him only bread and water. Do not give him anything else to eat until I return safely from the battle!”
Ku ce ga abin da sarki ya ce, ‘Ku sa wannan mutum a kurkuku, kuma kada ku ba shi wani abu sai dai burodi da ruwa, sai na dawo lafiya.’”
28 Micaiah replied, “If you return safely, [it will be clear that] it was not Yahweh who told me what to say to you!” Then he said [to all those who were standing there], “Do not forget what I have said [to King Ahab]!”
Mikahiya ya furta, “Idan har ka dawo lafiya, to, Ubangiji bai yi magana ta wurina ba.” Ya kuma ƙara da cewa, “Ku lura da maganata, dukanku mutane!”
29 So the King of Israel and the King of Judah [led their armies] to Ramoth, in [the] Gilead [region].
Sai sarkin Isra’ila da Yehoshafat sarkin Yahuda suka haura zuwa Ramot Gileyad.
30 King Ahab said to Jehoshaphat, “I will put on different clothes, [in order that no one will recognize that I am the king]. But you should wear your (royal robe/robe that shows that you are a king).” So Ahab disguised himself, and they both went into the battle.
Sarkin Isra’ila ya ce wa Yehoshafat, “Zan ɓad da kama in shiga wurin yaƙi, amma ka sa kayan sarautarka.” Saboda haka sarkin Isra’ila ya ɓad da kama, ya shiga cikin yaƙi.
31 The King of Syria told this to his thirty-two men who were driving the chariots: “Attack only the king of Israel!”
Sarkin Aram kuwa ya umarci shugabanni kekunan yaƙinsa talatin da biyu, ya ce, “Kada ku yaƙe kowa, ƙarami ko babba, sai dai sarkin Isra’ila.”
32 So when the men who were driving the Syrian chariots saw Jehoshaphat [wearing (his royal robes/clothes that showed he was the king)], they pursued him. They shouted, “There is the king of Israel!” But when Jehoshaphat cried out,
Sa’ad da shugabannin kekunan yaƙin suka ga Yehoshafat, suka yi tsammani, suka ce, “Tabbatacce wannan shi ne sarkin Isra’ila.” Saboda haka suka juye don su yaƙe shi, amma sa’ad da Yehoshafat ya yi ihu,
33 they realized that he was not the king of Israel. So they stopped pursuing him.
sai shugabannin kekunan yaƙin suka ga ashe ba sarkin Isra’ila ba ne, sai suka daina binsa.
34 But one [Syrian] soldier shot an arrow at Ahab, without knowing that it was Ahab. The arrow struck Ahab between the places where the parts of his armor joined together. Ahab told the driver of his chariot, “Turn the chariot around and take me out of here! I have been severely wounded!”
Amma wani ya ja bakansa kawai ya bugi Ahab sarkin Isra’ila a tsakanin sassan kayan yaƙinsa. Sai sarki ya ce wa mahayin keken yaƙinsa, “Juye, ka fitar da ni daga yaƙin. An ji mini rauni.”
35 The battle continued all the day. Ahab was sitting propped up in his chariot, facing the Syrian troops. The blood from his wound ran down to the floor of the chariot. And late in the afternoon he died.
Dukan yini aka yi ta yaƙi, aka kuma riƙe sarki a keken yaƙinsa yana fuskanci Arameyawa. Jini daga mikinsa ya yi ta zuba a ƙasan keken yaƙin, a wannan yamma kuwa ya mutu.
36 Just as the sun was going down, someone among the Israeli troops shouted, “[The battle is ended!] Everyone should return home!”
Da rana tana fāɗuwa, sai kuka ta bazu cikin mayaƙa, “Kowane mutum ya tafi garinsu; kowa ya tafi ƙasarsa!”
37 So king Ahab died, and they took his body [in the chariot] to Samaria [city] and buried his body there.
Sai sarki ya mutu, aka kuwa kawo shi Samariya, aka binne shi a can.
38 They washed his chariot alongside the pool in Samaria, a pool where the prostitutes bathed. And dogs [came and] licked the king’s blood, just like Yahweh had predicted would happen.
Suka wanke keken yaƙi a tafki, a Samariya (inda karuwai suke wanka), sai karnuka suka lashe jininsa, kamar yadda maganar Ubangiji ta furta.
39 The account/record of the other things that happened while Ahab was ruling, and about the palace decorated with much ivory [that they built for him], and the cities that were built for him, was written in the scroll called ‘The History of the Kings of Israel’.
Game da sauran ayyukan mulkin Ahab, haɗe da dukan abin da ya yi, da fadan da ya gina ya kuma shimfiɗa da hauren giwa, da biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
40 When Ahab died, his body was buried where his ancestors were buried. Then his son Ahaziah became king.
Ahab ya huta da kakanninsa. Ahaziya ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
41 Before King Ahab died, when he had been ruling in Israel for four years, Asa’s son Jehoshaphat started to rule in Judah.
Yehoshafat ɗan Asa ya zama sarkin Yahuda a shekara ta huɗu ta Ahab sarkin Isra’ila.
42 Jehoshaphat was thirty-five years old when he started to rule, and he ruled in Jerusalem for twenty-five years. His mother was Azubah, the daughter of Shilhi.
Yehoshafat yana da shekara talatin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru ashirin da biyar. Sunan mahaifiyarsa, Azuba’yar Shilhi.
43 Jehoshaphat was a good king, just like his father Asa had been. He did things that pleased Yahweh. But while he was king, he did not remove all the pagan altars [that the people had built] on the hilltops. So the people continued to offer sacrifices [to idols] on those altars and burned incense there.
A cikin kome ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa Asa, bai kuma kauce daga gare su ba; ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji. Amma bai rurrushe masujadai da suke kan tuddai ba, mutane kuwa suka ci gaba da miƙa hadayu suna kuma ƙone turare a can.
44 Jehoshaphat also made [a] peace [agreement] with the king of Israel.
Yehoshafat kuma ya zauna lafiya da sarkin Isra’ila.
45 All the other things that happened while Jehoshaphat was ruling, and the great things that he did and the victories his [troops] won, are written in the scroll called ‘The History of the Kings of Judah’.
Game da sauran ayyukan mulkin Yehoshafat da abubuwan da ya yi, da kuma yaƙe-yaƙensa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
46 Jehoshaphat’s father Asa [had tried to expel] the male prostitutes that stayed at the pagan shrines, but some of them were still there. Jehoshaphat got rid of them.
Ya kawar da karuwai maza na masujadai da suke kan tuddai waɗanda suka rage tun mulkin mahaifinsa Asa.
47 At that time, there was no king in Edom; a ruler who had been appointed by Jehoshaphat ruled there.
Babu sarki a lokacin Edom, saboda haka sai mataimaki ya yi mulki.
48 Jehoshaphat [ordered some Israeli men to] build a fleet/group of ships to sail [south] to [the] Ophir [region] to get gold. But they were wrecked at Ezion-Geber/Elath, so the ships never sailed.
To, Yehoshafat ya gina jerin jiragen ruwan kasuwanci don su je Ofir saboda zinariya, amma ba su yi tafiya ba, gama sun farfashe a Eziyon Geber.
49 Before the ships were wrecked, Ahab’s son Ahaziah suggested to Jehoshaphat, “Allow my sailors to go with your sailors,” but Jehoshaphat refused.
A lokacin Ahaziya ɗan Ahab ya ce wa Yehoshafat, “Bari mutanena su tafi tare da mutanenka,” amma Yehoshafat ya ƙi.
50 When Jehoshaphat died, his [body] was buried where his ancestors were buried in [Jerusalem, ] the city where King David [had ruled]. Then Jehoshaphat’s son Jehoram became king.
Yehoshafat kuwa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin Dawuda kakansa. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi.
51 Before King Jehoshaphat died, when he had been ruling in Judah for 17 years, Ahab’s son Ahaziah began to rule in Israel. Ahaziah ruled in Samaria for two years.
Ahaziya ɗan Ahab ya zama sarkin Isra’ila a Samariya a shekara ta goma sha bakwai ta Yehoshafat sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekaru biyu.
52 He did many things that Yahweh considered to be evil, doing the [evil] things that his father and mother had done and the evil things that Jeroboam had done—the king who had led all the Israeli people to sin [by worshiping idols].
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, domin ya yi tafiya a hanyoyin mahaifinsa da na mahaifiyarsa, da kuma a hanyoyin Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila suka yi zunubi.
53 Ahaziah bowed in front of Baal’s idol and worshiped it. That caused Yahweh, the God who was the true God of the Israeli people, to become very angry, just as Ahaziah’s father had caused Yahweh to become angry.
Ya bauta, ya kuma yi wa Ba’al sujada, ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila yă yi fushi, kamar yadda mahaifinsa ya yi.

< 1 Kings 22 >