< 1 Kings 21 >

1 King Ahab had a palace in Jezreel [city]. Near the palace was a vineyard owned by a man from that city whose name was Naboth.
Ana nan bayan haka sai waɗannan abubuwa suka faru. Nabot mutumin Yezireyel yana da gonar inabi a Yezireyel, a yankin Samariya, kusa da gidan Sarki Ahab.
2 One day, Ahab [went to] Naboth and said to him, “Your vineyard is close to my palace. I would like to buy it, so that I can plant some vegetables there. In exchange, I will give you a better vineyard [somewhere else], or if you prefer, I will pay you for your vineyard.”
Sai Ahab ya ce wa Nabot, “Ka ba ni gonar inabinka in yi amfani da ita don kayan lambu, da yake tana kusa da fadana. Zan ba ka wata gonar inabin da ta fi wannan, ko kuma in ka gwammace, sai in biya ka duk abin da ya dace da ita.”
3 But Naboth replied, “That land belonged to my ancestors, [so I want to keep it]. I hope that Yahweh will never allow me to give that land to you!”
Amma Nabot ya amsa wa Ahab ya ce, “Ubangiji yă sawwaƙe in ba ka gādon kakannina.”
4 So Ahab became very sullen and angry because of what Naboth had said. He went home and lay down on his bed. He turned his face toward the wall, and he refused to eat anything.
Ahab ya cika da fushi saboda Nabot, mutumin Yezireyel ya ce, “Ba zan ba ka gādon kakannina ba.” Ya kwanta a gadonsa yana zub da hawaye, ya kuma ƙi cin abinci.
5 His wife Jezebel came in and asked him, “Why are you so depressed? Why are you refusing to eat anything?”
Matarsa Yezebel ta shiga ciki ta tambaye shi, ta ce, “Me ya sa ka kumbura? Me ya sa ba za ka ci abinci ba?”
6 Ahab replied, “I talked to Naboth, that man from Jezreel. I told him that [I wanted] his vineyard. [I said, ] ‘I will buy it from you, or I will give you another vineyard for it.’ But he refused [to let me have it].”
Sai ya amsa mata, ya ce, “Domin na ce wa Nabot mutumin Yezireyel, ‘Ka sayar mini gonar inabinka; ko kuwa in ka gwammace, zan ba ka wata gonar inabi a maimakonta.’ Amma ya ce, ‘Ba zan ba ka gonar inabina ba.’”
7 His wife replied, “You are [RHQ] the king of Israel, [so you can get whatever you want] Get up, and eat some food and do not worry [about what Naboth said]. I will get Naboth’s vineyard for you.”
Yezebel matarsa ta ce, “Yaya kake yi kamar ba kai ne sarki Isra’ila ba? Tashi ka ci abinci! Ka yi farin ciki. Zan ba ka gonar inabin Nabot mutumin Yezireyel.”
8 Then Jezebel wrote some letters, and she signed Ahab’s name on them. She used his official seal to seal them. Then she sent them to the older leaders and other important men who lived in Naboth’s town.
Sai ta rubuta wasiƙu a sunan Ahab, ta buga hatiminsa a kansu, sa’an nan ta aika su ga dattawa da manyan gari waɗanda suke zama a birnin da Nabot yake.
9 This is what she wrote in the letters: “Proclaim a day when all the people will [gather together and] (fast/abstain from eating food). Give to Naboth an important place to sit among them.
Cikin waɗannan wasiƙu ta rubuta, “Ku yi shelar ranar azumi, ku zaunar da Nabot a wuri mai martaba a cikin mutane.
10 Then find two men who always cause trouble. Give them places to sit opposite/facing him. Tell these men to testify that they heard Naboth say things that criticized God and the king. Then take Naboth out of the city and kill him by throwing stones at him.”
Amma ku zaunar da waɗansu’yan iska biyu ɗaura da shi, ku sa su ba da shaida cewa ya zagi Allah da sarki. Sa’an nan ku ɗauke shi ku jajjefe shi da dutse sai ya mutu.”
11 The leaders [received the letters and] did what Jezebel had written in the letters for them to do.
Sai dattawa da manyan gari, waɗanda suke zama a birnin da Nabot yake, suka yi kamar yadda Yezebel ta umarta a cikin wasiƙun da ta rubuta.
12 They declared a day on which the people would all (fast/abstain from food). And they gave Naboth a seat in a place where honored people sat, in front of the people.
Suka yi shelar azumi, suka kuma zaunar da Nabot a wuri mai martaba a cikin mutane.
13 Two men who always caused trouble sat opposite/facing Naboth. While everyone was listening, they stated that they had heard Naboth say things that criticized God and the king. So the people seized Naboth. They took him outside the city and killed him [by throwing] stones at him.
Sa’an nan’yan iska biyu suka zo, suka zauna ɗaura da shi, suka kawo zarge a kan Nabot a gaban mutane, suna cewa, “Nabot ya zagi Allah da sarki.” Saboda haka aka ɗauke shi waje da birnin, aka jajjefe shi da dutse har ya mutu.
14 Then those leaders sent a message to Jezebel, saying “We have executed Naboth.”
Sa’an nan suka aika wa Yezebel. “An jajjefe Nabot, ya kuma mutu.”
15 When Jezebel found out that Naboth had been killed, she told Ahab, “Naboth is dead. Now you can go and take possession of the vineyard that he refused to sell to you.”
Nan da nan sa’ad da Yezebel ta ji cewa an jajjefe Nabot da dutse ya kuma mutu, sai ta ce wa Ahab, “Tashi ka mallaki gonar inabin Nabot mutumin Yezireyel wanda ya ƙi ya sayar maka. Ba shi da rai, ya mutu.”
16 When Ahab heard that Naboth was dead, he got up and went to the vineyard to claim that he now owned it.
Da Ahab ya ji cewa Nabot ya mutu, sai ya tashi ya gangara don yă mallaki gonar inabin Nabot.
17 Then Yahweh spoke to Elijah the prophet. He said,
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya mutumin Tishbe.
18 “Go to Samaria and talk to Ahab, the king of Israel. He is in the vineyard of a man named Naboth. He has gone there to claim that he now owns it.
Ta ce, “Gangara don ka sadu da Ahab sarkin Isra’ila, wanda yake mulki a Samariya. Yanzu yana a gonar inabin Nabot, inda ya tafi yă mallake ta.
19 Tell Ahab that this is what I, Yahweh, say to him: ‘You have murdered Naboth and taken his land.’ So I am telling you this: ‘In the same place where [Naboth died and] dogs came and licked up Naboth’s blood, [you will die and] the dogs will lick up your blood, too!’”
Ka ce masa, Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ba ka kashe mutum ka kuma ƙwace kayansa ba?’ Sa’an nan ka ce masa ga abin da Ubangiji ya ce, ‘A inda karnuka suka lashe jinin Nabot, karnuka za su lashe jininka, I, naka!’”
20 So when Elijah met with Ahab, Ahab said to him, “You, my enemy, have found me!” [RHQ] Elijah answered, “Yes, I have found you. You have never stopped doing the things that Yahweh says are wrong.
Ahab ya ce wa Iliya, “Wato, ka same ni kuma, abokin gābana!” Sai ya amsa ya ce, “Na same ka, domin ka sayar da kanka ga yin mugunta a gaban Ubangiji.
21 So this is what Yahweh says to you: ‘I will soon get rid of you. I will kill you, and I will also kill every male in your household, including those who are slaves and those who are not slaves.
‘Zan kawo masifa a kanka. Zan kawar da zuriyarka, in kuma yanke daga Ahab kowane ɗa namiji na ƙarshe cikin Isra’ila, bawa ko’yantacce.
22 Your family will all be killed, just like the family of King Jeroboam and like the family of King Baasha were killed. I will get rid of you because you have caused me to become very angry, and you have also led the Israeli people to sin.’
Zan mai da gidanka kamar gida Yerobowam ɗan Nebat, da na Ba’asha ɗan Ahiya, domin ka tsokane ni har na yi fushi, ka kuma sa Isra’ila ya yi zunubi.’
23 Yahweh has also told me that [your wife] Jezebel [will be killed, and] dogs in Jezreel will eat her corpse.
“Game da Yezebel kuwa Ubangiji ya ce, ‘Karnuka za su cinye Yezebel a katangar Yezireyel.’
24 The [dead bodies of the] members of your family who die in this city [will not be buried, they] will be eaten by dogs, and [the corpses of] those who die in the fields will be eaten by vultures.”
“Karnuka za su cinye waɗanda suke na Ahab waɗanda suka mutu a cikin birni, tsuntsayen sararin sama kuma za su cinye waɗanda suka mutu a jeji.”
25 There was no man no man like Ahab who always did things that Yahweh considered to be evil. His wife Jezebel incited/urged him to do [many of] those things.
(Babu wani mutum kamar Ahab, wanda ya ba da kansa ga aikata mugunta a gaban Ubangiji. Yezebel matarsa ce ta zuga shi.
26 The most abominable/detestable thing that Ahab did was to worship idols, just like the Amor people-group had done. And that is why Yahweh took the Amor people’s land from them and gave it to the Israelis.
Ya yi abar ƙyama ƙwarai ta wurin bin gumaka, kamar Amoriyawan da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ila.)
27 After Elijah finished talking to Ahab, Ahab tore his clothes [to show that he was sorry for all the sins that he had committed]. He put on rough clothes that were made from sacks, and he refused to eat anything. He even wore those rough clothes made from sacks when he slept, to show that he was sorry.
Sa’ad da Ahab ya ji waɗannan kalmomi, sai ya yage rigarsa, ya sa rigunan makoki, ya kuma yi azumi. Ya kwanta a kayan makoki, ya kuma yi tafiya cikin sauƙinkai.
28 Then Yahweh said this to Elijah:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya mutumin Tishbe, ta ce,
29 “I have seen [RHQ] that Ahab is now very sorry for all the evil things that he has done. So the things that I promised to do to his [family] will not happen while he is still alive. I will cause them to happen after his son becomes king. Then those things will happen to his family.” [MTY]
“Ka lura da yadda Ahab ya ƙasƙantar da kansa a gabana kuwa? Domin ya ƙasƙantar da kansa, ba zan kawo wannan masifa a kwanakinsa ba, amma zan kawo ta a kan gidansa a kwanakin ɗansa.”

< 1 Kings 21 >