< 1 Kings 20 >

1 Ben-Hadad, the king of Syria, gathered all his army, and he persuaded 32 other kings to join him with their armies and horses and chariots. They marched to Samaria [city, the capital of Israel], and surrounded it, and [prepared to] attack it.
Ben-Hadad sarkin Aram kuwa ya tattara mayaƙansa gaba ɗaya. Sarakuna talatin da biyu suka tafi tare da shi haɗe da dawakansu da kekunan yaƙinsu. Ya haura ya yi wa Samariya kwanto, ya kuma yaƙe ta.
2 Ben-Hadad sent messengers into the city to King Ahab, to say this to him: “This is what King Ben-Hadad says:
Ya aika da’yan aika zuwa cikin birnin wurin Ahab sarkin Isra’ila yana cewa, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce,
3 ‘[You must give to] me all your silver and gold, your (good-looking/most beautiful) wives/women and strongest children.’”
‘Azurfarka da zinariyarka nawa ne. Mafi kyau cikin matanka da’ya’yanka nawa ne.’”
4 The king of Israel replied to them, “Tell this to King Ben-Hadad: ‘I agree to do what you requested. You can have me and everything that I own.’”
Sarkin Isra’ila ya amsa, ya ce, “Kamar dai yadda ka faɗa, ranka yă daɗe, sarki. Ni da dukan abin da nake da shi, naka ne.”
5 [The messengers told that to] Ben-Hadad, and he [sent them back with] another message: “I sent a message to you saying that you must give me all your silver and gold and your wives and your children.
Sai’yan aikan suka sāke dawo suka ce, “Ga abin da Ben-Hadad ya ce, ‘Na aika ka ba da azurfarka da zinariyarka, matanka da kuma’ya’yanka.
6 But [in addition to that], about this time tomorrow, I will send some of my officials to search your palace and the houses of your officials, and to bring to me everything that pleases them.”
Amma war haka gobe zan aika shugabannina su bincika fadanka da kuma gidajen shugabanninka. Za su kwashe dukan abubuwan da kake ganin darajarsu su tafi.’”
7 King Ahab summoned all the leaders of Israel, and said to them, “You can see/realize for yourselves that this man is trying to cause much trouble. He sent me a message insisting that I must give him my wives and my children, my silver and my gold, and I agreed to do that.”
Sarkin Isra’ila ya tattara dukan dattawan ƙasar, ya ce musu, “Ku duba fa, wannan mutum yana neman tsokana! Sa’ad da ya aika in ba shi matana da’ya’yana, azurfana da zinariyana, ban hana masa ba.”
8 The leaders and all the other people said to him, “Do not pay any attention to him! Do not do what he is requesting!”
Dattawa da dukan mutane suka amsa, suka ce, “Kada ka saurare shi ko ka yarda da abin da yake bukata.”
9 So Ahab said to Ben-Hadad’s messengers, “Tell the king that I agree to give him the things that he first requested, but I do not agree to allow his officials to take anything that they want from my palace and from the houses of my officials.” So the messengers [reported that to King Ben-Hadad, and they] returned with another message from Ben-Hadad.
Saboda haka ya ba wa’yan aikan Ben-Hadad amsa, ya ce, “Ku faɗa wa ranka yă daɗe, sarki, ‘Bawanka zai yi dukan abin da ka bukaci da farko, amma wannan na ƙarshe ba zan iya yin ba.’” Suka tafi suka kai amsar wa Ben-Hadad.
10 In that message he said, “[We will destroy] your city [completely, with the result that] there will not be enough dust and rubble left for each of my soldiers to have one handful! I hope/wish that the gods will strike me dead if we do not do that!”
Sai Ben-Hadad ya aika da wani saƙo wa Ahab, ya ce, “Bari alloli su yi da ni yadda suke so, su kuma yi haka da tsanani, in isashen ƙura ta rage a Samariya da za a iya ba wa mutanena a tafin hannu.”
11 King Ahab replied [to the messengers], “Tell King Ben-Hadad that a soldier who is putting on his armor [preparing to fight a battle] [MTY] should not boast at that time; he [should wait until] after he wins the battle.”
Sarki Isra’ila ya amsa, ya ce, “Ku faɗa masa, ‘Wanda ya sa kayan yaƙinsa bai kamata yă yi fariya ba sai ya tuɓe su.’”
12 Ben-Hadad heard that message while he and the other rulers were drinking [wine] in their temporary shelters. He told his men to prepare to attack [MTY] the city. So his men did that.
Ben-Hadad ya ji wannan saƙo yayinda shi da sarakunan suke sha a cikin tentunansu, sai ya umarce mutanensa, ya ce, “Ku shirya don yaƙi.” Saboda haka suka shirya don su yaƙi birnin.
13 At that moment, a prophet came to King Ahab and said to him, “This is what Yahweh says: ‘[Do not be at all afraid of] [RHQ] the large enemy army that you see! I will enable your army to defeat them today, and you will know that it is I, Yahweh, [who have the power to do what I say that I will do].’”
Ana cikin haka sai wani annabi ya zo wurin Ahab sarkin Isra’ila ya sanar masa cewa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ga wannan ɗumbun mayaƙa? Zan ba da su cikin hannunka a yau, sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”
14 Ahab asked, “What group [of our army] will defeat them?” The prophet replied, “The young soldiers who are commanded by the district governors will do it.” The king asked, “Who should lead the attack?” The prophet replied, “You should!”
Ahab ya ce, “Amma wa zai yi haka?” Annabin ya amsa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Sojoji matasa na shugabannin yankuna za su yi haka.’” Ya tambaya, “Wa kuma zai fara yaƙin?” Annabin ya amsa, “Kai za ka fara.”
15 So Ahab gathered the young soldiers who were commanded by the district governors. There were 232 of those men. Then he also summoned all the Israeli army. There were [only] 7,000 soldiers.
Saboda haka Ahab ya kira sojoji matasa na shugabannin yankuna, mutum 232. Sa’an nan ya tattara sauran Isra’ilawa su 7,000 gaba ɗaya.
16 They started to attack at noon, while Ben-Hadad and the other rulers were getting drunk in their temporary shelters.
Suka fita da tsakar rana yayinda Ben-Hadad tare da sarakuna 32 masu goyon bayansa suke cikin tentunansu suna sha, suna buguwa.
17 The young soldiers advanced first. Some scouts who had been sent out by Ben-Hadad reported to him, “There are men coming out of Samaria [city]”!
Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka fara fita. Ben-Hadad kuwa ya riga ya aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka ce, “Mutane suna zuwa daga Samariya.”
18 He said, “It does not matter whether they are coming to fight against us or to ask for peace. Capture them, but do not kill them
Ya ce, “In sun fito don salama, ku kamo su da rai; in sun fito yaƙi ne, ku kamo su da rai.”
19 The young Israeli soldiers went out of the city to attack [the Syrian army], and the other soldiers in the Israeli army followed them.
Sojojin nan matasa na shugabannin yankuna suka taka suka fita daga birnin da mayaƙa a bayansu.
20 Each [Israeli soldier] killed a [Syrian] soldier. The rest of the Syrian army then ran away, and the Israeli soldiers pursued them. But King Ben-Hadad escaped riding his horse, along with some other men riding horses.
Kowannensu kuwa ya buge abokin gābansa. Ganin wannan, sai Arameyawa suka gudu, Isra’ilawa suna bi. Amma Ben-Hadad na Aram ya tsere a kan dokinsa tare da waɗansu mahayan dawakansa.
21 Then the king of Israel went out [of the city], and he and his soldiers captured [all] the [other Syrian] horses and chariots, and also killed a large number of Syrian soldiers.
Sarki Isra’ila ya bi, ya kuma sha ƙarfin dawakan da keken yaƙin, ya kashe Arameyawa da yawa.
22 Then that same prophet went to King Ahab and said to him, “Go back and prepare your soldiers, and think carefully about what will be necessary for you to do, because the king of Syria with attack with his army again in the springtime of next year.”
Daga baya, annabin ya zo wurin sarkin Isra’ila ya ce, “Ka ƙarfafa matsayinka ka kuma ga abin da za a yi, gama a bazara mai zuwa sarkin Aram zai sāke kawo yaƙi.”
23 [After the Syrian army was defeated, ] Ben-Hadad’s officials said to him, “The gods that the Israelis [worship] are gods [who live] in the hills. [Samaria is built on a hill, and] that is why their soldiers were able to defeat us. But if we fight against them in the plains/lowlands, we certainly will be able to defeat them.
Ana cikin haka, shugabannin sarkin Aram suka ba shi shawara, “Allolinsu, allolin tuddai ne. Shi ya sa suka fi mu ƙarfi. Amma in mun yaƙe su a fili, tabbatacce za mu fi su ƙarfi.
24 So, this is what you should do: You must remove the 32 kings [who are leading your troops] and replace them with army commanders.
Ka yi wannan. Ka cire dukan sarakuna daga matsayinsu ka sa waɗansu shugabanni a maimakonsu.
25 Then gather an army like the army that was defeated. Gather an army that has as many horses and chariots as the first army had. Then we will fight the Israelis in the plains/lowlands, and we will surely defeat them.” Ben-Hadad agreed with them, and he did what they suggested.
Dole kuma ka tā da waɗansu mayaƙa kamar waɗanda ka rasa, doki don doki, keken yaƙi kuma don keken yaƙi, saboda mu iya yaƙe Isra’ila a fili. Ta haka tabbatacce za mu fi ƙarfinsu.” Sai ya yarda da su, ya kuma yi haka.
26 In the spring of the following year, he gathered his soldiers and marched [with them] to Aphek [city east of Galilee Lake], to fight against the Israeli army.
Bazara na biye Ben-Hadad ya tattara Arameyawa, ya haura zuwa Afek don yă yaƙi Isra’ila.
27 The Israeli army was also gathered together, and they were equipped with the things that they needed [for the battle]. Then they marched out and formed two groups facing the Syrian army. Their army was very small; they resembled two small flocks of goats, whereas the Syrian army [was very large and] spread all over the countryside.
Sa’ad da aka tattara Isra’ilawa, aka kuma ba su guzuri, sai suka taka suka fita don su sadu da Arameyawa. Isra’ilawa suka kafa sansani ɗaura da su kamar ƙananan garkuna biyu na awaki, yayinda Arameyawa suka rufe dukan jejin.
28 A prophet came to King Ahab and said to him, “This is what Yahweh says: ‘The Syrians say that I am a god who lives in the hills, and that I am not a god who lives in the valleys. So I will [show that they are wrong by] enabling your men to defeat this huge army [IDM] [in the valley], and you will know that I, Yahweh, [have done it].’”
Sai mutumin Allah ya zo ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Domin Arameyawa suna tsammani Ubangiji allahn tuddai ne, ba allahn kwari ba, zan ba da wannan ɗumbun mayaƙa a hannuwanka, za ka kuwa sani ni ne Ubangiji.’”
29 The two armies stayed in their tents for seven days, in groups that faced each other. Then, on the seventh day, they started fighting. The Israeli army killed 100,000 Syrian soldiers.
Kwana bakwai suka yi sansani ɗaura da juna, a rana ta bakwai sai yaƙi ya haɗu. Isra’ilawa suka kashe sojojin kafa na Arameyawa dubu ɗari a rana ɗaya.
30 The other Syrian soldiers ran away into Aphek City. Then the wall of the city collapsed and killed 27,000 more Syrian soldiers. Ben-Hadad also escaped into the city, and hid in the back room of a house.
Sauransu suka tsere zuwa birnin Afek, inda katangar ya fāɗa a kan mutum dubu ashirin da bakwai. Sai Ben-Hadad ya gudu zuwa birni ya ɓuya a ciki cikin ɗaki.
31 His officials went to him and said, “We have heard a report that the Israelis act mercifully. So allow us to go to the king of Israel, wearing coarse sacks around our waists and ropes on our heads/necks [to indicate that we will be his slaves]. Perhaps [if we do that, ] he will allow you to remain alive.”
Fadawansa suka je suka ce masa, “Mun ji an ce sarakunan Isra’ila masu jinƙai ne, bari mu sa tufafin makoki, mu ɗaura igiyoyi a wuyanmu, sa’an nan mu tafi wurin sarkin Isra’ila, wataƙila zai bar ka da rai.”
32 [The king permitted them to do that, ] so they wrapped coarse sacks around their waists and put ropes on their heads/necks, and they went to the king of Israel and said to him, “Ben-Hadad, who greatly respects you, says, ‘Please do not kill me.’” Ahab replied, “Is he still alive? He is like a brother to me!”
Saye da tufafin makoki kewaye a gindinsu, da kuma igiyoyi kewaye da kawunansu, suka tafi wurin sarkin Isra’ila, suka ce, “Bawanka Ben-Hadad ya ce, ‘Ina roƙonka bari in rayu.’” Sarki ya amsa, “Har yanzu yana da rai? Shi ɗan’uwana ne.”
33 Ben-Hadad’s officials were trying to find out if Ahab would act mercifully, and when Ahab said “brother,” they (were optimistic/thought that Ahab would be merciful). So they replied, “Yes, he is like your brother!” Ahab said, “Go and bring him to me.” So they [went and] brought Ben-Hadad to him. [When Ben-Hadad arrived, ] Ahab told him to get in his chariot [and sit with him].
Da ma abin da fadawan suke so su ji ke nan, sai suka yi sauri, suka karɓi maganar a bakinsa, suka ce, “I, ɗan’uwanka, Ben-hadad!” Sarki ya ce, “Ku je ku kawo shi.” Da Ben-Hadad ya fita, sai Ahab ya sa aka kawo shi cikin keken yaƙinsa.
34 Ben-Hadad said to him, “I will give back to you the towns that my father’s army took from your father. And I will allow you to set up market areas for your merchants in Damascus [my capital], just as my father did in Samaria [your capital].” Ahab replied, “Because you agree to do that, I will not execute you.” So Ahab made an agreement with Ben-Hadad, and allowed him to go home.
Ben-Hadad ya ce, “Zan mayar da biranen mahaifinka da na ƙwace daga mahaifinka. Za ka iya sa wurin kasuwarka a cikin Damaskus, kamar yadda mahaifinka ya yi a Samariya.” Ahab ya ce, “Bisa wannan yarjejjeniya zan sake ka.” Saboda haka ya yi yarjejjeniya da shi, sai ya bar shi ya tafi.
35 Then Yahweh spoke to a member of a group of prophets and said to him, “Ask one of your fellow prophets to strike and wound you.” [So he did what Yahweh told him to do]. [He said to one of his fellow prophets, ‘Strike me and wound me].’ But that man refused to do it.
Ta wurin maganar Ubangiji, ɗaya daga cikin’ya’ya maza na annabawa ya ce wa abokinsa, “Ka buge ni da makaminka,” amma mutumin ya ƙi.
36 So the prophet said to him, “Because you refused to obey what Yahweh told you to do, a lion will kill you as soon as you leave me.” And as soon as he left that prophet, a lion suddenly pounced on him and killed him.
Sai annabin ya ce, “Domin ba ka yi biyayya da Ubangiji ba, da zarar ka bar ni zaki zai kashe ka.” Daga baya mutumin ya tafi, zaki ya same shi, ya kuma kashe shi.
37 Then the prophet found another prophet, and said to him, “Strike me!” So that man hit him [very hard] and injured him.
Annabin ya sami wani mutum ya ce, “Ka buge ni, ina roƙonka.” Sai mutumin ya buge shi, ya ji masa ciwo.
38 Then the prophet put a large bandage/cloth over his face so that no one would recognize him. Then he went and stood alongside the road, waiting for the king to come by.
Sa’an nan annabin ya tafi ya tsaya a bakin hanya yana jiran sarki. Ya ɓad da kamanni da ƙyalle a kansa. Ƙyallen ya sauka zuwa bisa idanunsa.
39 When the king passed by, the prophet cried out to him, saying “Your majesty, [after I was wounded] while I was fighting in a battle, a soldier brought to me one of our enemies that he had captured, and said to me, ‘Guard this man! If he escapes, you must pay me 3,000 pieces of silver, and if you do not pay that, you will be executed!’
Yayinda sarki yake wucewa, sai annabin ya yi kira da ƙarfi gare shi ya ce “Ni bawanka na tafi yaƙi, sai ga wani ya kawo mini wani mutum, ya ce, ‘Ka riƙe wannan mutum, kada ka bar shi yă kuɓuta ko da ƙaƙa, idan ka bari ya kuɓuta, a bakin ranka, ko kuwa ka biya talanti ɗaya na azurfa.’
40 But while I was busy doing other things, the man escaped!” The king of Israel said to him, “That is your problem! You yourself have said that you deserve to be punished.”
Yayinda bawanka yana fama, yana kai da kawowa, sai mutumin ya ɓace.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Hukuncinka ke nan, ka furta shi da kanka.”
41 The prophet immediately took off the bandage, and the king of Israel recognized that he was one of the prophets.
Sai annabin ya cire ƙyallen da sauri daga kansa, da ya rufe idanunsa, sarkin Isra’ila kuwa ya gane shi a matsayi ɗaya daga cikin annabawa.
42 And the prophet said to him, “This is what Yahweh says: ‘You have allowed that man [Ben-Hadad] to escape after I commanded you to be sure to execute him! Since you did not do that, you will be killed instead. And your army will be destroyed because you allowed [some of] his army to escape!’”
Sai ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka saki mutumin da na ƙudura yă mutu. Saboda haka ranka zai zama a maimakon ransa, mutanenka a maimakon mutanensa.’”
43 The king went back home to Samaria, very angry and depressed/dejected.
Cike da fushi, sarkin Isra’ila ya tafi fadarsa a Samariya.

< 1 Kings 20 >