< 1 Kings 17 >

1 Elijah was [a prophet] who lived in Tishbe [town] in [the] Gilead [region]. One day he [went to] King Ahab and said to him, “Yahweh is the God whom we Israelis [worship] and the God whom I worship and serve. Just as certainly as Yahweh lives, there will be no dew or rain for the next few years, if I do not command rain to fall!”
To, Iliya mutumin Tishbe, daga Tishbe a Gileyad, ya ce wa Ahab, “Muddin Ubangiji, Allah na Isra’ila wanda nake bauta wa yana a raye, ba za a yi raɓa ko ruwan sama a’yan shekaru masu zuwa ba, sai ko na faɗa haka.”
2 Then Yahweh said to Elijah,
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya, ta ce,
3 “[Because you have made the king angry with you, escape from the king and, ] go to the east, to the Kerith Brook, east of where it flows into the Jordan [River].
“Ka bar nan, ka nufi wajajen gabas, ka ɓuya a Rafin Kerit, gabas da Urdun.
4 You will be able to drink water from the brook, and [you will be able to eat what] the crows [bring to you, because] I have commanded them to bring food to you.”
Za ka sha daga rafin, zan kuma umarci hankaki su ciyar da kai a can.”
5 So Elijah did what Yahweh commanded him to do. He went and camped alongside Kerith Brook.
Saboda haka sai Iliya ya yi abin da Ubangiji ya faɗa masa. Ya tafi Rafin Kerit, gabas da Urdun, ya zauna a can.
6 Crows bought bread and meat to him every morning and every evening, and he drank [water] from the brook.
Hankaki suka riƙa kawo masa abinci da nama, safe da yamma, ya kuma sha daga rafin.
7 But after a while, the water in the brook dried up, because rain did not fall anywhere in the land.
Ana nan sai rafin ya bushe saboda ba a yi ruwan sama a ƙasar ba.
8 Then Yahweh said to Elijah,
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya cewa,
9 “Go and live in Zarephath [village], near Sidon [city]. There is a widow there who will give you food to eat. I have [already] told her what to do about that.”
“Je ka, nan take, zuwa Zarefat na Sidon, ka zauna a can. Na umarci wata gwauruwa a can tă ciyar da kai.”
10 So [Elijah did what God said]. He went to Zarephath. As he arrived at the gates of the village, he saw a widow who was gathering sticks. He said to her, “Would you please bring me a cup of water?”
Saboda haka sai ya tafi Zarefat. Sa’ad da ya isa ƙofar gari, sai ga wata gwauruwa tana tattara’yan itace. Sai ya kira ta, ya ce, “Ki kawo mini ɗan ruwa a tulu don in sha.”
11 While she was going to get it, he called out to her, “Bring me a piece of bread, too!”
Da ta kama hanya za tă tafi tă kawo, sai ya sāke kiranta ya ce, “Ina roƙonki, ki kuma kawo mini ɗan abinci.”
12 But she replied, “Your God knows that what I am telling you is true: I do not have even one piece of bread in my house. I have only a handful of flour in a jar, and a little [olive] oil in a jug. I was gathering a few sticks to use these to [make a fire and] cook one more meal, and then after my son and I eat that, we will die [from hunger].”
Sai ta ce masa, “Na rantse da Ubangiji Allahnka, ba ni da wani abinci, sai dai ɗan gari hannu guda a tulu, da kuma ɗan mai a kwalaba. Ina tattara’yan itacen nan ne don in kai gida in yi abinci wa kaina da ɗana, don mu ci, mu mutu.”
13 But Elijah said to her, “Do not be worried! Go home and do what you said that you were going to do. But first, bake me a little loaf of bread and bring it to me. After you do that, take what is left and prepare some food for you and your son.
Iliya ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Ki tafi gida, ki yi yadda kika ce. Amma da farko ki yi mini’yar wainar burodi daga abin da kike da shi ki kawo mini, sa’an nan ki yi wani abu wa kanki da kuma ɗanki.
14 [I know that you will be able to do that, ] because Yahweh, the God whom we Israelis [worship], says this: ‘There will always be plenty of flour and [olive] oil left in your containers, until the time when I send rain again [and the crops grow again]!’”
Gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Tulun garin ba zai ƙare ba, kwalabar man kuma ba zai bushe ba sai ranar da Ubangiji ya bayar da ruwan sama a ƙasar.’”
15 So the woman did exactly what Elijah told her to do. And she and her son and Elijah had enough food every day,
Sai ta tafi, ta yi yadda Iliya ya faɗa mata. Saboda haka aka kasance da abinci kowace rana wa Iliya da kuma don macen da iyalinta.
16 because the flour in the jar was never finished, and the jug of oil was never empty. That happened just like Yahweh had told Elijah that it would happen.
Gama tulun garin bai ƙare ba, kwalabar man kuma bai bushe ba, kamar yadda Ubangiji ya faɗa wa Iliya.
17 Some time later, the woman’s son became sick. He continued to get worse, and finally he died.
Ana nan sai ɗan matan, wato, gwauruwan nan ya fara ciwo. Ciwon ya ƙara muni, daga ƙarshe sai ya daina numfashi.
18 So the woman went to Elijah and said to him, “You are a prophet; so why have you done this to me? Have you come here to punish me for my sins by causing my son to die?”
Sai ta ce wa Iliya, “Mutumin Allah, yaya haka? Ka zo ne domin ka nuna wa Allah zunubaina, ka kuma jawo mutuwar ɗana?”
19 But Elijah replied, “Give your son to me.” So she gave her son to him, and he took the boy’s [body] from her and carried it up [the steps] to the room where he stayed. He laid the boy’s [body] on his bed.
Iliya ya ce, “Ki miƙa mini ɗanki.” Sai ya ɗauke shi daga hannuwanta, ya kai shi ɗakin sama inda yake zama, ya kwantar da shi a gadonsa.
20 Then Elijah cried out to Yahweh, “O Yahweh my God, this widow [has kindly allowed] me to stay in her home. So why have you brought this tragedy to her and caused her son to die?” [RHQ]
Sa’an nan ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, don me ka kawo wannan masifa a kan gwauruwan nan? Kai ka ce in zauna tare da ita, ga shi yanzu ɗanta ya mutu.”
21 Then Elijah stretched himself on top of the boy’s [body] and called out to Yahweh saying, “Yahweh my God, please allow this boy to become alive again!” He did this three times.
Sai ya kwanta, ya miƙe kansa a kan yaron sau uku, ya kuma yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, ka mai da ran yaron nan!”
22 Yahweh heard what Elijah prayed, and [he caused] the boy [to] become alive again [DOU].
Ubangiji kuwa ya ji kukan Iliya, sai ran yaron ya dawo masa, ya kuma rayu.
23 Elijah carried the boy down [the steps] and gave him to his mother. He said, “Look, your son is alive!”
Iliya ya ɗauki yaron ya sauko da shi daga ɗakin sama zuwa cikin gida. Ya ba da shi ga mahaifiyarsa, ya ce, “Duba, ɗanki yana da rai!”
24 The woman said to Elijah, “Now I know [for certain] that you are a prophet and that the words that you speak are truly from Yahweh!”
Sai matar ta ce wa Iliya, “Yanzu na san cewa kai mutumin Allah ne, Ubangiji kuma yana magana ta wurinka.”

< 1 Kings 17 >