< 1 Kings 16 >
1 During the time that Baasha [was king of Israel], [the prophet] Jehu, Hanani’s son, gave Baasha this message that he had received from Yahweh:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Yehu ɗan Hanani game da Ba’asha,
2 “You were very insignificant/unimportant [IDM] when I caused you to become the ruler of my Israeli people. But you have caused me to become very angry by doing [IDM] the kinds of evil things that King Jeroboam did. You have also caused me to become angry by causing my people to sin.
“Na ɗaga ka daga ƙura na mai da kai shugaban mutanena Isra’ila, amma ka yi tafiya a hanyoyin Yerobowam, ka kuma sa mutanena Isra’ila suka yi zunubi, ka tsokane ni na yi fushi ta wurin zunubansu.
3 So now I will get rid of you and your family [MTY]. I will do to you just like I did to Jeroboam and his family.
Saboda haka ina gab da cinye Ba’asha da gidansa, zan kuma mai da gidanka kamar na Yerobowam ɗan Nebat.
4 [The bodies of] those in your family who die in this city [will not be buried; they] will be eaten by dogs; and [the corpses of] those who die in the fields will be eaten by vultures.”
Karnuka za su cinye waɗanda suke na Ba’asha da suka mutu a birni, tsuntsaye kuma za su cinye waɗanda suka mutu a jeji.”
5 The other things that happened during the time that Baasha ruled Israel, and the things that he did, are written [RHQ] in the scroll called ‘The History of the Kings of Israel’.
Game da sauran ayyukan mulkin Ba’asha, abin da ya yi, da kuma nasarorinsa, an rubuta su cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
6 When Baasha died, he was buried in Tirzah, [the capital city]. Then his son Elah became king.
Ba’asha ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Tirza. Sai Ela ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
7 Yahweh gave that message about Baasha and his family to the prophet Jehu. Baasha had done many things that Yahweh considered to be evil, which caused Yahweh to become angry. Baasha did the same kind of things that King Jeroboam and his family had done previously. Yahweh was also angry with Baasha because he had killed all of Jeroboam’s family.
Ban da haka, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Yehu ɗan Hanani wa Ba’asha da gidansa, saboda dukan muguntar da ya aikata a gaban Ubangiji, ya tsokane shi yă yi fushi ta wurin abubuwan da ya yi, da kuma zama kamar gidan Yerobowam, da kuma domin ya hallaka gidan Yerobowam.
8 After Asa had been the king of Judah for almost 26 years, Elah became the king of Israel. Elah ruled in Tirzah for [only] two years.
A shekara ta ashirin da shida ta Asa sarkin Yahuda, Ela ɗan Ba’asha ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi mulki a Tirza shekaru biyu.
9 [A man named] Zimri was one of Elah’s army officers. He commanded the drivers of half of Elah’s army’s (chariots/two-wheeled vehicles pulled by horses). He made plans to kill Elah while Elah was in Tirzah, getting drunk at the house of [a man named] Arza. Arza was the man who took care of the things in the king’s palace.
Zimri, ɗaya daga cikin shugabanni, wanda ya shugabanci rabin kekunan yaƙin Ela, ya yi maƙarƙashiya a kansa. Ela yana a Tirza a lokacin, ya bugu a gidan Arza, sarkin fada a Tirza.
10 Zimri went into Arza’s house and killed Elah. Then Zimri became the king of Israel. That was when Asa had been the king of Judah for 27 years.
Zimri ya shiga, ya buge shi ya kashe a shekara ta ashirin da bakwai na Asa sarkin Yahuda. Sa’an nan ya gāje shi a matsayin sarki.
11 As soon as Zimri became king [MTY], he killed all of Baasha’s family [MTY]. That included every male [IDM] in Baasha’s family and all of Baasha’s male friends.
Nan da nan sai ya fara mulki ya kuwa zauna a kujerar sarauta, ya kashe dukan iyalin Ba’asha. Bai bar namiji guda ɗaya ba, ko dangi, ko aboki.
12 That was just what Yahweh told the prophet Jehu would happen.
Ta haka Zimri ya hallaka dukan iyalin Ba’asha, bisa ga maganar da Ubangiji ya yi game da Ba’asha ta wurin annabi Yehu.
13 Baasha and his son Elah had sinned and led the Israeli people to sin. They caused Yahweh, the God whom the Israeli people worshiped, to become angry, because they both urged the people [to worship] worthless idols.
Wannan ya faru saboda dukan zunuban Ba’asha da waɗanda ɗansa Ela ya yi, da ya sa Isra’ila suka yi, har suka tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, yă yi fushi ta wurin gumakansu marasa amfani.
14 Everything else that Elah did is written in the scroll called ‘The History of the Kings of Israel’.
Game da sauran ayyukan mulkin Ela, da dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
15 So Zimri became the king of Israel after Asa had been king of Judah for 27 years. But Zimri ruled in Tirzah for only seven days. The Israeli army was beseiging/surrounding Gibeah, a town which belonged to the Philistine people-group.
A shekara ta ashirin da bakwai na Asa sarkin Yahuda, Zimri ya yi mulki a Tirza kwana bakwai. Mayaƙa suka yi sansani kusa da Gibbeton, wani garin Filistiyawa.
16 The men in the Israeli army camp heard that Zimri had secretly planned to kill King Elah, and then had killed him. So on that day the soldiers chose Omri, the commander of their army, to become the king of Israel.
Sa’ad da Isra’ilawa a cikin sansani suka ji cewa Zimri ya yi maƙarƙashiya a kan sarki, ya kuma kashe shi, sai suka yi shela, suka naɗa Omri, shugaban mayaƙa ya zama sarki a bisa Isra’ila, a wannan rana a cikin sansani.
17 The Israeli army was camped near Gibbethon [city]. When they heard what Zimri had done, they left there and went to Tirzah, and surrounded the city.
Sai Omri da dukan Isra’ilawa suka janye daga Gibbeton, suka yi wa Tirza kwanto.
18 When Zimri realized that the city was [about to be] captured, he went into his palace and set it on fire. So the palace burned down, and he died [in the fire].
Da Zimri ya ga cewa an kame birnin, sai ya je ya shiga hasumiya fadan sarki ya sa wa fadan wuta wutar kuwa ta ƙone shi ya mutu.
19 He died because he had sinned by doing the things that Yahweh considered to be evil. Jeroboam had led the Israeli people to sin, and Zimri sinned just like Jeroboam had sinned.
Wannan ya faru saboda zunuban da ya yi, ya yi mugunta a gaban Ubangiji ya kuma yi tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubin da Yerobowam ya yi da ya sa Isra’ila suka yi.
20 All the other things that Zimri did, and the record of how he rebelled [against King Elah], are written in the scroll called ‘The History of the Kings of Israel’.
Game da sauran ayyukan mulkin Zimri, da tawayen da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
21 After Zimri died, the Israeli people were divided. One group wanted Tibni, the son of Ginath, to be their king. The other group wanted Omri [to be the king].
Sai mutanen Isra’ila suka rabu kashi biyu; rabi guda sun goyi bayan Tibni ɗan Ginat yă zama sarki, ɗayan rabin kuma sun goyi bayan Omri.
22 Those who supported Omri (were stronger than/defeated) those who supported Tibni. So Tibni was killed, and Omri became king.
Amma mabiyan Omri suka nuna sun fi na Tibni ɗan Ginat ƙarfi. Sai Tibni ya mutu, Omri kuwa ya zama sarki.
23 Omri became king when Asa had been king of Judah for almost 31 years. Omri ruled Israel for 12 years. For the first six years he ruled in Tirzah.
A shekara ta talatin da ɗaya na Asa sarkin Yahuda, Omri ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu, shekaru shida a Tirza.
24 Then he bought a hill from [a man named] Shemer and paid him about (150 pounds/70 kg.) of silver for it. Then Omri ordered his men to build a city on that hill, and he called it Samaria, to honor Shemer, the man who owned it previously.
Ya saya tudun Samariya daga Shemer, a bakin talentin biyu na azurfa, ya kuma gina birni a kan tudun, ya kira shi Samariya, bayan Shemer, sunan mai tudun a dā.
25 But Omri did many things that Yahweh considered to be evil. He did more evil deeds than any of the kings who ruled Israel before he did.
Amma Omri ya yi mugunta a gaban Ubangiji, ya kuma yi zunubi fiye da dukan waɗanda suka kasance kafin shi.
26 [When] Jeroboam [was previously the king, he] had led the Israeli people to sin, and Omri committed the same kind of sins that Jeroboam did. The Israeli people caused Yahweh, the God the Israeli people had worshiped, to become very angry, because they worshiped worthless idols.
Ya yi tafiya a dukan hanyoyin Yerobowam ɗan Nebat da kuma cikin zunubinsa wanda ya sa Isra’ila suka yi, har suka tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila yă yi fushi ta wurin gumakansu marasa amfani.
27 Everything that Omri did, and the record of the victories that his [army] won, are written in the scroll called ‘The History of the Kings of Israel’.
Game da sauran ayyukan mulkin Omri, abin da ya yi, da kuma abubuwan da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
28 After Omri died, he was buried in Samaria, and his son Ahab became king.
Omri ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Samariya. Sai Ahab ya gāje shi a matsayin sarki.
29 Ahab became king of Israel when Asa had ruled Judah for almost 38 years. Ahab ruled in Samaria [city] for 22 years.
A shekara ta talatin da takwas ta Asa sarkin Yahuda, Ahab ɗan Omri ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi mulki a Samariya a kan Isra’ila, shekara ashirin da biyu.
30 Ahab did many things that Yahweh considered to be evil. He did more evil things than any of the kings who ruled Israel before he did.
Ahab ɗan Omri ya yi mugunta sosai a gaban Ubangiji fiye da wani daga cikin waɗanda suka riga shi.
31 He committed the same kind of sins that Jeroboam did, but he did things that were worse than the things that Jeroboam did. He married [a woman named] Jezebel, the daughter of Ethbaal, the king of Sidon [city]. Then Ahab started to worship Baal, [the god that the Canaan people-group worshiped].
Bai zama masa wani abu mai wuya ba, yă yi zunuban Yerobowam ɗan Nebat, har ma ya auri Yezebel’yar Etba’al sarkin Sidoniyawa, ya kuma fara bauta wa Ba’al, ya yi masa sujada.
32 He built a temple in Samaria in order that the Israeli people could worship Baal there, and he put an altar there for [making sacrifices to] Baal.
Ya kafa bagade domin Ba’al a haikalin Ba’al da ya gina a Samariya.
33 He also made an idol that represented Asherah, [Baal’s wife]. He did many more things that caused Yahweh to become angry. He did more evil things than any of the previous kings of Israel had done.
Ahab ya gina ginshiƙin Ashera, ya kuma aikata abubuwa masu yawa don yă tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila yă yi fushi fiye da dukan sarakunan Isra’ila da suka riga shi.
34 During the years that Ahab [ruled], Hiel, a man from Bethel [city], rebuilt Jericho [city]. But when he started to rebuild the city, his oldest son Abiram died. And [when the city was finished, ] while Hiel was building the city gates, his youngest son Segub died. They died just like Yahweh had told Joshua would happen [to the sons of anyone who would rebuild Jericho].
A lokaci Ahab ne, Hiyel mutumin Betel ya sāke gina Yeriko. Ya kafa tushensa a bakin ran ɗan farinsa Abiram, ya kuma kafa ƙofofinsa a bakin ran autansa Segub, bisa ga maganar Ubangiji da ya yi ta wurin Yoshuwa ɗan Nun.