< 1 Kings 14 >

1 At that time, Jeroboam’s son Abijah became very sick.
A lokacin Abiya, ɗan Yerobowam ya kamu da ciwo,
2 Jeroboam said to his wife, “Disguise yourself, in order that no one will recognize that you are my wife. Then go to Shiloh [city], where the prophet Ahijah [lives]. He is the one who predicted/prophesied that I would become the king of Israel.
sai Yerobowam ya ce wa matarsa, “Ki tafi, ki ɓad da kama, don kada a gane ke a matsayin matar Yerobowam. Ki je Shilo. Annabi Ahiya yana a can, wannan wanda ya ce mini zan zama sarki a bisa wannan mutane.
3 Take with you ten [loaves of] bread and some small flat cakes, and a jar of honey, [and give them] to him. [Tell him about] our son, [and] he will tell you what will happen to him.”
Ki ɗauki dunƙulen burodi goma tare da ke, da waina, da tulun zuma, ki tafi wurinsa. Zai faɗa miki abin da zai faru da yaron.”
4 So his wife went to Shiloh, to Ahijah’s house. Ahijah was unable to see, because he was very old and had become blind.
Saboda haka matar Yerobowam ta yi abin da ya faɗa, ta kuma tafi gidan Ahiya a Shilo. Yanzu dai Ahiya ba ya gani; idanunsa sun tafi saboda tsufa.
5 But [before she got there, ] Yahweh told Ahijah that Jeroboam’s wife was coming to inquire about their son, who was very sick. And Yahweh told Ahijah what he should tell her. When she came to him, she pretended to be another woman.
Amma Ubangiji ya ce wa Ahiya, “Matar Yerobowam tana zuwa tă tambaye ka game da ɗanta, gama yana ciwo, za ka kuwa ba ta amsa kaza da kaza. Sa’ad da ta iso za tă yi kamar wata ce dabam.”
6 But when Ahijah heard her footsteps as she entered the doorway, he said to her, “Come in, wife of Jeroboam! (Why do you pretend that you are someone else?/It will not help you to pretend that you are someone else.) [RHQ] [Yahweh] has given me bad news to tell you.
Saboda haka sa’ad da Ahiya ya ji motsin sawunta a ƙofa, sai ya ce, “Ki shigo, matar Yerobowam. Me ya sa kike yi kamar wata ce dabam? An aiko ni wurinki da labari marar daɗi.
7 Go and tell Jeroboam that this is what Yahweh, the God whom we Israelis [worship], says to you: ‘I chose you from among the common people and enabled you to become the king of my Israeli people.
Je ki faɗa wa Yerobowam cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na tā da kai daga cikin mutane, na mai da kai shugaba a bisa mutanena Isra’ila.
8 I took [most of] the kingdom of Israel away from David’s descendants and gave it to you. But you have not been like David, who served me [very well]. He obeyed all my commandments very sincerely, doing only things that I considered to be right.
Na yage mulki daga gidan Dawuda na ba da shi gare ka, amma ba ka zama kamar bawana Dawuda wanda ya kiyaye umarnaina ya kuma bi ni da dukan zuciyarsa, yana yin abin da yake daidai kaɗai a idanuna ba.
9 But you have done more evil things/deeds than all those [who ruled] before you. You have rejected me, and you have caused me to become very angry by making metal images of other gods so that you [and others] could worship them.
Ka aikata mugunta fiye da dukan waɗanda suka rayu kafin kai. Ka yi wa kanka waɗansu alloli, gumakan da aka yi da ƙarfe; ka tsokane ni na yi fushi, ka kuma juye mini baya.
10 ‘So, I am going to cause terrible things to happen to your family. I will cause all your male descendants to die, young ones and old ones. I will completely get rid of your family [MTY]. I will get rid of your family [MTY] just like a man completely burns dung [to cook his food].
“‘Saboda wannan, zan kawo masifa a gidan Yerobowam. Zan yanke kowane ɗa na ƙarshe a Isra’ila, bawa ko’yantacce. Zan ƙone gidan Yerobowam kamar yadda mutum yakan ƙone juji, sai duk ya ƙone ƙurmus.
11 [The corpses of] any members of your family who die in cities will be eaten by dogs. And [the corpses of] any members of your family who die in the open fields will be eaten by vultures. [This will surely happen because] I, Yahweh, have said [that it will happen].’
Karnuka za su ci waɗanda suka mutu na Yerobowam a cikin birni, kuma tsuntsayen sararin sama za su cinye waɗanda suka mutu a jeji. Ni Ubangiji na faɗa!’
12 So go back home. And as soon as you enter the city, your son will die.
“Ke kuma, ki koma gida. Sa’ad da kika taka ƙafa a birninki, yaron zai mutu.
13 All the Israeli people will mourn for him and bury him. He is the only one of Jeroboam’s family who will be buried [properly], because he is the only one of Jeroboam’s family with whom Yahweh is pleased.
Dukan Isra’ila kuwa za su yi makoki dominsa. Shi ne kaɗai na Yerobowam wanda za a binne, domin shi ne kaɗai a gidan Yerobowam wanda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya sami wani ɗan abu mai kyau a kansa.
14 Furthermore, Yahweh will appoint for himself a king to rule over Israel who will get rid of Jeroboam’s descendants. And that [will start to happen] today!
“Ubangiji zai tā da wani sarki wa kansa a bisa Isra’ila wanda zai hallaka iyalin Yerobowam. Ko yanzu ma, wannan zai fara faruwa.
15 Yahweh will punish the people of Israel; he will shake them like [the wind] shakes the reeds [that grow in] a stream. He will expel the Israeli people from this good land that he gave to our ancestors. He will scatter them into countries east of [the Euphrates] River, because they have caused him to become very angry by [worshiping statues of] the goddess Asherah.
Ubangiji kuma zai bugi Isra’ila, har tă zama kamar kyauro mai girgiza a bakin rafi. Zai tumɓuke Isra’ila daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba wa kakanninsu, yă watsar da su gaba da Kogin Yuferites domin sun tsokane Ubangiji har ya yi fushi, ta wurin yin ginshiƙan Ashera.
16 Yahweh will abandon the Israeli people because of the sins that Jeroboam committed, sins which led the Israeli people to commit them.”
Zai kuma ba da Isra’ila saboda zunuban da Yerobowam ya yi, da ya kuma sa Isra’ila suka yi.”
17 Jeroboam’s wife returned home to Tirzah [city, the new capital of Israel]. And just as she entered her house, her son died.
Sai matar Yerobowam ta tashi ta tafi, ta kuwa tafi Tirza. Nan da nan da ta taka madogarar ƙofar gidan, sai yaron ya mutu.
18 All the Israeli people mourned for him and buried him, which is what Yahweh had told his servant, the prophet Ahijah, would happen.
Suka binne shi, dukan Isra’ila kuwa suka yi makoki dominsa, yadda Ubangiji ya faɗa ta wurin bawansa annabi Ahiya.
19 Everything else that Jeroboam did, and the record of wars that his [army] fought, and how he ruled, is written in the scroll called ‘The History of the Kings of Israel’.
Sauran ayyukan sarautar Yerobowam, da yaƙe-yaƙensa, da yadda ya yi mulki, ba a rubuce suke a littafin tarihi na sarakunan Isra’ila ba?
20 Jeroboam ruled for 22 years; then he died [EUP] and his son Nadab became king.
Ya yi mulki shekaru ashirin da biyu, sai ya huta tare da kakanninsa. Sai Nadab ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
21 Solomon’s son Rehoboam ruled Judah. He was 41 years old when he started to rule, and he ruled for 17 years. He ruled in Jerusalem, which is the city that Yahweh chose out of all the tribes of Israel to be the place where he should be worshiped [MTY]. Rehoboam’s mother’s name was Naamah; she was from the Ammon people-group.
Rehobowam ɗan Solomon ya zama sarki a Yahuda. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekaru goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga cikin dukan kabilan Isra’ila don yă sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita mutuniyar Ammon ce.
22 The people of Judah did things that Yahweh considered to be evil. They caused him to become angry because they committed more sins than their ancestors had committed: They worshiped many other gods instead of worshiping only Yahweh.
Yahuda ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Ta wurin zunuban da suka yi, sun tā da fushin kishinsa fiye da yadda kakanninsu suka yi.
23 They built places to worship those gods; on high hills, and under big trees they set up [stone] pillars to worship the goddess Asherah.
Sun kuma kafa wa kansu masujadai da suke kan tuddai, da a kan keɓaɓɓun duwatsu, suka kuma gina ginshiƙan Ashera a kowane tudu, da kuma a ƙarƙashin kowane duhuwar itace.
24 Also, there were male prostitutes at these places of worship. The Israeli people did the same disgraceful things that had been done by the people whom Yahweh had expelled while the Israelis were advancing through the land.
Har ma akwai maza karuwai na masujada. Mutane suka sa kansu ga yin kowane abin ƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora kafin Isra’ilawa.
25 When Rehoboam had been ruling for almost five years, King Shishak of Egypt came [with his army] to attack Jerusalem.
A shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam, Shishak sarkin Masar ya kai wa Urushalima yaƙi.
26 They took away all the valuable things in the temple and in the king’s palace, including the gold shields that Solomon’s [workers] had made.
Ya kwashe dukiyar haikalin Ubangiji da kuma dukiyar fadan sarki. Ya ɗauki kome, har da dukan garkuwoyi na zinariya da Solomon ya yi.
27 King Rehoboam’s [workers] made bronze shields to replace them and entrusted them to officers who guarded the entrance to the king’s palace.
Saboda haka sarki Rehobowam ya yi garkuwoyin tagulla ya mayar da su. Ya kuma naɗa waɗannan shugabannin matsara ya sa su aiki a ƙofar zuwa fadan sarki.
28 Every time that the king went into the temple, those guards carried those shields; and [when he left the temple] they returned the shields to the storeroom.
Duk sa’ad da sarki ya tafi wurin haikalin Ubangiji, matsara sukan riƙe garkuwoyinsu, daga baya kuma sai su mai da su ɗakin tsaro.
29 Everything else that Rehoboam did is written [RHQ] in the scroll called ‘The History of the Kings of Judah’.
Game da sauran ayyukan mulkin Rehobowam kuwa, da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
30 There were wars continually between [the armies of] Rehoboam and Jeroboam.
Aka ci gaba da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
31 Then Rehoboam died [EUP], and he was buried in [the part of Jerusalem called] ‘The City of David’, where his ancestors were buried. Then his son Abijah became the king.
Sai Rehobowam ya huta da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita kuwa mutuniyar Ammon ce. Sai Abiyam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.

< 1 Kings 14 >