< 1 Kings 12 >

1 All [HYP] the people of [northern] Israel went to Shechem [city] in order to appoint Rehoboam to be their king. So Rehoboam also went there.
Rehobowam ya tafi Shekem, gama dukan Isra’ila sun je can don su naɗa shi sarki.
2 When Jeroboam, who was still in Egypt, heard about that, he returned from Egypt [to Israel].
Sa’ad da Yerobowam ɗan Nebat ya ji labari (gama har yanzu yana a Masar, inda ya gudu daga Sarki Solomon), sai ya dawo daga Masar.
3 The [leaders of the northern tribes] summoned him, and they went together [to talk] to Rehoboam. They said to him,
Saboda haka mutane suka aika Yerobowam yă zo, sai shi da dukan taron Isra’ila suka tafi wurin Rehobowam, suka ce masa,
4 “Your father [Solomon] forced us to work very hard [MET] for him. If you (lighten these loads/do not force us to work that hard), and if you charge us less taxes than we were paying to him, we will serve you [faithfully].”
“Mahaifinka ya sa mana kaya mai nauyin gaske, amma yanzu ka sassauta wannan aiki mai zafi, da kuma kaya masu nauyin da ya sa a kanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
5 He replied, “Go away, and come back three days from now [and I will give you my answer].” So those leaders and Jeroboam left.
Rehobowam ya amsa, “Ku tafi, bayan kwana uku, ku dawo.” Sai mutane suka watse.
6 Then King Rehoboam consulted the older men who had advised his father Solomon while he was still living. He asked them, “What shall I say to answer those men?”
Sai Sarki Rehobowam ya nemi shawarar dattawa waɗanda suka yi wa mahaifinsa Solomon, hidima a kwanakinsa. Ya ce, “Wace shawara ce za ku ba ni don in amsa wa waɗannan mutane?”
7 They replied, “If you want to serve your people well, speak kindly to those men when you reply to them. If you do that, your people will always serve you faithfully.”
Suka amsa, “In a yau za ka zama bawan waɗannan mutane, ka kuma yi musu hidima, ka ba su amsa mai kyau, kullum za su kasance bayinka.”
8 But he ignored what the older men advised him to do. Instead, he consulted the younger men who had grown up with him, who were now (his advisors/the ones who told him what would be good to do).
Amma Rehobowam ya ƙi shawarar da dattawan suka ba shi, sai ya nemi shawarar matasa waɗanda suka yi girma tare, waɗanda kuma suke masa hidima.
9 He said to them, “What should I say to the men who are asking me to reduce the [work and taxes] that my father required from them?”
Ya tambaye su, “Mece ce shawararku? Yaya za mu amsa wa waɗannan mutane masu cewa, ‘Ka sassauta nauyin da mahaifinka ya sa a kanmu’?”
10 They replied, “This is what you should tell them: ‘My little finger is thicker than my father’s waist.
Matasan, waɗanda suka yi girma tare da shi, suka amsa, “Faɗa wa waɗannan mutanen da suka ce maka, ‘Mahaifinka ya sa kaya masu nauyi a kanmu, amma ka sassauta kayanka.’ Ka ce musu, ‘Ƙaramin yatsana ya fi ƙugun tsohona kauri.
11 What I mean is that my father required you [to work hard and pay high taxes]. But I will make those loads heavier. [It was as though] my father whipped you, but [it will be as though] I will whip you with whips that have pieces of metal in them.’”
Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.’”
12 So three days later, Jeroboam and all the leaders came to Rehoboam again, as he had told them to do.
Bayan kwana uku, Yerobowam da dukan mutane suka dawo wurin Rehobowam yadda sarki ya faɗa, “Ku dawo gare ni cikin kwana uku.”
13 The king ignored the advice of the older men and spoke harshly to the Israeli leaders.
Sai Sarki ya amsa wa mutane da zafi. Yana ƙin shawarar da dattawa suka ba shi.
14 [He told them what the younger men had advised.] He said, “My father put heavy burdens [of work and taxes] on you, but I will put heavier burdens on you. [It was as though] he beat you with whips, but I will beat you with whips that have pieces of metal in them!”
Ya bi shawarar matasa, ya ce, “Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.”
15 So the king did not pay any attention to the Israeli leaders. But this happened in order that what Yahweh wanted would occur, what he had told the prophet Ahijah about Jeroboam [becoming king of the ten tribes].
Saboda haka sarki bai saurare mutane ba, gama wannan abin da ya faru daga wurin Ubangiji ne, don a cika maganar Ubangiji da ya yi wa Yerobowam ɗan Nebat ta wurin Ahiya, mutumin Shilo.
16 When the Israeli leaders realized that the king did not pay any attention to what they said, they shouted, “We do not [RHQ] want anything to do with this descendant of King David! We will not pay attention to what this grandson of Jesse says! You people of Israel, let’s go home! As for this descendant of David [MTY], he can rule his own kingdom [MTY]!” So the Israeli leaders returned to their homes.
Da dukan Isra’ila suka ga sarki ya ƙi yă saurare su, sai suka amsa wa sarki, “Ina ruwanmu da Dawuda! Ai! Ba mu da gādo wurin ɗan Yesse. Ya Isra’ila, kowa yă koma tentinsa! Dawuda, sai ka lura da gidanka!” Saboda haka Isra’ilawa suka watse zuwa gida.
17 And [after that, ] the [only Israeli] people whom Rehoboam ruled over were those who lived in the territory of [the tribe of] Judah.
Amma ga Isra’ilawan da suke zama a garuruwan Yahuda kuwa, Rehobowam ya ci gaba da mulki a kansu.
18 Then King Rehoboam sent Adoniram [to talk to the Israeli people]. Adoniram was the man who supervised [all the men who were] forced to work [for Rehoboam]. But the Israeli people killed him by throwing stones at him. When that happened, King Rehoboam quickly got in his chariot and escaped to Jerusalem.
Sarki Rehobowam ya aiki Adoniram wanda yake shugaban aikin gandu, amma Isra’ila suka jajjefe shi da dutse har ya mutu. Sarki Rehobowam, ya sullale ya hau keken yaƙinsa ya tsere zuwa Urushalima.
19 Ever since that time, the people of [the northern tribes of] Israel have been rebelling against the descendants [MTY] of [King] David.
Tun daga wannan ranar ne mutanen Isra’ila suka shiga gāba da gidan Dawuda har wa yau.
20 When the Israeli people heard that Jeroboam had returned [from Egypt], they invited him to come to a meeting, and there they appointed him to be the king of Israel. Only the people of the tribes of Judah [and Benjamin] continued to be loyal to [the kings descended from King] [MTY] David.
Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ji Yerobowam ya dawo, sai suka aika, suka kira shi zuwa taro, suka kuma naɗa shi sarki bisa dukan Isra’ila. Kabila Yahuda kaɗai ta kasance mai biyayya ga gidan Dawuda.
21 When Rehoboam arrived in Jerusalem, he gathered 180,000 of the best soldiers from the tribes [MTY] of Judah and Benjamin. He wanted them to fight against the northern tribes of [MTY] Israel [and defeat them], in order that he could [rule all the tribes of] his kingdom again.
Da Rehobowam ya isa Urushalima, ya tattara dukan gidan Yahuda da kabilar Benyamin, ya sami sun kai mayaƙa dubu da tamanin. Sai aka shirya don su yaƙi gidan Isra’ila, su kuma mayar da masarautar wa Rehobowam ɗan Solomon.
22 But God spoke to the prophet Shemaiah and said this to him:
Amma waɗannan kalmomin Allah suka zo wa Shemahiya, mutumin Allah, cewa,
23 “Go and tell this to [Solomon’s son] Rehoboam, the king of Judah, and to all the people of the tribes of Judah and Benjamin and the people from the northern tribe who live in Judah:
“Faɗa wa Rehobowam ɗan Solomon, sarkin Yahuda, ka faɗa wa dukan gidan Yahuda da Benyamin, da kuma dukan sauran mutane,
24 ‘Yahweh says that you must not go to fight against your own relatives, the people of Israel. All of you must go home. What has happened is what Yahweh wanted to happen.’” [So Shemaiah went and told that to them, ] and they all paid attention to what Yahweh had commanded them to do, and they went home.
‘Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kada ku haura don ku yi yaƙi da’yan’uwanku, Isra’ilawa. Ku koma gida, kowannenku, gama wannan aikina ne.”’” Saboda haka suka yi biyayya da maganar Ubangiji, suka sāke watse zuwa gida, yadda Ubangiji ya umarta.
25 Then Jeroboam’s workers built [walls around] Shechem [city] in the hilly area [where the descendants] of Ephraim [lived], and he ruled from there for a while. He and his workers then left there and went to Peniel [town], and they built walls around that town.
Sai Yerobowam ya ƙara gina Shekem a ƙasar tudu ta Efraim, ya zauna a can. Daga can ya tafi ya gina Fenuwel.
26 Then Jeroboam said to himself, “If my people [continue to] go to Jerusalem and offer sacrifices to Yahweh at the temple there, soon they will again become loyal to Rehoboam, the king of Judah [DOU], and they will kill me.”
Yerobowam ya yi tunani a ransa ya ce, “Mai yiwuwa mulkin yă koma gidan Dawuda.
In waɗannan mutane sun riƙa haurawa don su miƙa hadayu a haikalin Ubangiji a Urushalima. Za su sāke nuna biyayya ga mai girma, Rehobowam, sarkin Yahuda. Za su kashe ni su kuma koma ga Sarki Rehobowam.”
28 So he consulted [his advisors, and then he did what they suggested]. He [told his workers to] make gold [statues of] two calves. Then he said to the people, “You have been going to Jerusalem [to worship] for a long time. It is a big trouble for you to continue going there. You people of Israel, look! These statues are the gods that brought our [ancestors] up from Egypt! [So you can worship these, here!]”
Bayan ya nemi shawara, sai sarki ya yi siffofin’yan maruƙa biyu na zinariya. Ya ce wa mutane, “Kun daɗe kuna haurawa zuwa can Urushalima. Ga allolinku, ya Isra’ila, waɗanda suka fitar da ku daga ƙasar Masar.”
29 He [told his workers to] place one of the statues in Bethel [city in the south] and one in Dan [city in the north].
Sai ya kafa ɗaya a Betel, ɗaya kuma a Dan.
30 So [what Jeroboam did caused] the people [to] sin. Some of them went and worshiped the calf at Bethel, and others went and worshiped the other calf at Dan.
Wannan ya zama zunubi, gama mutane suna tafiya yin wa wannan da yake a Betel sujada, su kuma je har Dan don su yi wa ɗayan sujada.
31 [Moses had declared that only men from the tribe of Levi would be priests, but] Jeroboam also told his workers to build shrines on hilltops, and then he appointed men who were not from the tribe of Levi to be priests.
Yerobowam ya gina masujadai da suke kan tuddai, ya kuma naɗa firistoci barkatai daga cikin mutanen da ba na zuriyar Lawi ba.
32 He also appointed Adonijah and two priests, Elishama and Jehoram. They had a celebration at the end of October, like the celebration [of Living in Temporary Shelters] that occurred in Judah [each year]. On the altar [that they built] in Bethel, he offered sacrifices to the gold statues of calves that they had made, and he stationed the priests there at the shrines that his workers had built.
Ya kafa biki a rana ta goma sha biyar ta watan takwas, kamar bikin da ake yi a Yahuda, ya kuma miƙa hadayu a bisa bagade. Ya yi haka a Betel, yana miƙa wa siffofin maruƙan da ya yi hadayu. A Betel kuma ya naɗa firistoci a wuraren tudun da ya yi.
33 Jeroboam went up to that altar on that day in October which he himself had chosen. There on that altar he burned incense [to be a sacrifice]. And he declared that the people should celebrate that festival [on that same day every year].
A rana ta goma sha biyar ta watan takwas, watan da ya zaɓa, ya miƙa hadayu a bisa bagaden da ya gina a Betel. Saboda haka ya kafa biki don Isra’ilawa, ya kuma haura zuwa bagade don yă miƙa hadayu.

< 1 Kings 12 >