< 1 Chronicles 11 >

1 Then the people of Israel came to David at Hebron [town] and said to him, “Listen, we have the same ancestors [IDM] that you have.
Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
2 In the past, when Saul was our king, it was you who led our Israeli [soldiers in our battles]. You are the one to whom Yahweh our God promised, ‘You will be the leader [MET] of my people; you will be their king.’”
A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
3 So all the Israeli elders came to David at Hebron. And David made a sacred agreement with them while Yahweh was listening. They anointed him [with olive oil to set him apart] to be the king of the Israeli people. That is what Yahweh had previously told [the prophet] Samuel would happen.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
4 David and all the Israeli [soldiers] [SYN] went to Jerusalem. [At that time, ] Jerusalem was called Jebus, and the people who lived there were the Jebus people-group.
Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
5 Those people said to David, “Your [soldiers] will not be able to get inside our city!” But David’s [soldiers] captured the city, even though it had strong walls around it, and since then it has been called ‘The City of David’.
suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
6 [What happened was this: ]: David said [to his soldiers], “The one who leads [our soldiers] to attack the Jebus people-group will become the commander of all my army.” Joab, the son of Zeruiah, led the soldiers, so he became the commander of all the army.
Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
7 [After they captured] the city which had strong walls around it, David moved there. That is why they named it ‘The City of David’.
Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
8 David’s workers rebuilt the city, starting where the land was filled in and extending to the wall that was around the city. Joab’s [men] repaired the other parts of the city.
Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
9 David became more and more powerful/influential, because the Almighty Commander of the armies of angels was with/helping him.
Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
10 Yahweh had promised [that David would become the king]. And all the Israeli people (were happy that David was/supported David as) their king. There were many soldiers/warriors who helped David’s kingdom to remain strong.
Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
11 This is a list of the leaders of David’s [most mighty] warriors: Jashobeam was from the Hacmon clan. He was one of the leaders of David’s most powerful soldiers. One time he fought against 300 enemies and killed them all with his spear.
Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
12 Another one was Eleazar, who was the son of Dodo from the clan of Ahoh.
Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
13 [One day] he was with David at Pas Dammim when the soldiers of Philistia gathered there for the battle. There was a field of barley there. At first the Israeli soldiers ran away from the soldiers of Philistia,
Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
14 but then David and Eleazar stopped in the middle of the field and fought to defend it and killed [many of] the soldiers of Philistia. Yahweh enabled them to win a great victory on that day.
Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
15 One time three of David’s thirty most mighty warriors came to David when he was camping next to the huge rock outside the cave near Adullam. At that same time, the army of Philistia had camped in the Rephaim Valley.
Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
16 David was in a fortress, and some of the soldiers of Philistia were occupying Bethlehem.
A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
17 [One day] David was very thirsty and said, “I wish that someone would bring me some water from the well near the gate at Bethlehem!”
Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
18 So those three most outstanding warriors forced their way through the camp of Philistia soldiers and drew some water from the well, and brought it to David. But he would not drink it. Instead, he poured it out [on the ground to be an offering] to Yahweh.
Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
19 He said, “Yahweh, it would certainly not be right for me to drink this water! That would be like [RHQ] drinking the blood of these men who were willing/ready to die for me!” So he refused to drink it. That was one of the things that those three most outstanding warriors did.
Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
20 Joab’s [younger] brother Abishai was the leader of the 30 most mighty warriors. [One time] Abishai fought 300 [enemy] soldiers with his spear and killed them.
Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
21 So he became as famous as those three most outstanding warriors. He became their commander, even though he was not one of those three men.
Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
22 Jehoiada’s son Benaiah was a brave soldier from Kabzeel [town] who did heroic deeds. He killed two of the best warriors from [the] Moab [people-group]. One day he went down into a pit when snow was falling [on the ground] and killed a lion there.
Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
23 He also killed a soldier from Egypt who was (7-1/2 feet/2.3 meters) tall. The soldier from Egypt carried a spear that was as long as a weaver’s rod. Benaiah had [only] a club, but he grabbed the other man’s spear and killed him with it.
Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
24 Those are some of the things that Benaiah did. So he became as famous as the three mighty warriors.
Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
25 He was more honored than the other members of the group of thirty most mighty warriors, but he did not become a member of the group of three most outstanding warriors. David appointed him to be the leader of his bodyguards.
Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
26 These are the names of David’s mighty warriors: Asahel, the [younger] brother of Joab; Elhanan, the son of Dodo, from Bethlehem;
Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
27 Shammah, from [the] Harod [clan]; Helez, from [the] Pelon [clan];
Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
28 Ira, the son of Ikkesh, from Tekoa [town]; Abiezer, from Anathoth [city];
Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
29 Sibbecai, from Hushah’s [clan]; Ilai from Ahoh’s clan;
Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
30 Maharai, from Netophah [town]; Heled, the son of Baanah, also from Netophah [town];
Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
31 Ithai, the son of Ribai, from Gibeah [town] in [the land that belonged to] the tribe of Benjamin; Benaiah, from Pirathon [town];
Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
32 Hurai, from the valleys near Gaash [Mountain]; Abiel from the clan of Arabah;
Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
33 Azmaveth, from Baharum [town]; Eliahba, from Shaalbon [town];
Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
34 The sons of Hashem from [the] Gizon [clan]; Jonathan the son of Shagee from the Harar [town/clan];
’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
35 Ahiam the son of Sharar/Sacar, from Harar [town/clan]; Eliphal the son of Ur;
Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
36 Hepher from the Mekerath [clan]; Ahijah from the Pelon [clan/town];
Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
37 Hezro from Carmel [city]; Naarai the son of Ezbai;
Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
38 Joel the [younger] brother of Nathan; Mibhar the son of Hagri;
Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
39 Zelek from the Ammon people-group; Naharai, the man who carried Joab’s weapons, from Beeroth [town];
Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
40 Ira and Gareb from Jattir [town];
Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
41 Uriah, [Bathsheba’s husband], from the Heth people-group; Zabad the son of Ahlai;
Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
42 Adina the son of Shiza, a leader from the tribe of Reuben, who had thirty [soldiers] with him;
Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
43 Hanan the son of Maacah; Joshaphat from Mithna [town/clan];
Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
44 Uzzia from Ashterath [town]; Shama and Jeiel, the sons of Hotham, from Aroer [city];
Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
45 Jediael the son of Shimri and his [younger] brother Joha, from Tiz [town/clan];
Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
46 Eliel from Mahavah [town/clan]; Jeribai and Joshaviah, the sons of Elnaam; Ithmah from [the] Moab [region];
Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
47 Eliel and Obed, and Jaasiel from Zobah [town/clan].
Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.

< 1 Chronicles 11 >