< Romans 11 >
1 I ask then, has God rejected his people? Certainly not! For I too am an Israelite, a descendant of Abraham, of the tribe of Benjamin.
Sai na ce, Allah ya ki mutanensa ne? Ba zai taba yiwuwa ba. Domin ni ma ba-Isra'ile ne, na zuriyar Ibrahim, a kabilar Bilyaminu.
2 God has not rejected his people whom he foreknew. Do you not know what the Scripture says in the passage about Elijah, how he pleads with God against Israel, saying,
Allah bai ki mutanen sa da ya ke da rigyasaninsu ba. Ko kun san abin da nassi ya ce game da Iliya, yadda ya kai karar Isra'ila a gaban Allah?
3 “Lord, they have killed yoʋr prophets and demolished yoʋr altars, and I alone am left, and they are seeking my life”?
Ya ce, ''Ubangiji, sun kashe annabawanka, sun rushe alfarwanka kuma, Ni kadai ne na rage, ga shi suna neman su kashe ni.''
4 But what does the divine response say to him? “I have reserved for myself seven thousand men who have not bowed down to Baal.”
Amma wacce amsa ce Allah ya ba shi? Ya ce, ''Ina da mutane dubu bakwai da na kebe don kaina, da ba su taba rusuna wa Ba'al ba.''
5 So then, in the present time also there is a remnant chosen by grace.
Ban da haka ma, ban da haka ma a wannan lokacin akwai sauran zabe na alheri.
6 Now if it is by grace, it is no longer by works, otherwise grace would no longer be grace. But if it is by works, it is no longer grace, otherwise work would no longer be work.
Amma tun da ta wurin alheri ne, ba ga ayyuka ba. In ba haka ba, alheri ba zai zama alheri ba kenan.
7 What then? Israel did not obtain what it was seeking. The chosen obtained it, but the rest were hardened,
Sai kuma me? Abin da Isra'ila ke nema, ba su samu ba, amma zababbun sun same shi, saura kuma sun taurare.
8 as it is written, “God gave them a spirit of stupor, eyes not to see and ears not to hear, down to this very day.”
Kamar yadda yake a rubuce, ''Allah ya ba su ruhun rashin fahimta, ga idanu amma ba za su gani ba, ga kunnuwa amma ba za su ji ba, har zuwa wannan rana.''
9 And David says, “Let their table become a snare and a trap, a stumbling block and a retribution to them.
Dauda kuma ya ce, ''bari teburinsu ya zama taru, da tarko, ya zama dutsen tuntube da abin ramako a gare su.
10 Let their eyes be darkened so that they cannot see, and keep their backs forever bent.”
Bari idanunsu ya duhunta domin kada su gani; bayansu kuma a duke kullum.''
11 I ask then, did the Israelites stumble so as to fall? Certainly not! Rather, by their trespass salvation has come to the Gentiles, to provoke Israel to jealousy.
Na ce, ''sun yi tuntube domin su fadi ne?'' Kada abu kamar haka ya faru. A maimakon haka, juyawa baya da suka yi ya sa, ceto ya zo ga Al'ummai, domin ya sa su kishi.
12 Now if their trespass means riches for the world, and their loss means riches for the Gentiles, how much more will it mean when their full number is included?
Idan yanzu juyawa baya da sun yi ya zama arziki ga duniya, rashin su kuma arziki ga Al'ummai, yaya kwatancin girmansa zai kasance in sun zo ga kammala?
13 Now I am speaking to you who are Gentiles. Inasmuch as I am an apostle to the Gentiles, I glorify my ministry
Yanzu ina magana da ku ku da ke Al'ummai. Tunda yake ni ne manzo ga Al'ummai, ina kuma fahariya cikin hidimata.
14 if somehow I provoke my own people to jealousy and save some of them.
Yana yiwuwa in sa ''yan'uwa na kishi, domin mu ceci wadansu su.
15 For if their rejection means reconciliation for the world, what will their acceptance mean but life from the dead?
Idan kinsu ya kawo sulhuntawa ga duniya, Karbarsu kuma zata zama yaya? Zata zama rai ne daga mutuwa.
16 If the dough offered as firstfruits is holy, so is the whole lump; and if the root is holy, so are the branches.
'ya'yan farko sunan haka ma kakkabensu yake, Idan saiwar itace na nan, haka ma rassan za su zama.
17 Now if some of the branches have been broken off, and yoʋ, a wild olive branch, have been grafted in among them and have become a fellow partaker of the root and richness of the olive tree,
Amma idan an karye wasu daga cikin rassan, idan ku rassan zaitun na ainihi ne, da aka samu daga cinkinsu, kuma idan kuna da gado tare da su, acikin saiwar itacen zaitun din.
18 do not boast against the branches. But if yoʋ do boast against them, remember that yoʋ do not sustain the root, but the root sustains yoʋ.
Kada ku yi fahariya a kan rassan. Amma idan kuka yi fahariya to ba ku bane masu karfafa saiwar amma saiwar ce ke karfafa ku.
19 Yoʋ will say then, “Branches were broken off so that I could be grafted in.”
Kana iya cewa, ''An karye rassan domin a same ni a ciki.''
20 Right! They were broken off because of unbelief, but yoʋ stand because of faith. So do not be arrogant, but be afraid.
Wannan gaskiya ne! Saboda rashin bangaskiyarsu ne ya sa aka karye su daga rassan, amma ku tsaya da karfi acikin bangaskiyarku. Kada ku dauki kanku fiye da yadda ya kamata, amma ku ji tsoro.
21 For if God did not spare the natural branches, perhaps he will not spare yoʋ either.
Domin idan Allah bai bar ainihin rassan ba, to ba zai bar ku ba.
22 Consider therefore the kindness and severity of God: to those who have fallen, severity; but to yoʋ, kindness, if yoʋ continue in his kindness; otherwise yoʋ too will be cut off.
Ku duba yadda irin ayyuka masu tsananni na Allah. Ta daya hannun kuma, tsanannin kan zoa kan Yahudawa wadanda suka fadi. Har 'ila yau jinkai Allah ya zo maku, idan kun cigaba cikin alherinsa baza a sare ku ba. Amma in kun ki za a sare ku.
23 And if they do not continue in unbelief, they will be grafted in; for God is able to graft them in again.
Hakanan, idan ba su ci gaba cikin rashin bangaskiyarsu ba, za a maida su cikin itacen. Domin Allah zai iya sake maida su.
24 For if yoʋ were cut off from what is by nature a wild olive tree and were grafted contrary to nature into a cultivated olive tree, how much more will the natural branches be grafted back into their own olive tree?
Idan an yanke ka daga itacen zaitun da ke na jeji, har ya yiwu an hada ka cikin itacen zaitun na ainihi, yaya kuma wadannan Yahudawa wadanda sune ainihin rassan, da za'a maido cikin zaitun da ke na ainihi?
25 I do not want you to be unaware, brothers, of this mystery, lest you be wise in your own estimation: A partial hardening has come upon Israel until the full number of Gentiles has come in,
Yan'uwa, ba na so ku kasance cikin duhu a game da wannan asirin, domin kada ku zama da hikima cikin tunaninku. Wannan asirin shine cewa wannan taurarewa ta faru a Isra'ila, har sai da Al'ummai suka shigo ciki.
26 and in this way all Israel will be saved, as it is written, “The Deliverer will come from Zion and will remove ungodliness from Jacob.”
Ta haka dukan Isra'ila za su tsira, kamar yadda yake a rubuce: ''Daga cikin Sihiyona mai Kubutarwa zai fito; Zai kawar da kazanta daga cikin Yakubu.
27 “And this will be my covenant with them, when I take away their sins.”
Wannan zai zama alkawarina da su, sa'adda na kawar da zunubansu.''
28 With respect to the gospel, the Israelites are enemies for your sake; but with respect to being chosen, they are beloved for the sake of the fathers.
A wani bangaren kuma game da bishara, su makiya ne amamadinku, ta wani fannin kuma bisa ga zabin Allah su kaunattatu ne saboda ubanni.
29 For the gifts and calling of God are irrevocable.
Domin baye-baye da kiran Allah basa canzawa.
30 Just as you were once disobedient to God but have now received mercy because of their disobedience,
Domin ku ma da ba ku yin biyayya ga Allah, amma yanzu kun sami jinkai saboda rashin biyayyarsu.
31 so they too have now become disobedient in order that, by the mercy shown to you, they also may receive mercy.
Ta wannan hanyar dai, wadannan Yahudawan sun zama marasa biyayya. Sakamakon haka shine ta wurin jinkan da aka nuna maku, suma su samu jikai yanzu.
32 For God has confined all in disobedience so that he might have mercy on all. (eleēsē )
Domin Allah ya rufe kowa ga rashin biyayya, domin ya nuna jinkai ga kowa. (eleēsē )
33 Oh the depth of the riches, wisdom, and knowledge of God! How unsearchable are his judgments and untraceable his ways!
Ina misalin zurfin wadata da kuma hikima da sani na Allah! Hukunce-hukuncensa sun fi gaban a bincika, hanyoyinsa kuma sun fi gaban ganewa!
34 “For who has known the mind of the Lord, or who has become his counselor?”
Don wanene ya san tunanin Ubangiji? Wanene kuma ya zama mai bashi shawara?
35 “Or who has first given to God, that he should be repaid?”
Ko kuma, wanene ya fara ba Allah wani abu, domin a biya shi?''
36 For from him and through him and to him are all things. To him be the glory forever. Amen. (aiōn )
Daga wurinsa ne, ta wurinsa ne kuma, a gare shi ne kuma dukan abu suka fito. A gare shi daukaka ta tabbata har abada. Amin. (aiōn )