< Revelation 20 >
1 Then I saw an angel coming down from heaven, holding in his hand the key to the abyss and a great chain. (Abyssos )
Sai na ga mala'ika na saukowa daga sama. Yana da makullin rami marar iyaka, yana kuma da babar sarka a hannunsa. (Abyssos )
2 He seized the dragon, the ancient serpent, who is the devil and Satan, the deceiver of the whole world, and he bound him for a thousand years.
Sai ya dauki tsohon macijin, wanda shine iblis, ko shaidan, ya daure shi shekaru dubu.
3 He threw him into the abyss and locked and sealed it over him, so that he would no longer deceive the nations until the thousand years were completed. After that he must be released for a short time. (Abyssos )
Ya jefa shi cikin rami marar iyaka, ya rufe shi ya kuma sa hatimi a bisansa. Hakan ya faru ne domin kada ya kara yaudarar al'ummai har sai bayan shekaru dubu. Bayan wannan, dole a sake shi na dan lokaci. (Abyssos )
4 Then I saw thrones, and those who sat on them were given authority to judge. I also saw the souls of those who had been beheaded for the testimony of Jesus and for the word of God. They had not worshiped the beast or his image and had not received the mark on their foreheads or their hands. They came to life and reigned with Christ for the thousand years.
Sa'annan na ga kursiyoyi. Wadanda ke zaune a bisansu sune wadanda aka ba ikon hukunci. Na kuma ga rayukan wadanda aka fille wa kai saboda shaidar Yesu da maganar Allah. Ba su yi wa dabban sujada ba ko siffarsa, suka ki su karbi alamar a goshinsu ko a hannu. Sun sake rayuwa, suka yi mulki tare da Kristi shekaru dubu.
5 (The rest of the dead did not come to life until the thousand years were completed.) This is the first resurrection.
Sauran matattun basu sake dawowa da rai ba har sai da shekaru dubu din suka cika. Wannan shine tashin matattu na fari.
6 Blessed and holy are those who take part in the first resurrection. The second death has no power over them, but they will be priests of God and of Christ, and will reign with him for a thousand years.
Mai albarka ne mai tsarki ne kuma wanda yake da rabo cikin tashin matattu na fari! Mutuwa ta biyu ba ta da iko akan wadannan. Za su zama firistocin Allah da na Almasihu za su kuma yi mulki tare da shi shekaru dubu.
7 When the thousand years are completed, Satan will be released from his prison
Sa'adda shekaru dubu suka zo ga karshe, za a saki shaidan daga kurkukunsa.
8 and will go out to deceive the nations that are at the four corners of the earth, Gog and Magog, to gather them for battle; their number is like the sand of the sea.
Za ya fito domin ya yaudari al'ummai da ke kursuyoyi hudu na duniya, Gog da Magog ya tattara su domin yaki. Yawan su zai zama kamar yashin teku.
9 They marched up over the breadth of the earth and surrounded the camp of the saints and the beloved city, but fire came down out of heaven from God and devoured them.
Suka bazu a fuskar duniya suka kuma kewaye sansanin masu ba da gaskiya, kaunataccen birni. Amma wuta ta sauko daga sama ta lankwame su.
10 And the devil, who had deceived them, was thrown into the lake of fire and sulfur, where the beast and the false prophet had been thrown, and they will be tormented day and night forever and ever. (aiōn , Limnē Pyr )
Shaidan, wanda ya yaudare su, aka jefa shi cikin korama ta farin wuta mai ci, inda aka jefa dabban da makaryacin annabin. Za su sha azaba dare da rana har abada abadin. (aiōn , Limnē Pyr )
11 Then I saw a great white throne and one who sat upon it. The earth and the sky fled from his face, and no place was found for them.
Sai na ga babban kursiyi da wanda ke zaune a kansa. Duniya da sama suka guje wa fuskarsa, amma babu wurin da za su tafi.
12 And I saw the dead, great and small, standing before the throne, and books were opened. Then another book was opened, which is the book of life. And the dead were judged by what was written in the books, according to their works.
Na ga matattu manya da kanana- suna tsaye gaban kursiyin, aka bude litattafai. Sai aka bude wani littafi - Littafin rai. Aka yi wa matattu shari'a bisa ga abinda aka rubuta cikin litattafan, gwargwadon ayyukansu.
13 Then the sea gave up the dead who were in it, and Death and Hades gave up the dead who were in them, and each person was judged according to his works. (Hadēs )
Teku ta ba da matattun dake cikinta. Mutuwa da hades suka ba da matattun da ke cikinsu, aka yi masu shari'a gwargwadon abin da suka yi. (Hadēs )
14 Then Death and Hades were thrown into the lake of fire. This is the second death, the lake of fire. (Hadēs , Limnē Pyr )
Aka jefa mutuwa da hades cikin tafkin wuta. Wannan shine mutuwa ta biyu - tafkin wuta. (Hadēs , Limnē Pyr )
15 If anyone's name was not found written in the book of life, he was thrown into the lake of fire. (Limnē Pyr )
Duk wanda ba a sami sunansa a rubuce cikin littafin rai ba, aka jefar da shi cikin tafkin wuta. (Limnē Pyr )