< Revelation 1 >
1 The revelation of Jesus Christ, which God gave him to show his servants what must soon take place. He made it known by sending his angel to his servant John,
Wannan shine wahayin Yesu Almasihu da Allah ya bashi ya nuna wa bayinsa abinda zai faru ba da dadewa ba. Ya bayyana wannan ta wurin aiko da mala'ikansa ga bawansa Yahaya.
2 who testified to the word of God and the testimony of Jesus Christ, even to all that he saw.
Yahaya yayi shaida akan abinda ya gani game da maganar Allah da kuma shaidar da aka bayar game da Yesu Almasihu.
3 Blessed is he who reads and those who hear the words of this prophecy and keep what is written in it, for the time is near.
Mai albarka ne wanda ke karanta littafin nan da murya mai karfi, da kuma wadanda ke sauraron kalmomin wannan annabci kuma suke biyayya da abinda aka rubuta a ciki, domin kuwa lokaci ya kusato.
4 John to the seven churches in Asia: Grace to you and peace from God, who is and who was and who is to come, and from the seven Spirits who are before his throne,
Ni Yahaya, zuwa ga ikilisiyoyi bakwai na kasar Asiya: alheri zuwa gare ku da salama daga wanda ke yanzu, wanda ya kuma kasance a da, shi ne kuma mai zuwa nan gaba, kuma daga ruhohin nan bakwai da ke gaban kursiyinsa,
5 and from Jesus Christ, the faithful witness, the firstborn from the dead, and the ruler of the kings of the earth. To him who loves us and washed us from our sins with his blood
kuma daga Yesu Almasihu, wanda ke amintaccen mashaidi, dan fari na tashi daga cikin matattu, kuma mai mulkin sarakunan duniya. Ga wanda ya ke kaunar mu ya kuma kwance mu daga daurin zunubanmu ta wurin jininsa,
6 and made us to be a kingdom, priests to his God and Father—to him be the glory and the power forever and ever. Amen. (aiōn )
ya maishe mu masu mulki, firistoci na Allahnsa da Ubansa - daukaka da iko su tabbata gare shi har abada abadin, Amin. (aiōn )
7 Behold, he is coming with the clouds, and every eye will see him, even those who pierced him, and all the tribes of the earth will wail on account of him. So shall it be! Amen.
Duba yana zuwa tare da gizagizai, kowane ido zai gan shi, har ma da wadanda suka soke shi. Haka kuma dukkan kabilun duniya za su yi makoki saboda da shi. I, Amin.
8 “I am the Alpha and the Omega,” says the Lord God, “who is and who was and who is to come, the Almighty.”
“Nine na farko da na karshe”, in ji Ubangiji Allah, “Wanda yake shine a yanzu, shine wanda ya kasance a da, kuma shi ne mai zuwa nan gaba, Mai iko duka.”
9 I, John, your brother and partner in the tribulation, kingdom, and endurance that are in Christ Jesus, was on the island called Patmos because of the word of God and the testimony of Jesus Christ.
Ni, Yahaya- dan'uwan ku da wanda ke tarayya daku cikin shan wahala, da mulki da tsawon jimrewa wadanda ke cikin Yesu - ina tsibirin da ake kira Batmusa saboda maganar Allah da kuma shaida game da Yesu.
10 I was in the Spirit on the Lord's day, and I heard behind me a loud voice like that of a trumpet,
Ina cikin Ruhu a ranar Ubangiji. Sai naji wata murya mai karfi a baya na kamar ta kaho.
11 saying, “Write what yoʋ see in a book and send it to the seven churches: to Ephesus, Smyrna, Pergamum, Thyatira, Sardis, Philadelphia, and Laodicea.”
Ta ce, “Rubuta abinda ka gani a cikin littafi, ka kuma aika wa ikilisiyoyin nan bakwai - ga Afisus, ga Simirna, ga Birgamas, ga Tayatira, ga Sardisu, ga Filadalfiya, da kuma ga Laudikiya.”
12 Then I turned in that direction to see the voice that was speaking to me. And when I turned, I saw seven golden lampstands,
Na juya don in ga wanda muryarsa ke magana da ni, da na juya sai na ga fitilu bakwai akan madorin su
13 and in the midst of the seven lampstands I saw one like a son of man, clothed with a robe reaching down to his feet and with a golden sash wrapped around his chest.
A tsakiyar fitilun akwai wani mai kama da dan mutum, yana sanye da doguwar tufa har tafin sawunsa, da damara ta zinariya kewaye a kirjinsa.
14 His head and his hair were white like wool, as white as snow. His eyes were like a flame of fire,
Kansa da gashinsa fari fat kamar auduga - kamar dusar kankara, kuma idanun sa kamar harshen wuta.
15 his feet were like burnished bronze refined in a furnace, and his voice was like the roar of many waters.
Kafaffunsa kamar gogaggiyar tagulla, kamar tagullar da aka tace da wutar makera, muryar sa kuma kamar kugin ambaliyar ruwan teku ne.
16 In his right hand he held seven stars, and out of his mouth came a sharp two-edged sword. His face was like the sun shining in its strength.
A hannunsa na dama yana rike da taurari bakwai, daga bakinsa kuma kakkaifan takobi mai kaifi biyu ke fitowa. Fuskarsa tana haskakawa kamar sa'adda rana ke haskakawa kwarai.
17 When I saw him, I fell at his feet as dead. But he placed his right hand on me and said, “Do not be afraid. I am the first and the last,
Lokacin da na gan shi, na fadi kamar mataccen mutum a kafaffunsa. Ya dora hannunsa na dama a kaina ya ce, “Kada ka ji tsoro. Nine na farko da na karshe,
18 the living one. I was dead, but behold, I am alive forevermore. Amen. I have the keys of Death and Hades. (aiōn , Hadēs )
da kuma wanda ke raye. Na mutu, amma duba ina raye har abada! Kuma ina da mabudin mutuwa da na hades. (aiōn , Hadēs )
19 Therefore write what yoʋ have seen, what is now and what will take place after this.
Domin haka ka rubuta abinda ka gani, abin da ke yanzu, da abin da zai faru bayan wanan.
20 This is the mystery of the seven stars that yoʋ saw in my right hand and the seven golden lampstands: The seven stars are the angels of the seven churches, and the seven lampstands are the seven churches.
Akan boyayyar ma'ana game da taurari bakwai da ka gani a hannun dama na, da madorin fitilu bakwai na zinariya: Taurarin nan bakwai mala'iku ne na ikilisiyoyi bakwai, kuma madorin fitilun nan bakwai ikilisiyoyi ne bakwai.