< Matthew 25 >
1 “At that time the kingdom of heaven will be like ten virgins who took their lamps and went out to meet the bridegroom.
Sa'annan mulkin sama zai zama kamar budurwai goma da suka dauki fitilunsu domin su taryi ango.
2 Five of them were wise, and five were foolish.
Biyar daga cikin su masu hikima ne biyar kuma wawaye.
3 When those who were foolish took their lamps, they did not take oil with them,
Sa'adda wawayen budurwai suka dauki fitilunsu, ba su dauki karin mai ba.
4 but the wise took oil in their flasks along with their lamps.
Amma budurwai masu hikimar suka dauki gorar mai tare da fitilunsu.
5 When the bridegroom was delayed, they all became drowsy and slept.
To da angon ya makara, dukkan su sai suka fara gyangyadi sai barci ya dauke su.
6 But in the middle of the night there was a shout: ‘Behold, the bridegroom is coming! Come out to meet him.’
Amma da tsakkar dare sai aka yi shela, 'Ga ango ya iso! Ku fito taryensa.
7 Then all the virgins rose and trimmed their lamps.
Sai dukka budurwan nan suka tashi suka gyaggyara fitilunsu.
8 And the foolish ones said to the wise, ‘Give us some of your oil, for our lamps are going out.’
Wawayen su ka ce da masu hikimar, 'Ku sammana kadan daga manku gama fitilunmu su na mutuwa.'
9 But the wise replied, ‘No, there will not be enough for us and for you. Instead, go to those who sell oil and buy some for yourselves.’
“Amma masu hikimar suka ce 'Tun da man ba zai ishe mu tare da ku ba, sai ku je gun ma su sayarwa ku sayo wa kanku.
10 But while they were on their way to buy it, the bridegroom came, and those who were ready went in with him to the wedding feast. Then the door was shut.
Sa'adda suka tafi sayan man, sai angon ya shigo, kuma wadanda suke a shirye su ka shiga tare da shi bukin auren, sai aka rufe kofar.
11 Afterward the other virgins also came, saying, ‘Lord, Lord, open the door for us.’
Bayan dan lokaci kadan sauran budurwan suka dawo suna cewa, 'Mai gida, mai gida, bude mana kofar.'
12 But he answered, ‘Truly I say to you, I do not know you.’
Amma ya amsa ya ce, 'A gaskiya ina gaya maku, ni ban san ku ba.'
13 Therefore keep watch, for you do not know the day or the hour in which the Son of Man is coming.
Don haka sai ku lura, don baku san rana ko sa'a ba.
14 “For it is just like a man about to go on a journey, who called his servants and entrusted his possessions to them.
Domin yana kama da wani mutum da zai tafi wata kasa. Ya kira barorinsa ya ba su dukiyar sa.
15 To one he gave five talents, to another two talents, and to another one talent, each according to his ability. And he immediately went on his journey.
Ga wani ya ba shi talanti biyar, ga wani ya ba shi biyu, ga wani kuma ya ba shi talanti daya. kowa an bashi gwargwadon iyawarsa, sai wannan mutum ya yi tafiyar sa
16 The man who had received the five talents went and traded with them, and made five more talents.
nan da nan sai wanda ya karbi talanti biyar ya sa nasa a jari, ya sami ribar wasu talanti biyar.
17 In the same way, the man who had received the two talents also earned two more.
Haka ma wanda ya karbi talanti biyu ya sami ribar wasu biyu.
18 But the man who had received the one talent went and dug a hole in the ground and hid his master's money.
Amma bawan da ya karbi talanti dayan ya yi tafiyar sa, ya haka rami, ya binne kudin mai gidansa.
19 “After a long time the master of those servants came and settled accounts with them.
To bayan tsawon lokaci sai ubangidan barorin nan ya dawo, domin yayi lissafin kudinsu.
20 The man who had received the five talents came to him and brought the other five talents, saying, ‘Master, yoʋ entrusted me with five talents; behold, I have earned five more talents besides them.’
Bawan da ya karbi talanti biyar, ya kawo nasa da ribar wasu biyar. Yace, 'Maigida, ka bani talanti biyar, gashi na samo ribar karin talanti biyar.'
21 His master said to him, ‘Well done, good and faithful servant! Yoʋ have been faithful over a few things; I will set yoʋ over many things. Enter into the joy of yoʋr master.’
Maigidansa yace masa, 'Madalla, bawa na gari mai aminci! Ka yi aminci akan abu kadan. Zan sa ka akan abubuwa masu yawa. Ka shiga cikin farincikin maigidanka.'
22 The man who had received the two talents also came to him and said, ‘Master, yoʋ entrusted me with two talents; behold, I have earned two more talents besides them.’
Bawan da ya karbi talanti biyun, ya zo yace, 'Maigida, ka ba ni talanti biyu. Gashi kuwa na sami karin ribar wasu biyun.'
23 His master said to him, ‘Well done, good and faithful servant! Yoʋ have been faithful over a few things; I will set yoʋ over many things. Enter into the joy of yoʋr master.’
Ubangidansa yace masa, 'Madalla, kai bawa na gari mai aminci! Ka yi aminci akan abubuwa kadan. Zan saka akan abubuwa masu yawa. Ka shiga cikin farincikin maigidanka.'
24 Then the man who had received the one talent came to him and said, ‘Master, I knew that yoʋ were a hard man, reaping where yoʋ did not sow and gathering where yoʋ scattered no seed.
Sai bawan da ya karbi talanti daya ya zo yace, 'Maigida, na san kai mai tsanani ne. Kana girbi inda baka yi shuka ba, kuma kana tattarawa inda ba ka watsa ba.
25 So I was afraid and went and hid yoʋr talent in the ground. Behold, yoʋ have what is yoʋrs.’
Na ji tsoro, don haka sai na je na boye talantinka a rami. Duba, ga abinda yake naka.'
26 But his master answered him, ‘Yoʋ evil and lazy servant! Yoʋ knew, did yoʋ, that I reap where I have not sown and gather where I have scattered no seed?
Amma ubangidansa ya amsa yace, kai mugu malalacin bawa, ka san cewa ni mai girbi ne inda ban shuka ba kuma ina tattarawa inda ban zuba ba.
27 Then yoʋ should have deposited my money with the bankers, and when I came I would have received what is mine with interest.
To da ba sai ka kai kudina a banki ba, da bayan na dawo da sai in karbi abina da riba.
28 Therefore take the talent from him and give it to the one who has ten talents.
Saboda haka ku kwace talantin daga gare shi ku baiwa mai talanti goman nan.
29 For everyone who has will be given more, and he will have an abundance. But the one who does not have, even what he has will be taken away from him.
Gama ga wanda yake da shi za'a kara masa har ma a yalwace za'a kara bashi. Amma ga wanda bashi da komai abinda ke nasa ma za'a kwace.
30 And throw that worthless servant into the outer darkness. In that place there will be weeping and gnashing of teeth.’
Ku jefa wannan mugun bawan marar amfani, cikin duhu mai zurfi, inda ake kuka da cizon hakora.'
31 “When the Son of Man comes in his glory, and all the holy angels with him, he will sit down on his throne of glory.
Sa'adda Dan mutum zai zo cikin daukakarsa da dukan Mala'iku tare da shi, sa'annan zai zauna kursiyinsa na daukaka.
32 All the nations will be gathered before him, and he will separate them from one another as a shepherd separates the sheep from the goats.
A gabansa za'a tattara dukkan al'ummai, zai rarraba mutanen daya'daya, kamar yadda makiyayi yake rarraba tumaki daga awaki.
33 He will set the sheep on his right and the goats on his left.
Zai sa tumakin a hannunsa na dama, amma awakin a hannunsa na hagu.
34 Then the King will say to those on his right, ‘Come, you who are blessed by my Father, inherit the kingdom prepared for you from the foundation of the world.
Sa'annan sarkin zai ce wa na hannun damarsa, 'Ku zo ku da Ubana ya albarkata, ku gaji mulkin da aka shirya maku kafin a kafa duniya.
35 For I was hungry, and you gave me something to eat; I was thirsty, and you gave me something to drink; I was a stranger, and you took me in;
Gama na ji yunwa kuka bani abinci; Na ji kishi kuka bani ruwa; Na yi bakunci kun bani masauki;
36 I was naked, and you clothed me; I was sick, and you looked after me; I was in prison, and you came to visit me.’
Na yi huntanci kuka tufasar dani; Na yi ciwo kuka kula dani; Ina kurkuku kuka ziyarceni.'
37 Then the righteous will answer him, ‘Lord, when did we see yoʋ hungry and feed yoʋ, or thirsty and give yoʋ something to drink?
Sa'annan masu adalcin za su amsa su ce, 'Ubangiji, yaushe muka ganka kana jin yunwa muka baka abinci? Ko kana jin kishi muka baka ruwan sha?
38 When did we see yoʋ as a stranger and take yoʋ in, or naked and clothe yoʋ?
Kuma yaushe muka ganka kana bakunci har muka baka masauki? Ko kuma kana huntanci da muka tufatar da kai?
39 When did we see yoʋ sick or in prison and come to visit yoʋ?’
Yaushe kuma muka ganka kana ciwo ko a kurkuku har muka ziyarce ka?'
40 The King will answer them, ‘Truly I say to you, inasmuch as you did it to one of the least of these my brothers, you did it to me.’
Sa'annan Sarkin zai amsa masu yace, 'Hakika Ina gaya maku, duk abinda kuka yi wa daya mafi kakanta daga cikin 'yan'uwana a nan ni kuka yi wa.'
41 “Then he will say to those on his left, ‘Depart from me, you who are accursed, into the eternal fire prepared for the devil and his angels. (aiōnios )
Sa'annan zai cewa wadanda suke hannunsa na hagu, 'Ku rabu da ni, ku la'anannu, ku tafi cikin wutar jahannama da aka shirya wa Shaidan da aljannunsa, (aiōnios , questioned)
42 For I was hungry, and you did not give me anything to eat; I was thirsty, and you did not give me anything to drink;
domin ina jin yunwa baku bani abinci ba; ina jin kishi ba ku bani ruwa ba;
43 I was a stranger, and you did not take me in; I was naked, and you did not clothe me; I was sick and in prison, and you did not look after me.’
Ina bakunci amma baku bani masauki ba; ina huntanci, baku tufasar da ni ba; ina ciwo kuma ina kurkuku, baku kula da ni ba.'
44 Then they too will answer, ‘Lord, when did we see yoʋ hungry or thirsty or as a stranger or naked or sick or in prison, and not take care of yoʋ?’
Sa'annan suma zasu amsa su ce, 'Ubangiji, yaushe muka ganka kana jin yunwa, ko kishin ruwa, ko kana bakunci, ko kana huntanci, ko ciwo, kuma a kurkuku, da bamu yi maka hidima ba?'
45 He will answer them, ‘Truly I say to you, inasmuch as you did not do it to one of the least of these, neither did you do it to me.’
Sa'annan zai amsa ya ce masu, 'Ina gaya maku hakika abin da baku iya yiwa mafi karanta daga cikin wadannan ba, ba ku yi mani ba.'
46 And these will go away into eternal punishment, but the righteous into eternal life.” (aiōnios )
Wadannan kuwa zasu tafi cikin madawwamiyar azaba amma adalai zuwa rai madawwami.” (aiōnios )