< Luke 6 >

1 On the second major Sabbath, Jesus was going through the grainfields, and his disciples were plucking heads of grain, rubbing off the husks in their hands, and eating them.
Ana nan wata Asabaci Yesu yana ratsawa cikin gonar hatsi, almajiransa kuma na karyar zangarkun hatsin, suna murtsukawa a hanayensu suna ci.
2 But some of the Pharisees said to them, “Why are you doing what is not lawful to do on the Sabbath?”
Amma wasu daga cikin Farisawa suka ce, “Saboda me kuke yin abin da bai halatta a yi a ranar Asabaci ba?”
3 Jesus answered them, “Have you not read what David did when he was hungry, he and those who were with him,
Yesu ya amsa masu, ya ce, “Ba ku karanta abin da Dauda ya yi a lokacin da yake jin yunwa ba, shi da mutanen da ke tare da shi?
4 how he entered the house of God and took and ate the bread of the Presence, which is not lawful for anyone to eat except for the priests, and how he also gave it to those who were with him?”
Ya je cikin gidan Allah, ya dauki gurasar alfarwa ya kuma ci daga ciki, ya kuma ba mazajen da ke tare da shi su ci, ko da shike ya halarta ga Firistoci ne kadai su ci.”
5 Then he said to them, “The Son of Man is Lord even of the Sabbath.”
Sai ya ce masu, “Dan Mutum shi ne Ubangijin asabaci.”
6 On another Sabbath, Jesus went into the synagogue and was teaching, and a man was there whose right hand was withered.
Ya kasance a wata ranar Asabaci ya shiga cikin majami'a ya kuma koya wa mutane a can. Wani mutum na can wurin wanda hannun damansa ya shanye.
7 Now the scribes and the Pharisees were watching Jesus closely to see if he would heal on the Sabbath, so that they could find an accusation against him.
Marubuta da Farisawa na kallonsa su ga ko zai warkar da wani a ranar Asabaci, domin su samu dalilin zarginsa da yin abin da bai cancanta ba.
8 But he knew their thoughts and said to the man with the withered hand, “Rise and stand here.” So he rose and stood there.
Amma ya san abin da suke tunani, sai ya ce wa mai shanyeyen hannun, “Tashi, ka tsaya a nan tsakiyar jama'a.” Sai mutumin ya tashi ya tsaya a nan.
9 Then Jesus said to them, “Let me ask you something: Is it lawful on the Sabbath to do good or to do evil, to save life or to kill?”
Yesu ya ce masu, “Ina tambayar ku, ya halatta a ranar Asabaci a yi nagarta ko mugunta, a ceci rai ko a hallaka shi?
10 And after looking around at them all, he said to the man, “Stretch out yoʋr hand.” The man did so, and his hand was restored, becoming as sound as the other.
Sai ya dube su duka, ya kuma ce wa mutumin, “Mika hannunka.” Ya yi haka, sai hannunsa ya koma lafiyayye.
11 But the scribes and Pharisees were filled with mindless rage and discussed with one another what they might do to Jesus.
Amma suka fusata kwarai, suka yi shawara da junansu game da abin da za su yi da Yesu.
12 One day soon afterward Jesus went out to the mountain to pray, and spent the whole night in prayer to God.
Ya zama a kwanakin nan, ya hawo bisan dutse domin ya yi addu'a. Ya ci gaba dukan dare yana addua'a ga Allah.
13 When daybreak came, he called his disciples and chose twelve from among them, whom he also named apostles:
Da safiya ta yi, ya kira almajiransa zuwa wurinsa, ya kuma zabi goma sha biyu daga cikinsu, wadanda ya kira su “Manzanni.”
14 Simon (whom he also named Peter) and Andrew his brother, James and John, Philip and Bartholomew,
Sunayen Manzannin sune Siman (wanda ya kuma kira Bitrus) da dan'uwansa, Andrawus, Yakubu, Yahaya, Filibus, Bartalamawus,
15 Matthew and Thomas, James the son of Alphaeus, and Simon (who was called the Zealot),
Matta, Toma, Yakubu dan Halfa, Siman, wanda ake kira Zaloti, Yahuda dan Yakubu,
16 Judas the son of James, and Judas Iscariot (who became a traitor).
da Yahuda dan Iskariyoti, wanda ya zama maci amana.
17 Then Jesus came down with them and stood on a level place. A crowd of his disciples was there along with a great multitude of people from all Judea, Jerusalem, and the coastal region of Tyre and Sidon (who had come to hear him and to be healed of their diseases),
Sai Yesu ya gangaro daga dutsen tare da su, suka kuma tsaya a sarari. Almajiransa da yawa na nan a wurin, tare da mutane da yawa daga Yahudiya da Urushalima, da kuma bakin tekun Taya da Sidon.
18 as well as people who were harassed by unclean spirits. And they were healed.
Sun zo domin su ji shi, da kuma su sami warkarwa daga dukan cututukansu. Mutane waddan da ke fama da kazaman ruhohi ma sun sami warkarwa.
19 The entire crowd was trying to touch him, because power was coming out from him and healing them all.
Dukan taron jama'ar suna kokarin su taba shi domin ikon warkarwa yana fitowa daga wurinsa, ya kuma warkar da su duka.
20 Then he looked up at his disciples and said, “Blessed are you who are poor, for yours is the kingdom of God.
Sai ya dubi almajiransa ya ce, “Masu albarka ne ku matalauta, gama Mulkin Allah naku ne.
21 Blessed are you who hunger now, for you will be filled. Blessed are you who weep now, for you will laugh.
Masu albarka ne ku masu yunwa yanzu, domin za a kosar da ku. Masu albarka ne ku masu kuka a yanzu, domin za ku yi dariya.
22 Blessed are you when others hate you, when they exclude you, reproach you, and spurn your name as evil on account of the Son of Man.
Masu albarka ne ku idan mutane sun ki ku, suka nuna maku wariya suna mai da sunayen ku na mugunta, domin Dan Mutum.
23 Rejoice in that day and leap for joy, for behold, great is your reward in heaven, for their fathers treated the prophets in the same way.
Za ku yi farin ciki a ranan nan kuna tsalle domin murna, domin hakika za ku samu lada mai girma a sama, domin haka kakannin-kakannin su suka yi wa annabawa.
24 But woe to you who are rich, for you have received your comfort.
Amma kaitonku mawadata! Domin kun rigaya kun samu ta'aziyar ku.
25 Woe to you who are filled, for you will hunger. Woe to you who laugh now, for you will mourn and weep.
Kaitonku kosassu a yanzu! Domin za ku ji yunwa nan gaba. Kaitonku masu dariya yanzu! Domin za ku yi makoki kuna kuka nan gaba.
26 Woe to you when others speak well of you, for their fathers treated the false prophets in the same way.
Kaiton ku idan kowadanne mutane suna yabon ku! Domin haka kakannin-kakanninsu suka yi wa annabawan karya.
27 “But I say to you who are listening, love your enemies, do good to those who hate you,
Amma ina ce maku ku masu saurare na, ku kaunaci magabtanku, ku kuma aikata nagarta ga wadanda suke kinku.
28 bless those who curse you, and pray for those who mistreat you.
Ku albarkaci masu zaginku, ku kuma yi addu'a ga wadanda suke wulakanta ku.
29 If anyone strikes yoʋ on one cheek, offer him the other also. If anyone takes away yoʋr cloak, do not withhold yoʋr tunic from him either.
Wanda ya mare ku a wannan kunci, ku juya masa dayan. Idan wani ya dauki mayafinka, kada ka hana masa taguwarka.
30 Give to everyone who asks of yoʋ, and if anyone takes away yoʋr belongings, do not demand them back.
Ku bayar ga duk wanda ya roke ku. Idan wani ya dauki wani abu da ke naku, kada ku bidi ya mayar da shi.
31 As you wish that others would do to you, do the same also to them.
Duk abin da kake so mutane su yi maka, ka yi masu hakan nan.
32 If you love those who love you, what benefit is that to you? For even sinners love those who love them.
Idan ka kaunaci masoyan ka ne kadai, me wannan zai amfane ka? Ko masu zunubi ma na kaunar masoyan su.
33 And if you do good to those who do good to you, what benefit is that to you? For even sinners do the same.
Idan kuna nuna alheri ga wadan da ke maku alheri kadai, menene ladan ku a nan? Ko masu zunubi ma na yin hakan nan.
34 And if you lend to those from whom you expect to receive something back, what benefit is that to you? For even sinners lend to other sinners in order to receive back the same amount.
Idan kun ba da rancen abubuwa ga mutanen da kuna sa zuciya zasu mayar maku ne kadai, menene ribar ku a nan? Ko masu zunubi suna ba masu zunubi rance, suna kuma sa zuciya a mayar masu dadai gwargwado.
35 But love your enemies, do good to them, and lend to them without expecting anything in return. Then your reward will be great, and you will be sons of the Most High, for he is kind to the ungrateful and the evil.
Amma ku kaunaci magabtan ku, ku kuma nuna masu alheri. Ku basu rance, kada ku sa zuciya a maido maku, kuma sakamakon ku zai zama da girma. Za ku zama yayan Mafifici, domin shi da kansa yana nuna jinkai ga marasa godiya da miyagun mutane.
36 Therefore be merciful, just as your Father is merciful.
Ku zama masu jinkai, domin Ubanku mai jinkai ne.
37 “Do not judge, and you will certainly not be judged. Do not condemn, and you will certainly not be condemned. Forgive, and you will be forgiven.
Kada ku shari'anta, kuma ba za a shari'anta ku ba. Kada ku kayar, ku ma ba za a kashe ku ba. Ku yafe wa wasu, kuma za a yafe maku.
38 Give, and it will be given to you. A good measure, pressed down, shaken together, and running over, will be put into your lap. For with the same measure you use it will be measured to you in return.”
Ku bayar ga wasu, ku ma za a ba ku da yawa. Magwaji dankararre, girgizajje har ya cika yana zuba, za su zuba har cinyarku. Domin duk ma'aunin da ku ka yi amfani da shi, da shi za a auna maku.
39 He also told them a parable: “Can one blind person guide another? Will they not both fall into a pit?
Sai ya sake basu wani misali, “Makaho yana iya yi wa makaho jagora? Idan ya yi haka, dukansu biyu za su fada cikin rami, ko ba haka ba?
40 A disciple is not above his teacher, but everyone who is fully trained will be like his teacher.
Almajiri baya fin Malaminsa, amma duk wanda ya samu horo sosai zai zama kamar malaminsa.
41 Why do yoʋ see the speck in yoʋr brother's eye, but do not consider the beam in yoʋr own eye?
Don me kake duba dan hakin da ke a idon dan'uwanka, amma ba ka iya ganin gungumen da ke a idonka ba?
42 Or how can yoʋ say to yoʋr brother, ‘Brother, let me take the speck out of yoʋr eye,’ when yoʋ yoʋrself do not see the beam in yoʋr own eye? Hypocrite! First take the beam out of yoʋr own eye, and then yoʋ will see clearly to take the speck out of yoʋr brother's eye.
Don me za ka ce wa dan'uwanka, 'Dan'uwa, bari in cire dan hakin da ke a idonka', bayan kai da kanka ba ka iya ganin gungumen da ke a idonka ba? Kai munafuki! Ka fara cire gungumen da ke a idonka, sa'annan za ka gani da kyau yadda zaka cire hakin da ke a idon dan'uwanka.
43 “No good tree produces bad fruit, nor does a bad tree produce good fruit.
Domin babu itace mai kyau da ke haifar rubabbun 'ya'ya, ko rubabben itace da zai haifi kyawawan 'ya'ya.
44 Each tree is known by its own fruit. People do not gather figs from thorns, nor do they pick grapes from a bramble bush.
Domin ana iya sanin ko wani itace ta wurin 'ya'yan da yake bayarwa. Domin mutane basu kan tsinki 'ya'yan baure a jikin kaya, ko kuwa su dibi inabi daga jikin sarkakkiya.
45 The good person brings good things out of the good treasure of his heart, and the evil person brings evil things out of the evil treasure of his heart, for out of the abundance of his heart his mouth speaks.
Mutumin kirki, daga wadatar zuciyarsa ya kan ba da yaya masu kyau, kuma mugu daga cikin muguwar ajiyar zuciyarsa yake aikata mugunta. Domin daga cikar zuciyarsa ne bakinsa yakan yi magana.
46 “Why do you call me, ‘Lord, Lord,’ and not do what I say?
Don me kuke ce da ni, 'Ubangiji, Ubangiji', amma ba ku yin biyayya da magana ta?
47 I will show you what someone is like who comes to me, hears my words, and acts on them.
Duk wanda ya zo wurina ya ji kalmomina ya kuma yi biyayya da su, zan gaya maku yadda yake.
48 He is like a man building a house, who dug deep and laid a foundation on the rock. When a flood came, the river burst against that house but could not shake it, for it was founded on the rock.
Yana kama da mutum da ke gina gida, wanda ya haka da zurfi zuwa cikin kasa ya kuma gina harshashin gidan sa a kan dutse. Da rigyawa ta zo, sai ruwa ya buga gidan, amma bai iya girgiza shi ba, domin an gina shi da kyau.
49 But he who hears my words and does not act accordingly is like a man who built a house on the ground without a foundation. As soon as the river burst against that house, it fell and was utterly destroyed.”
Amma duk mutumin da ya ji kalmomina ya kuma ki biyayya da su, yana kamar mutum wanda ya gina gidansa a kan kasa, babu harshashi. Amma da ambaliyan ruwa ta buga gidan, nan take ya rushe, ragargajewar gidan kuma da girma take.

< Luke 6 >