< Luke 22 >
1 Now the Feast of Unleavened Bread was drawing near, which is called the Passover,
Anan nan idin gurasa mara yisti ya yi kusa, wanda a ke kira Idin ketarewa.
2 and the chief priests and the scribes were looking for a way to get rid of Jesus quietly, for they were afraid of the people.
Manyan firistoci da marubuta suka yi shawara yadda za su kashe Yesu, gama suna jin tsoron mutane.
3 Then Satan entered into Judas, the one called Iscariot, who was numbered among the twelve.
Shaidan ya shiga Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin goma sha biyun.
4 He went away and discussed with the chief priests and officers how he might deliver Jesus up to them.
Yahuza ya je ya yi shawara da manyan firistoci da Jarumawa yadda zai ba da Yesu a garesu.
5 They were glad and agreed to give him money.
Suka yi farin ciki, suka yarda su ba shi kudi.
6 So he accepted the offer and began looking for an opportunity to deliver Jesus up to them in the absence of a crowd.
Sai ya yarda, sai ya nimi dama yadda zai ba da shi garesu a lokacin da babu taro.
7 Then came the day for the Feast of Unleavened Bread, when the Passover lamb had to be sacrificed.
Ranar idin gurasa mara yisti ya yi, da dole za a yi hadayan rago na Idin ketarewa.
8 Jesus sent Peter and John, saying, “Go make preparations for us to eat the Passover.”
Yesu ya aiki Bitrus da Yahaya, ya ce masu, “Ku je ku shirya mana abincin Idin ketarewa, domin mu ci.”
9 They said to him, “Where do yoʋ want us to prepare it?”
Suka tambaye shi, “A ina ka ke so mu shirya?”
10 He said to them, “Behold, when you enter the city, a man carrying a jug of water will meet you. Follow him into the house he enters
Ya amsa masu, “Ku ji, sa'adda ku ka shiga birnin, wani mutum mai dauke da tulun ruwa zai same ku. Ku bishi zuwa cikin gidan da za ya shiga.
11 and say to the master of the house, ‘The Teacher asks yoʋ, “Where is the guest room where I can eat the Passover with my disciples?”’
Sai ku gaya wa mai gidan, 'Malam ya ce, “Ina dakin baki, inda zan ci abincin Idin ketarewa da almajirai na?'”
12 He will then show you a large upper room that is furnished; prepare it there.”
Zai nuna maku babban bene wanda yake a shirye. Ku shirya a can.”
13 So they went and found it just as Jesus had told them, and they prepared the Passover.
Sai suka tafi, suka sami komai kamar yadda ya gaya masu. Sai suka shirya abincin Idin ketarewan.
14 When the hour came, Jesus reclined at the table, and the twelve apostles were with him.
Sa'adda lokacin ya yi, ya zauna da almajiran.
15 He said to them, “I have earnestly desired to eat this Passover with you before I suffer.
Sai ya ce masu, “Ina da marmari matuka in ci wannan abincin Idin ketarewa da ku kamin in sha wahala.
16 For I tell you that I will certainly not eat it again until it is fulfilled in the kingdom of God.”
Gama na ce maku, ba zan ci shi kuma ba, sai dai an cika shi a mulkin Allah.”
17 Then he took a cup, and after giving thanks he said, “Take this and divide it among yourselves.
Sai Yesu ya dauki koko, sa'adda ya yi godiya, sai yace, “Karba wannan, ku rarraba a tsakaninku.
18 For I tell you, I will certainly not drink again from the fruit of the vine until the kingdom of God comes.”
Gama ina ce maku, ba zan sha wannan ruwan inabi kuma ba, sai dai mulkin Allah ya zo.”
19 Then he took bread, and when he had given thanks, he broke it and gave it to them, saying, “This is my body, which is given for you. Do this in remembrance of me.”
Sai ya dauki gurasa, sa'adda ya yi godiya, ya kakkarya shi, sai ya ba su, cewa, “Wannan jikina ne wanda aka bayar dominku. Ku yi wannan domin tunawa da ni.”
20 In the same way, he also took the cup after they had eaten supper, saying, “This cup is the new covenant in my blood, which is poured out for you.
Sai ya dauki kokon kuma bayan jibi, cewa, “Wannan koko sabon alkawari ne cikin jinina, wanda aka zubar dominku.
21 But behold, the hand of the one who is going to betray me is with mine on the table.
Amma ku yi lura. Wanda zai bashe ni yana tare da ni a teburi.
22 The Son of Man indeed goes as it has been determined, but woe to that man by whom he is betrayed.”
Gama Dan Mutum zai tafi lallai kamar yadda aka kaddara. Amma kaiton wannan mutum da shine za ya bashe shi!”
23 Then they began to discuss with one another which one of them could ever do such a thing.
Sai suka fara tambaya a tsakaninsu, wanene a cikinmu da zai yi wannan abu.
24 A dispute also arose among them as to which of them was considered to be greater.
Sai gardama ta tashi a tsakaninsu game da wanene mafi girma.
25 So Jesus said to them, “The kings of the Gentiles exercise lordship over them, and those who have authority over them are called benefactors.
Ya ce masu, “Sarakunan al'ummai suna nuna iko akansu, kuma wadanda suke da iko a kansu ana ce da su masu mulki da daraja.
26 But it must not be so with you; rather the greatest among you must become like the youngest, and the leader must become like one who serves.
Amma kada ya zama haka da ku. A maimakon haka, bari wanda ya ke mafi girma a cikinku ya zama mafi kankanta. Bari wanda yafi muhimmanci kuma ya zama kamar mai hidima.
27 For who is greater? The one who reclines at the table or the one who serves? Is it not the one who reclines at the table? But I am among you as one who serves.
Gama wanene yafi girma, wanda ya zauna a teburi, ko kuwa wanda yake yin hidima? Ba wanda ya zauna a teburi ba? Duk da haka ina kamar mai hidima a tsakaninku.
28 “You have stayed with me in my trials.
Amma ku ne wadanda ku ke tare da ni a cikin jarabobina.
29 And I bestow on you a kingdom, just as my Father bestowed one on me,
Na baku mulki, kamar yadda Ubana ya ba ni mulki,
30 so that you may eat and drink at my table. And you will sit on thrones judging the twelve tribes of Israel.”
domin ku ci ku kuma sha a teburi na mulkina. Za ku zauna a kan kursiyai kuna shari'anta kabilun nan goma sha biyu na Israila.
31 Then the Lord said, “Simon, Simon, behold, Satan has demanded to have you, so that he might sift you like wheat.
Siman, Siman, ka yi hankali, shaidan ya nemi izini a bada kai domin ya tankade ka kamar alkama.
32 But I have prayed for yoʋ that yoʋr faith may not fail. Once yoʋ have turned back, strengthen yoʋr brothers.”
Amma na yi maka addu'a, saboda kada bangaskiyarka ta fadi. Bayan da ka juyo kuma, ka karfafa 'yan'uwanka.”
33 Peter said to him, “Lord, I am ready to go with yoʋ both to prison and to death.”
Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ina shirye in tafi tare da kai zuwa cikin kurkuku da zuwa mutuwa.”
34 Jesus said, “I tell yoʋ, Peter, a rooster will certainly not crow today before yoʋ have denied three times that yoʋ know me.”
Yesu ya amsa masa, “Ina gaya maka, Bitrus, kamin caran zakara a yau, za ka yi musu na sau uku cewa ba ka sanni ba.”
35 Then Jesus said to them, “When I sent you without a moneybag, knapsack, or sandals, did you lack anything?” They said, “Nothing.”
Sa'annan Yesu ya ce masu, “Lokacin da na aike ku babu jaka, ko burgami ko takalma, ko kun rasa wani abu? Sai suka amsa, “Babu.”
36 Then he said to them, “But now he who has a moneybag must take it, and likewise a knapsack. And he who does not have a sword must sell his garment and buy one.
Ya kuma ce masu, “Amma yanzu, wanda ya ke da jaka, bari ya dauka, da kuma burgami. Wanda ba shi da takobi sai ya sayar da taguwarsa ya sayi guda.
37 For I tell you that this Scripture must still be fulfilled in me: ‘He was numbered with the lawless.’ For what is written about me is reaching its fulfillment.”
Gama ina ce maku, abin da aka rubuta game da ni dole sai ya cika, 'An lisafta shi kamar daya daga cikin masu karya doka.' Gama abinda aka fada akaina ya cika.”
38 So they said, “Lord, behold, here are two swords.” He said to them, “That is enough!”
Sai suka ce, “Ubangiji, duba! Ga takuba biyu.” Sai ya ce masu, “Ya isa.”
39 Then Jesus went out and made his way to the Mount of Olives, as was his custom, and his disciples followed him.
Bayan cin abincin yamma, Yesu ya tafi, kamar yadda ya saba yi, zuwa dutsen Zaitun, sai almajiran suka bi shi.
40 When he came to the place, he said to them, “Pray that you will not enter into temptation.”
Sa'adda suka iso, ya ce masu, “Ku yi addu'a domin kada ku shiga cikin jaraba.”
41 Then he withdrew from them about a stone's throw away and knelt down and prayed,
Ya rabu da su misalin nisan jifa, sai ya durkusa kasa ya yi addu'a,
42 “Father, if yoʋ are willing to take this cup away from me, do so; nevertheless, not my will, but yoʋrs be done.”
yana cewa “Uba, in ka yarda, ka dauke wannan kokon daga gareni. Ko da yake ba nufina ba, amma bari naka nufin ya kasance.”
43 Then an angel from heaven appeared to him and strengthened him.
Sai mala'ika daga sama ya bayyana a wurinsa, yana karfafa shi.
44 Being in agony, he prayed more earnestly, and his sweat became like drops of blood falling to the ground.
Yana cikin wahala sosai, sai ya dukufa cikin addu'a, har zufarsa kuma tana diga a kasa kamar gudajen jini.
45 When he rose from prayer and came to the disciples, he found them sleeping because of their sorrow.
Sa'adda ya tashi daga addu'arsa, sai ya zo wurin almajiran, ya same su suna barci domin bakin cikinsu,
46 So he said to them, “Why are you sleeping? Rise and pray, lest you enter into temptation.”
sai ya tambaye su, “Don me kuke barci? Tashi ku yi addu'a, saboda kada ku shiga cikin jaraba.”
47 While he was still speaking, behold, a crowd approached, and the man called Judas, one of the twelve, was leading them. He drew near to Jesus to kiss him,
Sa'adda yana cikin magana, sai, ga taron jama'a suka bayana, tare da Yahuza, daya daga cikin sha biyun, ya na jagabansu. Sai ya zo kusa da Yesu domin ya yi masa sumba,
48 and Jesus said to him, “Judas, are you betraying the Son of Man with a kiss?”
amma Yesu ya ce masa, “Yahuza, za ka ba da Dan Mutum da sumba?”
49 When those who were around him saw what was about to happen, they said to him, “Lord, shall we strike with the sword?”
Sa'adda wadanda suke kewaye da Yesu suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takobi ne?”
50 Then one of them struck the servant of the high priest, cutting off his right ear.
Sai daya daga cikinsu ya kai wa bawan babban firist sara a kunne, sai ya yanke masa kunnensa na dama.
51 But Jesus responded, “No more of this!” And he touched the man's ear and healed him.
Yesu ya ce, “Ya isa haka.” Sai ya taba kunnensa, sai ya warkar da shi.
52 Then Jesus said to the chief priests, the officers of the temple, and the elders who had come out against him, “Have you come out with swords and clubs as you would against a robber?
Yesu yace wa manyan firistoci, da masu tsaron haikali, da dattawa wadanda suke gaba da shi, “Kun fito kamar za ku kama dan fashi, da takuba da sanduna?
53 I was with you daily in the temple courts, and you did not lay a hand on me. But this is your hour, when the power of darkness reigns.”
Sa'adda nake tare da ku kowace rana a haikali, ba ku kama ni ba. Amma wannan shine lokacinku, da kuma ikon duhu.”
54 Then they arrested him, led him away, and brought him to the house of the high priest, and Peter was following at a distance.
Suka kama shi, sai suka tafi da shi, suka kawo shi cikin gidan babban firist. Amma Bitrus yana binsa daga nesa.
55 Some had kindled a fire there in the middle of the courtyard and sat down together, and Peter sat down among them.
Bayan da suka hura wuta a tsakiyar gidan da suka zazzauna tare, Bitrus ya zaune a tsakaninsu.
56 When a servant girl saw him sitting in the light of the fire, she looked at him intently and said, “This man also was with him.”
Sai wata baranya ta ganshi ya zauna a hasken wuta, sai ta zura masa ido ta ce, “Wannan mutum ma yana tare da shi.”
57 But Peter denied him, saying, “Woman, I do not know him.”
Amma Bitrus ya yi musu, yana cewa, “Mace, ban san shi ba.”
58 After a little while, someone else saw him and said, “Yoʋ also are one of them.” But Peter said, “Man, I am not.”
Bayan dan karamin lokaci sai wani mutum ya gan shi, sai ya ce, “Kaima kana daya daga cikinsu.” Amma Bitrus ya ce, “Mutumin, ba ni ba ne.”
59 After about an hour had gone by, another man kept insisting, “Truly this man also was with him, for he too is a Galilean.”
Bayan sa'a daya sai wani mutum ya nace da cewa, “Gaskiya wannan mutum yana tare da shi, gama shi dan Galili ne.”
60 But Peter said, “Man, I do not know what yoʋ are talking about!” And immediately, while he was still speaking, a rooster crowed.
Amma Bitrus ya ce, “Mutumin, ban san abin da kake fada ba.” Sai nan da nan, da yana cikin magana, sai zakara ta yi cara.
61 Then the Lord turned and looked at Peter, and Peter remembered what the Lord had said to him, “Before a rooster crows, yoʋ will deny me three times.”
Yana juyawa, sai Ubangiji ya dubi Bitrus. Sai Bitrus ya tuna kalmar Ubangiji, sa'adda ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau za ka musunce ni sau uku.”
62 And Peter went out and wept bitterly.
Da fitowarsa waje, Bitrus ya yi kuka mai zafi.
63 Now the men who were holding Jesus in custody began mocking him and beating him.
Sai mutanen da ke tsare da Yesu suka yi masa ba'a da bulala kuma.
64 They also blindfolded him and kept striking his face, saying to him, “Prophesy! Who is it that struck yoʋ?”
Bayan da suka rufe masa idanu, suka tambaye shi, cewa, “Ka yi annabci! Wa ya buge ka?”
65 And they said many other things against him, reviling him.
Suka yi wadansu miyagun maganganu na sabo game da Yesu.
66 When daybreak came, the elders of the people gathered together, both chief priests and scribes, and they led Jesus up to their Sanhedrin and said,
Da gari ya waye, sai dattawa suka hadu tare, da manyan firistoci da marubuta. Sai suka kai shi cikin majalisa
67 “If yoʋ are the Christ, tell us.” But he said to them, “If I tell you, you will surely not believe.
suka ce, “Gaya mana, in kai ne Almasihu.” Amma yace masu, “Idan na gaya maku, ba za ku gaskanta ba,
68 And if I ask you a question, you will surely not answer me or release me.
idan na yi maku tambaya, ba za ku amsa ba.
69 But from now on the Son of Man will be seated at the right hand of the power of God.”
Amma nan gaba, Dan Mutum zai zauna a hannun dama na ikon Allah.”
70 So they all said, “Are yoʋ then the Son of God?” He said to them, “You yourselves say that I am.”
Suka ce masa, “Ashe kai Dan Allah ne?” Sai Yesu ya ce masu, “Haka kuka ce, nine.”
71 Then they said, “What further testimony do we need? For we ourselves have heard it from his own mouth.”
Suka ce, “Don me muke neman shaida? Gama mu da kanmu munji daga bakinsa.”