< John 16 >
1 “I have said these things to you so that you will not fall away.
“Na fada maku wannan ne domin kada kuyi tuntube.
2 They will put you out of the synagogues; indeed, an hour is coming when anyone who kills you will think he is offering service to God.
Zasu fitar da ku daga majami'u. Amma, sa'a tana zuwa, wadda idan wani ya kasheku, zai yi zaton aikin Allah yake yi.
3 They will do these things because they have not known the Father or me.
Za suyi haka ne kuwa domin ba su san Uban ko ni ba.
4 But I have said these things to you so that when the hour comes you will remember that I said them to you. I did not say these things to you from the beginning, because I was with you.
Na fada maku wadannan abubuwa ne domin in lokacin da zasu faru yayi, ku tuna na fada maku.” Ban fada maku wadannan abubuwa ba tun da farko, domin ina tare da ku.
5 “But now I am going to him who sent me, yet none of you asks me, ‘Where are yoʋ going?’
Yanzu kuwa za ni wurin wanda ya aiko ni, duk da haka a cikinku, ba wanda ya tambaye ni, 'Ina za ka?'
6 Rather, sorrow has filled your hearts because I have said these things to you.
Amma saboda na fada maku wadannan abubuwa, bakin ciki ya cika zuciyarku.
7 But I tell you the truth, it is to your advantage that I go away, for if I do not go away, the Helper will not come to you. But if I do go, I will send him to you.
Amma ina gaya maku gaskiya: zai fi ye maku in na tafi. Domin in ban tafi ba, Mai Ta'aziyya ba zai zo gare ku ba, in kuwa na tafi, zan aiko shi gare ku.
8 And when he comes, he will convict the world concerning sin, righteousness, and judgment:
Idan kuwa ya zo, Mai Ta'aziyyar zai fadarkar da duniya a kan zunubi, da adalci, da kuma hukunci.
9 concerning sin, because they do not believe in me;
Game da zunubi, domin basu gaskata da ni ba,
10 concerning righteousness, because I am going to my Father, and you will no longer see me;
Game da adalci, domin za ni wurin Uba, kuma ba za ku sake ganina ba,
11 and concerning judgment, because the ruler of this world has been condemned.
game da hukunci kuma, domin an yanke wa mai mulki duniyan nan hukunci.
12 “I still have many things to say to you, but you cannot bear them now.
“Akwai abubuwa da yawa da zan gaya maku, amma ba za ku iya fahimta a yanzu ba.
13 When the Spirit of truth comes, he will guide you into all truth, for he will not speak on his own authority, but whatever he hears he will speak, and he will declare to you what is to come.
Saboda haka, sa'adda Ruhu na gaskiya ya zo, zai bishe ku a cikin dukan gaskiyar, domin ba zai yi magana don kansa ba, sai dai duk abin da ya ji, shi zai fada, zai kuma sanar da ku al'amuran da zasu faru.
14 He will glorify me, for he will receive from me what is mine and declare it to you.
Zai daukaka ni, domin zai dauko abubuwa dake nawa ya sanar da ku.
15 All that the Father has is mine. That is why I said that the Spirit will receive from me what is mine and declare it to you.
Duk abinda Uba yake da shi, nawa ne. Domin wannan ne nace zai dauko abubuwa da yake nawa ya sanar da ku.
16 “In a little while you will not see me; and again after a little while, you will see me, for I am going to the Father.”
“Bayan dan lokaci kadan, ba zaku kara ganina kuma ba. bayan dan lokaci kadan kuma, zaku gan ni.”
17 Then some of his disciples said to one another, “What does he mean by saying to us, ‘In a little while you will not see me; and again after a little while, you will see me,’ and, ‘for I am going to the Father’?”
Sai wadansu almajiransa sukace wa juna, “Me nene wannan da yake fadi mana, 'Bayan dan lokaci kadan ba zaku gan ni ba, bayan dan lokaci kadan kuma zaku gan ni?' da kuma, ' zan tafi wurin Uba'?”
18 So they kept saying, “What does he mean by saying, ‘a little while’? We do not know what he is talking about.”
Saboda haka sukace, “Me nene wannan da yake fada, 'Bayan dan lokaci kadan'? Bamu san abinda yake fada mana ba.”
19 Jesus knew that they wanted to ask him about this, so he said to them, “Are you asking one another what I meant when I said, ‘In a little while, you will not see me; and again after a little while, you will see me’?
Yesu kuwa ya ga suna so su tambaye shi, sai ya ce masu, “Wato kuna tambayar juna ne abinda nake nufi da cewa, “Bayan dan lokaci kadan ba zaku gan ni ba, bayan dan lokaci kadan kuma zaku gan ni'?
20 Truly, truly, I say to you, you will weep and lament, but the world will rejoice. You will be sorrowful, but your sorrow will turn to joy.
Hakika, hakika, ina gaya maku, zaku yi kuka da makoki, amma duniya za ta yi farin ciki, zaku cika da bakin ciki, amma bakin cikinku zai koma farin ciki.
21 When a woman is giving birth, she has pain because her hour has come. But when her baby is born, she no longer remembers the anguish because of her joy that a child has been born into the world.
Mace takan ji zafi lokacin da take nakuda don lokacin haihuwa ya zo. Amma da zarar ta haifi jinjirin nan, ba ta kara tunawa da zafin, domin ta na fariciki an haifi mutum a duniya.
22 So you also have sorrow now, but I will see you again, and your hearts will rejoice, and no one will take your joy away from you.
To yanzu dai kuna bakin ciki, amma zan sake ganinku, kuma ba wanda zai iya kwace maku wannan farin ciki.
23 In that day you will ask nothing of me. Truly, truly, I say to you, whatever you ask of the Father in my name he will give you.
A rannan, ba zaku tambaye ni komai ba. Hakika hakika, ina gaya maku, komai kuka roki Uba a cikin sunana zai ba ku shi.
24 Until now you have not asked for anything in my name. Ask, and you will receive, so that your joy may be full.
Harwa yau, ba ku roki komai cikin sunana ba. Ku roka, zaku karba, domin farin cikin ku ya zama cikakke.”
25 “I have told you these things in figures of speech, but an hour is coming when I will no longer use figures of speech but will tell you plainly about the Father.
“Na fada maku wadannan abubuwa cikin karin magana. Amma sa'a tana zuwa da ba zan kara fada maku komai ba cikin karin magana, amaimakon haka zan gaya maku komai a sarari game da Uba.
26 In that day you will ask in my name, and I do not say to you that I will ask the Father on your behalf,
A ranar nan, zaku yi roko a cikin sunana kuma bance maku zan yi addu'a ga Uba a madadinku ba,
27 for the Father himself loves you, because you have loved me and have come to believe that I came from God.
domin Uba da kansa yana kaunarku, domin kun kaunace ni, kun kuma gaskata daga wurin Uban na fito.
28 I came from the Father and have come into the world, and now I am leaving the world and going to the Father.”
Daga wurin Uban na fito, kuma na shigo duniya. Har wa yau, kuma zan bar duniya in koma wurin Uba.”
29 His disciples said to him, “Behold, now yoʋ are speaking plainly and not using any figure of speech.
Almajiransa sukace, duba, “Yanzu kake magana a sarari, ba cikin karin magana ba!
30 Now we know that yoʋ know all things and have no need for anyone to question yoʋ; because of this we believe that yoʋ came from God.”
Yanzu mun sani ka san komai, ba sai wani ya tambaye ka ba. Ta haka muka gaskata daga wurin Allah ka fito.”
31 Jesus answered them, “Now do you believe?
Yesu ya amsa masu yace, “Ashe, yanzu kun gaskata?
32 Behold, an hour is coming, and has now come, when you will be scattered, each to yoʋr own home, and will leave me all alone. Yet I am not alone, for the Father is with me.
Duba, sa'a na zuwa, I, sa'ar ta yi, da za a warwatsa ku, kowa ya koma gidansa, kuma ku bar ni ni kadai. Duk da haka kuwa ba ni kadai nake ba, domin Ubana yana tare da ni.
33 I have said these things to you so that in me you may have peace. In the world you will have tribulation, but take heart; I have overcome the world.”
Na fada maku wannan ne domin a ciki na ku sami salama. A duniya kuna shan tsanani, amma ku karfafa: na yi nasara da duniya,”