< John 15 >
1 “I am the true vine, and my Father is the vinedresser.
“Nine itacen inabi na hakika, Ubana kuwa shi ne manomin.
2 Every branch in me that does not bear fruit he takes away, and every branch that does bear fruit he prunes so that it will bear more fruit.
Yakan cire duk wani rashe a cikina da ba ya bada 'ya'ya, mai bada 'ya'ya kuwa ya kan gyara shi domin ya kara bada 'ya'ya.
3 You have already been pruned by the word I have spoken to you.
Kun rigaya kun tsarkaka saboda maganar da na yi muku.
4 Abide in me, and I will abide in you. As the branch cannot bear fruit by itself unless it abides in the vine, neither can you bear fruit unless you abide in me.
Ku zauna ciki na, Ni kuma cikin ku. Kamar yadda reshe ba ya iya bada 'ya'ya shi kadai sai ya zauna cikin itacen, haka kuma ba za ku iya ba, sai kun zauna ciki na.
5 I am the vine; you are the branches. Whoever abides in me, and I in him, bears much fruit, because apart from me you can do nothing.
Ni ne itacen inabi, ku ne rassan. Wanda ya zauna ciki na, ni kuma cikin sa, yana bada 'ya'ya dayawa, gama in ba tare da ni ba, ba za ku iya yin kome ba.
6 If anyone does not abide in me, he is thrown out like a branch and withers. Such branches are gathered up, thrown into the fire, and burned.
Wanda kuma bai zauna a ciki na ba, akan jefar da shi kamar reshe, ya bushe, kuma sukan tattara rassan su jefa a wuta, su kone.
7 If you abide in me and my words abide in you, you will ask for whatever you wish, and it will be done for you.
In kun zauna a ciki na, maganata kuma ta zauna a cikin ku, sai ku roki duk abinda kuke so, za a kuwa yi maku.
8 My Father is glorified when you bear much fruit, and by doing so you will be my disciples.
Ta haka ake daukaka Ubana: cewa ku bada 'ya'ya dayawa, kuma cewa ku almajiraina ne.
9 Just as the Father has loved me, so have I loved you; abide in my love.
Kamar yadda Ubana ya kaunace ni, haka Ni ma na kaunace ku; Ku zauna cikin kaunata.
10 If you keep my commandments, you will abide in my love, just as I have kept my Father's commandments and abide in his love.
Idan kun kiyaye dokokina, za ku zauna cikin kaunata kamar yadda Na kiyaye dokokin Ubana, na kuma zauna cikin kaunarsa.
11 I have told you these things so that my joy may abide in you, and so that your joy may be full.
Ina gaya maku wadannan al'amura domin farincikina ya kasance a cikin ku, kuma domin farincikinku ya zama cikakke.
12 “This is my commandment, that you love one another, just as I have loved you.
“Wannan shine umarnina, cewa ku kaunaci juna kamar yadda na kaunace ku.
13 No one has greater love than this, that he lay down his life for his friends.
Babu wanda ke da kaunar da tafi haka, wato ya bada ransa domin abokansa.
14 You are my friends if you do whatever I command you.
Ku abokaina ne idan kuna yin abubuwan da na umarce ku.
15 No longer do I call you servants, because a servant does not know what his master is doing; but I have called you friends, because I have made known to you everything I heard from my Father.
Nan gaba ba zan kara ce da ku bayi ba, don bawa bai san abinda Ubangijinsa ke yi ba. Na kira ku abokaina, domin na sanar da ku duk abinda na ji daga wurin Ubana.
16 You did not choose me, but I chose you and appointed you that you should go and bear fruit, and that your fruit should abide, so that whatever you ask of the Father in my name he will give you.
Ba ku kuka zabe ni ba, amma Ni ne na zabe ku, na aike ku don ku je ku bada 'ya'ya, 'ya'yanku kuma su tabbata. Wannan ya zama domin duk abinda kuka roki Uba a cikin sunana, zai baku.
17 I am giving you these commands so that you may love one another.
Na baku wannan umarni: domin ku kaunaci juna.
18 “If the world hates you, know that it hated me before it hated you.
In duniya ta ki ku, ku sani cewa ta kini kafin ta ki ku.
19 If you were of the world, the world would love you as its own. However, because you are not of the world, but I have chosen you out of the world, the world hates you.
Da ku na duniya ne, da duniya ta kaunace ku kamar nata. Amma saboda ku ba na duniya bane, na kuma zabe ku daga duniya, don haka duniya take kin ku.
20 Remember what I told you: ‘A servant is not greater than his master.’ If they persecuted me, they will persecute you also. If they kept my word, they will keep yours also.
Ku tuna da maganar da na yi muku, 'Bawa ba ya fi Ubangijinsa girma ba.' Idan sun tsananta mani, ku ma za su tsananta maku; Idan sun kiyaye maganata, za su kuma kiyaye maganarku.
21 But they will do all these things to you on account of my name, because they do not know him who sent me.
Za su yi maku duk wadannan abubuwa saboda sunana, don basu san wanda ya aiko ni ba.
22 If I had not come and spoken to them, they would have no sin, but now they have no excuse for their sin.
Da ban zo na yi masu magana ba, da basu da zunubi, amma yanzu, basu da wata hujja don zunubinsu.
23 Whoever hates me hates my Father also.
Duk wanda ya ki ni ya ki Ubana.
24 If I had not done among them the works that no one else had done, they would have no sin, but now they have seen and hated both me and my Father.
Da ban yi ayyukan da babu wanda ya taba yinsu a cikin su ba, da basu da zunubi, amma yanzu sun gani, sun kuma ki ni da Ubana duka.
25 But this has happened to fulfill what is written in their law: ‘They hated me for no reason.’
An yi wannan kuwa domin a cika maganar da ke rubuce a cikin shari'arsu, ' Sun ki ni ba dalili.'
26 “When the Helper comes, whom I will send you from the Father, the Spirit of truth who proceeds from the Father, he will testify about me.
Sa'adda Mai Ta'aziya- wanda zan aiko maku daga wurin Uban, wato, Ruhun gaskiya, wanda ke fita daga wurin Uban-ya zo, zai bada shaida a kai na.
27 You must also testify, because you have been with me from the beginning.
Ku ma kuna bada shaida saboda kuna tare da ni tun daga farko.