< Acts 21 >
1 After we parted from them and set sail, we followed a straight course and came to Cos. The next day we reached Rhodes, and from there we went to Patara.
Da muka rabu da su, muka shiga jirgin ruwa muka mike hanya zuwa birnin Kos, washegari sai birnin Rodusa, daga nan sai kuma zuwa birnin Batara.
2 When we found a ship crossing over to Phoenicia, we went on board and set sail.
Da muka sami jirgi mai hayewa zuwa Fonisiya sai muka shiga.
3 After coming in sight of Cyprus, we passed it on the left, sailed to Syria, and arrived at Tyre, for there the ship was to unload its cargo.
Da muka hango tsibirin Kubrus muka bar shi a hagun mu muka nufi Suriya, muka sauka a birnin Taya domin a nan ne jirgin ruwan zai sauke kayansa.
4 Then we found some disciples and stayed there for seven days. Through the Spirit they kept telling Paul not to go up to Jerusalem,
Bayan mun sami almajirai sai muka zauna can kwana bakwai. Al'majiran suka ce ma Bulus, ta wurin Ruhu, kada ma ya je Urushalima.
5 but when our days there came to an end, we left and went on our way. All the disciples accompanied us, along with their wives and children, until we were outside of the city. Then we knelt down on the beach and prayed.
Bayan 'yan kwanaki muka cigaba da tafiyarmu. Dukansu da matansu da 'ya'yansu suka raka mu har bayan birnin. Sa'annan muka durkusa a bakin gacci muka yi addu'a muka yi sallama da juna.
6 After saying goodbye to one another, we got on board the ship, and they returned to their homes.
Sai muka shiga jirgin ruwa, su kuma suka koma gida.
7 When we completed the voyage from Tyre, we arrived at Ptolemais. After greeting the brothers, we stayed with them for one day.
Da muka gama tafiyarmu a Taya muka iso Talamayas. A nan ne muka gaisa da 'yan'uwa, muka zamna kwana daya da su.
8 The next day Paul and his companions left and went to Caesarea. We entered the house of Philip the evangelist, who was one of the seven, and stayed with him.
Washegari muka tashi muka tafi Kaisariya. Muka shiga gidan Filibus mai shaida bishara, daya daga cikin bakwai din, muka zauna da shi.
9 (He had four virgin daughters who prophesied.)
Wannan mutum yana da 'ya'ya hudu mata, budurwai masu yin annabci.
10 After we had been there for several days, a prophet named Agabus came down from Judea.
Sa'anda muka zauna can 'yan kwanaki, wani annabi ya zo daga Yahudiya mai suna Agabus.
11 He came to us and took Paul's belt, and binding his own feet and hands, he said, “Thus says the Holy Spirit, ‘In this way the Jews in Jerusalem will bind the man who owns this belt and deliver him into the hands of the Gentiles.’”
Ya zo wurinmu ya dauki damarar Bulus ya daure tasa kafar da hannayensa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki ya ce, 'Haka Yahudawa za su daure mai wannan damarar, zasu kuma bashe shi ga al'ummai.'”
12 When we heard this, we and the local residents urged Paul not to go up to Jerusalem.
Da muka ji wannan sakon, sai dukanmu da mazaunan wurin muka roki Bulus kada ya tafi Urushalima.
13 But Paul responded, “What are you doing, weeping and breaking my heart? For I am ready not only to be imprisoned, but even to die in Jerusalem for the name of the Lord Jesus.”
Sai Bulus ya amsa ya ce, “Me kuke yi, kuna kuka kuna karya mani zuciya? Bama a shirye don dauri kadai nake ba har ma da mutuwa a Urushalima, sabili da sunan Ubangiji Yesu.”
14 Since he would not be persuaded, we said, “The Lord's will be done,” and then we kept silent.
Tun da Bulus bashi da niyyar a rinjaye shi, muka daina kuka muka ce, “Bari nufin Ubangiji ya tabbata.”
15 After those days we packed up our belongings and went up to Jerusalem.
Bayan wadannan kwanaki, muka dauki jakkunanmu muka haura Urushalima.
16 Some of the disciples from Caesarea went with us, bringing us to a Cypriot man named Mnason, an early disciple, with whom we were to stay.
Wadansu almjirai daga Kaisariya suka bi mu. Sun zo ne tare da wani ana ce da shi Manason, mutumin Kuburus mai bi na farko, wanda za mu zauna da shi.
17 When we arrived in Jerusalem, the brothers warmly welcomed us.
Da muka isa Urushalima, 'yan'uwa suka marabce mu da farin ciki.
18 The following day Paul went in with us to James, and all the elders were present.
Washegari Bulus ya tafi tare da mu zuwa wurin Bitrus, dukan dattawa kuma suna nan.
19 After greeting them, he reported in detail what God had done among the Gentiles through his ministry.
Bayan ya gaishe su, sai ya shaida masu daya bayan daya abubuwan da Allah ya yi cikin al'ummai ta wurin hidimarsa.
20 When they heard this, they began glorifying the Lord. Then they said to him, “Yoʋ see, brother, how many thousands of Jews there are who have become believers, and they are all zealous for the law.
Da suka ji haka, suka yabi Ubangiji suka ce masa, “Ka gani, dan'uwa, dubban Yahudawa sun bada gaskiya suna kuma da niyyar kiyaye shari'a.
21 They have been informed that yoʋ teach all the Jews who live among the Gentiles to forsake Moses, telling them not to circumcise their children or walk according to our customs.
An kuma gaya masu a kanka cewa, kana koya wa Yahudawan da suke zaune cikin al'ummai su yi watsi da Musa. Kana koya masu kada su yi wa 'ya'yansu kaciya, kada kuma su bi tsofaffin al'adu.
22 What then is to be done? The assembly will surely meet, for they will hear that yoʋ have come.
Me ya kamata mu yi? Hakika za su ji ka zo.
23 So yoʋ must do what we tell yoʋ. There are four men who are under a vow.
Sabo da haka ka yi abin da muka fada maka yanzu. Muna da maza hudu da suka dauki wa'adi.
24 Take these men and purify yoʋrself along with them and pay their expenses, so that they may shave their heads. Then everyone will know that there is no truth to what they have been told about yoʋ, but that yoʋ yoʋrself also walk in an orderly manner, keeping the law.
Tafi da wadannan ka tsarkake kanka tare da su, ka dauki dukan dawainiyar su dana askin kai. Ta haka kowanne mutum zai sani abubuwan da ake fadi a kanka karya ne. Za su sani cewa kai mai kiyaye shari'a ne.
25 But as for the Gentiles who have become believers, we have written a letter with our judgment that they should observe no such thing, except that they should keep themselves from what has been sacrificed to idols, from blood, from what has been strangled, and from fornication.”
Game da al'umman da suka bada gaskiya mun yi masu wasika, mun bada umarni su kaurace kansu daga sadakokin da aka mika wa gumaku, da jini, da abin da aka makare da kuma fasikanci.
26 Then Paul took the men, and on the next day he purified himself with them and went to the temple, giving notice of when the days of their purification would be completed and the offering would be presented for each of them.
Sai Bulus ya dauki mazannan, washegari ya tsarkake kansa tare da su, suka shiga haikali, domin ya sanar da cikar ranakun tsarkakewarsu, wato ranar ba da sadaka domin kowanne dayansu.
27 When the seven days were about to be completed, the Jews from Asia saw Paul in the temple courts and began stirring up the entire crowd. They seized him,
Da kwanakin nan bakwai suka yi gab da cika, wadansu Yahudawa daga Asiya suka ga Bulus a haikali, sai suka zuga taro, suka danke shi.
28 crying out, “Men of Israel, help us! This is the man who teaches everyone everywhere against our people, our law, and this place. Furthermore, he has even brought Greeks into the inner courts of the temple and has defiled this holy place.”
Suna ta kururuwa, “Mutanen Isra'ila ku taimaka mana. Wannan shine mutumin da ke koya wa dukan mutane ko'ina abubuwa gaba da mutane, da shari'a da kuma wannan wurin. Banda haka ya kawo Helenawa cikin haikalin nan ya kazantar da wannan wuri tsatsarka.”
29 (For they had seen Trophimus the Ephesian in the city with Paul, and they assumed that Paul had brought him into the inner courts of the temple.)
Domin dama sun ga Tarofimas mutumin Afisa tare da Bulus cikin birni, suka yi zaton ya kawo shi cikin haikali.
30 Then the entire city was in an uproar, and the people rushed together. They seized Paul and dragged him out of the temple courts, and the gates were immediately shut.
Sai duk gari ya rude, mutane suka runtuma suka danke Bulus. Suka ja shi waje daga cikin haikalin, nan da nan aka rufe kofofin.
31 But as they were trying to kill him, a report went up to the commander of the Roman cohort that all Jerusalem was in an uproar.
Suna kokarin kashe shi kenan, sai labari ya kai wurin hafsan sojoji cewa Urushalima duk ta yamutse da tarzoma.
32 At once he took soldiers and centurions and ran down to them. When the mob saw the commander and the soldiers, they stopped beating Paul.
Nan take ya dauki mayaka da jarumawa, suka sheka da gudu wurin taron. Da mutane suka ga hafsan sojoji da rundunansa sai suka daina dukan Bulus.
33 Then the commander came up, took him into custody, and commanded him to be bound with two chains. He then asked who he was and what he had done.
Sai hafsan ya tafi ya danke Bulus ya sa aka daure shi da sarkoki biyu. Ya tambaya ko shi wanene da kuma laifinsa.
34 But some in the crowd were shouting one thing, and some were shouting another, and since the commander could not find out any reliable information because of the uproar, he ordered Paul to be taken away to the barracks.
Wadansu cikin taron suna ta kururuwa wadansu su ce wannan, wadansu su ce, wancan. Tunda hafsan bai fahimci abin da suke fadi ba, sabo da ihunsu, ya dokaci a shigar da Bulus farfajiyar sojoji.
35 When Paul reached the steps, he had to be carried by the soldiers because of the violence of the crowd.
Da suka kai matakala, sojoji suka dauki Bulus sabo da tsananin husatar taron jama'a.
36 For the mob of people was following behind, crying out, “Away with him.”
Domin taron suka biyo baya suna ihu suna cewa, “A kashe shi.”
37 As Paul was about to be brought into the barracks, he said to the commander, “Do I have permission to speak to yoʋ?” The commander said, “Yoʋ know how to speak Greek?
An kusa shigar da shi farfajiyan kenan sai Bulus ya ce wa babban hafsan, “Ko ka yarda inyi magana da kai?” Hafsan ya ce, “Ka iya Helenanci?
38 Then yoʋ are not the Egyptian who before these days incited a revolt and led four thousand men of the Assassins out into the wilderness?”
Ashe ba kai ne Bamasaren nan da kwanakin baya ka haddasa tawaye, ka dauki 'yan ta'adda dubu hudu ka kai su jeji ba?”
39 Paul said, “I am a Jewish man from Tarsus of Cilicia, a citizen of an important city. Now I beg yoʋ, let me speak to the people.”
Bulus ya ce, “Ni Ba'ibrane ne daga birnin Tarsus a Kilikiya. Ni dan kasar babban birni ne. Ka amince mani in yi magana da mutanen.”
40 When the commander gave him permission, Paul stood on the steps and motioned with his hand to the people. When there was a great hush, he addressed them in the Hebrew language,
Da hafsan ya bashi izni, Bulus ya mike a kan matakala ya daga hannayensa sama ya yi nuni su yi shuru. Da wuri ya yi tsit, Bulus ya yi masu magana da Ibraniyanci. Ya ce,