< Acts 18 >

1 After this, Paul departed from Athens and went to Corinth.
Bayan haka sai Bulus ya tafi Antakiya daga nan, ya wuce Korinti.
2 There he found a Jew named Aquila, of Pontus by birth, who had recently come from Italy along with his wife Priscilla, because Claudius had ordered all the Jews to leave Rome. Paul came to them,
A can ya sadu da wani Bayahude mai sunan Akila, dan kasar Buntus ne; bai dade da zuwa garin ba, daga Italiya ya zo da matarsa mai suna Balkisu, saboda Kalaudiyas ya ba da umarni dukan Yahudawa su bar Roma; sai Bulus ya je wurinsu.
3 and because he was of the same trade, he stayed with them and worked, for they were tentmakers by trade.
Bulus ya zauna a gidansu don sana'arsu daya ce, wato, masu aikin Tanti ne.
4 Every Sabbath he reasoned in the synagogue and tried to persuade both Jews and Greeks.
Saboda haka Bulus na zuwa majami'a, yana yin nazari tare da su a kowace Asabaci. Yana kokari ya rinjayi Yahudawa da Helinawa.
5 When Silas and Timothy came down from Macedonia, Paul was compelled by the Spirit and testified to the Jews that Jesus is the Christ.
Amma a lokacin da Sila da Timoti suka iso Makidoniya, Ruhu ya matsa Bulus ya shaida wa Yahudawa cewa Yesu Almasihu ne.
6 But when the Jews opposed him and reviled him, he shook out his garments and said to them, “Your blood be upon your own heads! I am innocent. From now on I will go to the Gentiles.”
Lokacin da Yahudawa suka tayar masa suna zarginsa. Bulus ya kakkabe rigansa a gabansu yana cewa, “Alhakin jininku yana kanku; daga yanzu zan koma wurin al'ummai.”
7 So he moved on from there and went to the house of a man named Justus, a worshiper of God, whose house was next door to the synagogue.
Da ya bar wurinsu, ya tafi gidan Taitus Yustus mai wa Allah sujada. Gidansa na kusa da majami'a.
8 Crispus, the ruler of the synagogue, believed in the Lord together with his whole household. And many of the Corinthians, when they heard, believed and were baptized.
Kiristus shine shugaban majami'a, sai shi da dukan iyalin gidansa sun ba da gaskiya ga Ubangiji. Korantiyawa da yawa suka ji jawabin Bulus suka ba da gaskiya, aka yi masu Baftisma.
9 One night the Lord said to Paul in a vision: “Do not be afraid, but speak and do not be silent.
Da dare Ubangiji ya ce wa Bulus a cikin wahayi, “Kada ka ji tsoro, amma ka yi magana kada kuma ka yi shuru.
10 For I am with yoʋ, and no one will attack yoʋ to do yoʋ harm, for I have many people in this city.”
Gama ina tare da kai, ba wanda zai cutar da kai, gama ina da mutane anan garin.”
11 So Paul stayed for a year and six months, teaching the word of God among them.
Bulus ya zauna a nan tsawon shekara daya da wata shida, yana koyar masu da maganar Allah.
12 But when Gallio was proconsul of Achaia, the Jews rose up with one accord against Paul and brought him before the judgment seat,
Amma da Galiyo ya samu zaman gwamnan Akaya, sai Yahudawa suka tayar wa Bulus har suka kai shi gaban dakalin shari'a.
13 saying, “This man is persuading people to worship God in a manner contrary to the law.”
Suna cewa, “Wannan mutumin yana kokarin rinjayar mutane su yi sujadar da ta saba wa dokarmu.”
14 But just as Paul was about to open his mouth to speak, Gallio said to the Jews, “If it were a matter of some crime or evil misdeed, O Jews, I would bear with you, as is reasonable.
Duk da haka kafin Bulus ya yi magana, Galiyo ya ce wa Yahudawa, “Ku Yahudawa in da karar ku ta wani babban laifi ce wanda ya aikata, da sai in hukunta.
15 But since it is a question about words, names, and your own law, see to it yourselves, for I do not want to be a judge of such things.”
Amma tun da ya ke akan al'amurar, kalmomi ne, da ta sunaye da dokokin ku, ku je ku sasanta al'amuran ku.”
16 So he drove them away from the judgment seat.
Galiyo ya kore su daga dakalin shari'a.
17 Then all the Greeks took Sosthenes, the ruler of the synagogue, and began beating him in front of the judgment seat. But none of these things were of any concern to Gallio.
Saboda haka sai suka kama Sastanisu, suka yi masa duka sosai a gaban dakalin shari'a. Amma Galiyo bai damu da yadda suka karasa ba.
18 After staying in Corinth for many more days, Paul took leave of the brothers and set sail for Syria, and Priscilla and Aquila were with him. (Now he had shaved his head in Cenchreae because he was under a vow.)
Bulus kuwa, bayan ya zauna tare da su na wasu kwanaki masu yawa, ya bar 'yan'uwan zuwa Suriya ta jirgin ruwa, tare da Balkisu da Akila. Kafin ya bar tashar jiragen ruwa da ke a Sankuriya, ya tafi saboda ya aske kansa, domin ya dauki alkawarin Banazare.
19 When he arrived at Ephesus, he left Priscilla and Aquila there, but he himself went into the synagogue and reasoned with the Jews.
Da suka iso Afisa, Bulus ya bar Balkisu da Akila anan. Shi kuwa ya shiga majami'ar Yahudawa yana nazari tare da su.
20 When they asked him to stay with them for a longer period of time, he declined.
Da suka roki Bulus ya zauna da su na tsawon lokaci, bai yarda ba.
21 However, as he took leave of them, he said, “I must by all means keep the coming feast in Jerusalem, but I will return to you again, God willing.” Then he set sail from Ephesus.
Ya kama hanyarsa ya bar su ya ce, “In Allah ya yardar mani zan dawo wurinku wata rana.” Sai ya shiga jirgin ruwa daga Afisa.
22 When he arrived at Caesarea, he went up and greeted the church, and then went down to Antioch.
Daga saukar su a Kaisariya, sai ya haura zuwa Urushalima ya gai da iklisiya daga nan ya tafi Antakiya.
23 After spending some time there, he departed and went from place to place throughout the region of Galatia and Phrygia, strengthening all the disciples.
Bayan ya zauna na dan lokaci a wurin, Bulus ya kama hanyarsa zuwa yakin Galatiya da Firjiya anan ya karfafa almajirai.
24 Meanwhile a Jew named Apollos, an Alexandrian by birth, arrived in Ephesus. He was an eloquent man, well-versed in the Scriptures.
A nan dai akwai wani Bayahude mai suna Afolos, dan asalin Iskandariya ne da haihuwa, ya zo Afisa. Shi masani ne a maganar Allah.
25 He had been instructed in the way of the Lord. Being fervent in spirit, he spoke and accurately taught the facts about the Lord, though he knew only about the baptism of John.
Afolos dai ya sami horo daga maganar Ubangiji. Shi mai kokari ne a ruhu, yana wa'azi da koyarwa daidai game da Yesu. Amma ya san da Baftismar Yahaya ne kadai.
26 He began to speak boldly in the synagogue, but when Aquila and Priscilla heard him, they took him aside and explained to him the way of God in greater detail.
Afolos ya fara wa'azinsa da gabagadi a cikin majami'a. Da Balkisu da Akila suka ji shi sai suka yi abokantaka da shi, suka kara bayyana masa game da labarin hanyar Allah mafi daidai.
27 And when Apollos wanted to cross over to Achaia, the brothers wrote to the disciples, encouraging them to receive him. When he arrived, he was a great help to those who had become believers through grace,
Da ya so ya wuce zuwa cikin Akaya 'yan'uwa suka karfafa shi, sun rubuta wa almajiran da ke a Akaya, don su karbe shi da hannu biyu. Da ya iso wurinsu, ya kuwa karfafa 'yan'uwa da sun ba da gaskiya ta wurin alheri.
28 for he powerfully refuted the Jews in public, showing by the Scriptures that Jesus is the Christ.
Afolos ya ba Yahudawa mamaki da irin ikon da yake da shi da gwanintarsa, yadda yake nunawa daga nassoshi cewa Yesu shine Almasihu.

< Acts 18 >