< Acts 14 >

1 At Iconium Paul and Barnabas went together into the synagogue of the Jews and spoke in such a way that a great multitude of both Jews and Greeks believed.
A lokacin da Bulus da Barnaba sun shiga garin Ikoniya suka shiga majami'an Yahudawa suka yi wa'azi yadda har mutane da yawa daga cikin Yahudawa da Hellinawa suka ba da gaskiya.
2 But the Jews who refused to believe stirred up and corrupted the minds of the Gentiles to be against the brothers.
Amma Yahudawa da basu yi biyayya ba, suka zuga al'umman har suka yi fushi da 'yan'uwan.
3 So Paul and Barnabas spent a long time there, speaking boldly for the Lord, who was testifying to the message of his grace by granting signs and wonders to be done by their hands.
Suka zauna a wurin na tsawon lokaci, suna yni maganarsu gabagadi da ikon Ubangiji, yana kuma shaidar sakon alherinsa. Ya yi wannan ta wurin alamu da al'ajibai ta hannun Bulus da Barnaba.
4 But the population of the city was divided; some were with the Jews, and some were with the apostles.
Saboda haka mutanen garin sun rabu: wadansun su suka bi ra'ayin Yahudawa, wasu kuwa sun bi manzannin.
5 And when an attempt was made by both the Gentiles and the Jews, together with their rulers, to mistreat them and stone them,
Al'umman garin da Yahudawa sun nemi jan hankali shugabanninsu, don su wulakanta Bulus da Barnaba, su jajjefe su,
6 Paul and Barnabas became aware of it and fled for refuge to the Lycaonian cities of Lystra and Derbe and to the surrounding region.
da suka gane haka suka gudu zuwa biranen Likoniya, Listira da Darbe, da garuruwa wadanda ke kewaye da su,
7 There they continued to preach the gospel.
a can suka yi wa'azin bishara.
8 Now there was a man sitting in Lystra who could not use his feet. He had been lame from his mother's womb and had never walked.
A Listira akwai wani wanda ke zaune bai taba tashi da kafafunsa ba, don shi gurgu ne tun daga haihuwa.
9 This man listened to Paul as he was speaking. Paul looked at him intently, and when he saw that he had faith to be healed,
Wannan mutumin ya ji Bulus yana magana. Bulus ya kafa masa ido, ya gane mutumin na da bangaskiya da za a warkar da shi. Sai ya ce masa da murya mai karfi, “Tashi ka tsaya akan kafafunka”
10 he said with a loud voice, “Stand up on yoʋr feet!” So the man leaped up and began to walk.
Sai mutumin ya yi tsalle ya fara tafiya da kafafunsa, yana yawo.
11 When the crowds saw what Paul had done, they lifted up their voices, saying in Lycaonian, “The gods have come down to us in the likeness of men.”
Da jama'an garin sun ga abin da Bulus ya yi, suka tada muryarsu suna cewa da Likoniyanci, “Ai alloli sun ziyarce mu daga sama, da kamanin mutane.”
12 Barnabas they called Zeus, and Paul they called Hermes, since he was the one who took the lead in speaking.
Suna kiran Barnaba da sunan “Zafsa,” Bulus kuwa suka kira shi da sunan “Hamisa” domin shine yafi yin magana.
13 Then the priest of the shrine of Zeus that was located in front of their city brought bulls and garlands to the city gates, intending to offer sacrifices together with the crowds.
Sai firist din zafsa wanda dakin yin masa sujada na kofar birni; ya kawo bijimai biyu da furannin da aka saka su kamar gammo; shi da jama'arsa suna so su yi masa hadaya.
14 But when the apostles Barnabas and Paul heard about it, they tore their clothes and rushed into the crowd, crying out,
Amma da manzannin, wato Barnaba da Bulus, su ka ji labarin, suka yage rigunansu, suka hanzarta zuwa gun taron mutanen.
15 “Men, why are you doing these things? We also are men with the same nature as you. We are bringing you good news, telling you to turn from these worthless things to the living God, who made the heavens, the earth, the sea, and all that is in them.
Suna ta cewa, “Kuji! Ku mutane don me kuke wannan abin? Mu fa mutane ne kamarku. Mun kawo maku labari mai dadi ne, da cewa, ku rabu da abubuwa marar amfani, ku koma ga Allah mai rai, wanda ya hallici sama da kasa da teku da dukan abubuwa da ke cikinsu.
16 In past generations he allowed all the nations to go their own way,
A da dai ya bar mutane su yi abinda suka ga dama.
17 although he did not leave himself without a witness in that he did good by giving you rain from heaven and fruitful seasons, filling our hearts with food and gladness.”
Duk da haka, bai bar kansa ba tare da shaida ba, don yana bada abubuwa masu kyau, yana ba ku ruwan sama, lokatai masu albarka, ya cika ranku da abinci da farin ciki.”
18 Yet even by saying these things, they barely restrained the crowds from offering sacrifices to them.
Duk da wadannan kalmomin da kyar, Bulus da Barnaba suka iya tsayar da su daga yi masu hadaya.
19 Then some Jews came from Antioch and Iconium and persuaded the crowds. They stoned Paul and dragged him out of the city, supposing that he was dead.
Amma wasu Yahudawa daga Antakiya da wasunsu daga Ikoniya suka rinjayi tarun jama'ar. Suka jajjefi Bulus suka ja shi zuwa wajen garin, suna ganin kamar ya mutu.
20 But when the disciples gathered around him, he rose and entered the city. The next day he went on with Barnabas to Derbe.
Duk da haka da almajirai suka kewaye shi a tsaitsaye, sai ya tashi ya koma cikin garin. Washegari, ya tafi Darba tare Barnaba.
21 After preaching the gospel in that city and making many disciples, Paul and Barnabas returned to Lystra, Iconium, and Antioch,
Bayan sun yi wa'azin bishara a wannan birnin suka kuma sami almajirai da yawa, suka dawo Listira, da Ikoniya da Antikiya.
22 strengthening the souls of the disciples, exhorting them to continue in the faith, and telling them that through many tribulations we must enter the kingdom of God.
Suna karfafa zuciyar almajiran su rike bangaskiyarsu, su ci gaba da ita, suna ce masu, “Ta wurin jimrewa mai yawa zamu shiga mulkin Allah, don haka dole ne mu sha wahala.”
23 And when they had appointed elders for them in every church, with prayer and fasting they entrusted them to the Lord in whom they had come to believe.
Da suka zabar masu dattawa a kowace iklisiya, sai suka yi addu'oi da azumi, suka mika su ga Ubangiji, ga wanda suka gaskanta a gareshi.
24 After passing through Pisidia, they came to Pamphylia,
Sa'annan sun bi ta Bisidiya suka kai Bamfiliya.
25 and when they had spoken the word in Perga, they went down to Attalia.
Da suka yi maganarsu a Biriya, sun wuce zuwa har Italiya.
26 From there they sailed to Antioch, where they had been committed to the grace of God for the work they had now completed.
Ta jirgin ruwa zuwa Antakiya, a nan ne aka mika su ga alherin Allah don aikin da suka gama a yanzu.
27 After they arrived and gathered the church together, they reported all that God had done through them, and how he had opened a door of faith to the Gentiles.
Da isowarsu Antakiya sun tara 'yan iklisiya a wuri daya, sun ba da labarin dukan abin da Allah ya yi ta wurinsu. Da yadda Ya bude kofa a wurin al'ummai ta bangaskiya.
28 And they stayed there with the disciples for some time.
Sun zauna tare da almajiran na tsawon lokaci.

< Acts 14 >