< Matthew 21 >

1 And as he approached Jerusalem, and came to Bethphage, by the side of the mount of Olives, Jesus sent two of his disciples;
Yayinda Yesu da almajiransa suka kusato Urushalima sai suka zo Betafaji wajen dutsen zaitun, sai Yesu ya aiki almajiransa guda biyu,
2 and said to them: Go into this village which is over against you, and directly ye will find an ass tied, and a colt with her. Untie and bring them to me.
yace masu, “Ku shiga kauyen da yake gaban ku zaku iske wata jaka da aholaki tara da ita. Ku kwance su ku kawo mani su.
3 And if any man say ought to you, tell him, That they are needed by our Lord: and at once he will send them hither.
Idan wani ya gaya maku wani abu game da haka, sai ku ce, 'Ubangiji ne yake bukatarsu,' mutumin kuwa zai aiko ku da su nan da nan.”
4 Now this whole occurrence was, that so might be fulfilled that which was spoken by the prophet, saying:
Anyi wannan kuwa domin a cika annabcin anabin. Yace,
5 Tell ye the daughter of Sion, Behold, thy king cometh to thee, meek, and riding on an ass, and on a colt the foal of an ass.
“Ku cewa diyar Sihiyona, duba, ga sarkinki na zuwa wurin ki, mai tawali'u ne, kuma akan jaki wanda aholaki ne.”
6 And the disciples went, and did as Jesus commanded them.
Sai almajiran suka tafi suka yi kamar yadda Yesu ya umarce su.
7 And they brought the ass and the colt. And they placed their garments on the colt, and set Jesus upon it.
Suka kawo jakar da dan aholakin, suka sa tufafinsu akai, Yesu kuwa ya zauna akan tufafin.
8 And a very great throng strewed their clothes in the path; and others cut branches from the trees, and cast them in the path.
Yawancin jama'a kuwa suka baza tufafinsu akan hanya, wasu kuma suka yanko ganye daga bishiyoyi suka shimfida su a hanya.
9 And the multitudes that went before him, and that followed after him, shouted and said: Hosanna to the son of David: Blessed is he that cometh in the name of the Lord: Hosanna in the highest.
Taron jama'a da suke gabansa da wadanda suke bayansa, suka ta da murya suna cewa, “Hossana ga dan Dauda! mai albarka ne shi wanda ke zuwa cikin sunan Ubangiji. Hossana ga Ubangiji!”
10 And as he entered Jerusalem, the whole city was in commotion; and they said, Who is this?
Sa'adda Yesu ya shiga Urushalima sai doki ya cika birnin ana cewa, “Wanene wannan?”
11 And the multitudes said, This is Jesus the prophet, who is from Nazareth of Galilee.
Sai jama'a suka amsa, “Wannan shine Yesu annabi, daga Nazaret ta Galili.”
12 And Jesus entered into the temple of God, and expelled all them that bought and sold in the temple, and overset the counters of the money-brokers, and the seats of them that sold doves.
Sai Yesu ya shiga haikalin. Ya kori duk wadanda ke saye da sayarwa a cikin ikiilisiya. Ya birkice teburan masu canjin kudi da kujerun masu sayar da tantabaru.
13 And he said to them: It is written, my house shall be called the house of prayer; but ye have made it a den of robbers.
Ya ce masu, “A rubuce yake, 'Za a kira gidana gidan addu'a,' amma kun mayar dashi kogon 'yan fashi.”
14 And there came to him in the temple the blind and the lame; and he healed them.
Sai makafi da guragu suka zo wurin sa a haikalin, ya warkar da su.
15 And when the chief priests and Pharisees saw the wonderful things which he performed, and the children shouting in the temple and saying, Hosanna to the son of David, their indignation was excited.
Amma da manyan firistoci da malaman attaura suka ga abubuwan banmamaki da yayi, kuma sa'adda suka ji yara suna tada murya a cikin haikalin suna cewa, “Hossana ga dan Dauda,” sai suka ji haushi.
16 And they said to him: Hearest thou what these are saying? Jesus said to them: Yes. Have ye never read, Out of the mouth of children and infants
Suka ce masa, kana jin abinda wadannan mutanen ke fadi?'' Yesu ya ce masu, “I! Amma ba ku taba karantawa ba, 'daga bakin jarirai da masu shan mama ka sa yabo'?”
17 thou hast acquired praise? And he left them, and retired out of the city to Bethany, and lodged there.
Sai Yesu ya bar su, ya fice daga birnin zuwa Betaniya ya kwana a wurin.
18 And in the morning, when he returned to the city, he was hungry.
Washegari da safe yayin da yake komawa birnin, sai yaji yunwa.
19 And he saw a fig-tree by the way, and came to it and found nothing on it, except leaves only. And he said to it: There shall no more be fruit on thee for ever. And immediately the fig-tree withered. (aiōn g165)
Da ya ga bishiyar baure a bakin hanya, sai yaje wurin amma bai sami kome ba sai dai ganye. Sai ya ce mata, “Kada ki kara yin 'ya'ya har abada.” Sai nan take bishiyar bauren ta bushe. (aiōn g165)
20 And the disciples saw it, and admired, and said: How suddenly hath the fig-tree withered!
Da almajiran suka ga haka, sai suka yi mamaki suka ce, “Kaka bishiyar bauren ta bushe nan da nan?”
21 Jesus replied and said to them: Verily I say to you, That if there be faith in you, and ye shall not doubt, ye may not only do this thing of the fig-tree, but also if ye shall say to this mountain, be thou lifted up, and fall into the sea, it will be so.
Yesu ya amsa yace masu, “Hakika ina ce maku, in dai kuna da bangaskiya ba ku yi shakka ba, ba abinda aka yi wa bauren nan kadai za kuyi ba har ma za ku cewa tsaunin nan, “Ka ciru ka fada teku,' sai kuwa haka ta kasance.
22 And whatsoever ye shall ask in prayer, and shall believe, ye shall receive.
Kome kuka roka cikin addu'a, in dai kun gaskanta, za ku samu.”
23 And when Jesus came to the temple, the chief priests and the Elders of the people came to him as he was teaching, and said to him: By what authority doest thou these things? And who gave thee this authority?
Sa'adda Yesu ya shiga haikalin, sai manyan fristocin da shugabannin jama'a suka zo suka same shi yayin da yake koyarwa, suka ce, “Da wane iko kake yin wadannan abubuwa?”
24 Jesus replied and said to them: I also will ask you one question, and if ye will tell me, I also will tell you by what authority I do these things.
Yesu ya amsa yace masu, “Ni ma zan yi maku tambaya daya. In kun fada mani, ni ma zan fada maku ko da wane iko nake yin wadannan abubuwa.
25 The baptism of John, from whence was it? From heaven, or from men? And they reasoned among themselves, and said: If we should say, From heaven; he will say to us, Why did ye not believe in him?
Daga ina baftismar Yahaya ta fito, daga sama ko kuma daga mutune?” Sai suka yi shawara a tsakanin su, suka ce, “In munce, 'daga sama,' zai ce mana, 'don me bamu gaskanta dashi ba?'
26 And if we should say, From men; we are afraid of the multitude, for they all hold John as a prophet.
Amma in munce, ' daga mutune,' muna tsoron jama'a, saboda sun san Yahaya annabi ne.”
27 And they answered, and said to him: We do not know. Jesus said to them: Neither do I tell you by what authority I do these things.
Sai suka amsa ma Yesu suka ce, ''Bamu sani ba.” Shi ma yace masu, “Nima bazan gaya maku ko da wane iko nake yin abubuwan nan ba.
28 But how appeareth it to you? A certain man had two sons; and he came to the first and said to him, My son, go, labor to-day in the vineyard.
Amma me kuke tunani? Wani mutum yana da 'ya'ya biyu. Ya je wurin na farkon yace, 'Da, je ka kayi aiki yau a cikin gona.'
29 And he answered and said, I am not willing. But afterwards he repented and went.
Yaron ya amsa yace, 'bazan yi ba,' amma daga baya ya canza tunaninsa ya tafi.
30 And he came to the other, and said the same to him. And he answered and said: I go, my lord, but did not go.
Sai mutumin ya je wurin da na biyun ya fada masa abu guda. Wannan dan ya amsa ya ce, 'zanje, baba,' amma bai je ba.
31 Which of these two performed the pleasure of his father? They say to him, The first. Jesus said to them: Verily I say to you That publicans and harlots go before you into the kingdom of God.
Wanene a cikin 'ya'ya biyun nan yayi nufin ubansa?” Suka ce, “na farkon.” Yesu ya ce masu, “Hakika ina gaya maku, masu karbar haraji da karuwai za su shiga mulkin Allah kafin ku.
32 For John came to you in the way of righteousness, and ye believed him not; but the publicans and harlots believed him: and ye, after ye had seen it, did not even then repent and believe in him.
Gama Yahaya ya zo maku a hanyar adalci, amma ba ku gaskata da shi ba, a yayinda masu karbar haraji da karuwai suka gaskata da shi. Ku kuwa, bayan kun ga abin da ya faru, baku ma tuba daga baya ba don ku gaskata da shi.
33 Hear ye another similitude. A certain man, the lord of a house, planted a vineyard, and inclosed it with a hedge, and digged in it a wine-press, and built a tower in it, and leased it to cultivators, and removed to a distance.
Ku saurari wani misalin. Anyi wani mutum, mai gona. Yayi shuka a gonar, ya shinge ta, ya gina ramin matse inabi a cikin gonar, ya kuma gina wata hasumiyar tsaro, sai ya bada hayar gonar ga wadansu manoma. Sai ya tafi wata kasa.
34 And when the time for the fruits arrived, he sent his servants to the cultivators that they might remit to him of the fruits of the vineyard.
Da kakar inabi ta yi, sai ya aiki wadansu bayi su karbo masa amfanin gonar.
35 And the cultivators laid hold of his servants, and beat one, and stoned another and one they slew.
Amma manoman suka kama bayin, suka doddoki dayan, suka kashe dayan, suka jejjefe dayan da duwatsu.
36 And again he sent other servants, more numerous than the first; and they did the like to them.
Sai mai gonar ya sake aika wadansu bayinsa da suka fi na farko, amma manoman suka yi masu kamar yadda suka yi wa sauran.
37 And at last he sent to them his son: for he said, Perhaps they will respect my son.
Bayan wannnan, sai mai gonar ya aika da dansa wurin su yana cewa, 'za su yi wa dana biyayya.'
38 But the cultivators, when they saw the son, said among themselves: This is the heir: Come; let us kill him, and retain his inheritance.
Amma da manoman suka ga dan, sai suka ce a tsakanin su, 'wannan shine magajin. Kuzo, mu kashe shi mu gaji gonar.'
39 And they laid hold of him, thrust him out of the vineyard, and slew him.
Sai suka dauke shi, suka jefar da shi daga cikin gonar, suka kashe shi.
40 When the lord of the vineyard, therefore, shall come; what will he do to those cultivators?
To idan me gonar ya zo, me zai yiwa manoman?
41 They say to him: He will utterly destroy them; and will lease the vineyard to other cultivators, who will render him the fruits in their seasons.
Suka ce masa, “Zai hallaka mugayen manoman nan ta hanya mai tsanani, zai kuma bada gonar haya ga wadansu manoman, mutanen da za su biya, lokacin da inabin ya nuna.”
42 Jesus said to them: Have ye never read in the scripture, The stone which the builders rejected, hath become the head of the corner: this is from the Lord; and it is marvellous in our eyes?
Yesu yace masu, “Baku taba karantawa a nassi ba,'' 'Dutsen da magina suka ki ya zama dutse mafi amfani. Wannan daga Ubangijine, kuma abin mamaki ne a idanunmu?'
43 Therefore I say to you, That the kingdom of God shall be taken from you, and shall be given to a people that will yield fruits.
Saboda haka ina gaya maku, za a karbe mulkin Allah daga wurin ku a ba wata al'umma da zata bada amfaninsa.
44 And whoever shall fall upon this stone, will be fractured; but on whomsoever it shall fall, it will crush him to atoms?
Duk wanda ya fadi akan dutsen nan zai ragargaje. Amma duk wanda dutsen ya fadawa, zai nike.”
45 And when the chief priests and Pharisees had heard his similitudes, they understood that he spoke in reference to them.
Da manyan firistocin da farisawan suka ji wannan misalin, sai suka gane da su yake.
46 And they sought to apprehend him, but were afraid of the multitude, because they accounted him as a prophet.
Da suka nemi kama shi, sai suka ji tsoron taron, saboda mutanen sun dauke shi annabi.

< Matthew 21 >