< Matthew 19 >

1 And when Jesus had ended these discourses, he removed from Galilee, and came to the confines of Judaea on the other side of Jordan.
Sai ya zama sa'adda Yesu ya gama wadannan maganganu, sai ya bar Galili ya zo kan iyakokin Yahudiya, ketaren kogin Urdun.
2 And great multitudes followed after him, and he healed them there.
Taro mai yawa suka bi shi, ya kuma warkar da su a wurin.
3 And Pharisees came to him, and tempted him and said: Is it lawful for a man to divorce his wife for every cause?
Farisawa suka zo wurinsa, suna gwada shi, suka ce masa, ''Ya hallata bisa ga doka mutum ya saki matarsa don kowanne dalili?''
4 And he answered and said to them: Have ye not read, that he who made them at the beginning, made them a male and a female?
Yesu ya amsa ya ce, ''Baku karanta ba, cewa shi wanda ya yi su tun farko ya yi su miji da mace?
5 And he said: For this reason, a man shall leave his father and his mother, and adhere to his wife; and they two shall be one flesh.
Shi wanda ya yi su kuma ya ce, “Saboda wannan dalilin, mutum zai rabu da mahaifinsa da mahaifiyarsa ya hade da matarsa, su biyun su zama jiki daya?”
6 Wherefore they were not two, but one flesh. What therefore God hath united, let not man sunder.
Su ba biyu ba ne kuma, amma jiki daya. Don haka, duk abin da Allah ya hada, kada wani ya raba.''
7 They say to him: Why then did Moses command to give a bill of divorce, and to put her away?
Sai suka ce masa, ''To me yasa Musa ya umarcemu mu bada takardar saki, mu kuma kore ta?''
8 He said to them: Moses, on account of the hardness of your heart, permitted you to divorce your wives: but from the beginning it was not so.
Sai ya ce masu, ''Saboda taurin zuciyarku, shi yasa Musa ya yarda maku ku saki matanku, amma da farko ba haka yake ba.
9 And I say to you, That whoever leaveth his wife not being an adulteress, and taketh another, committeth adultery. And whoever taketh her that is divorced, committeth adultery.
Ina gaya maku, duk wanda ya saki matarsa in ba saboda zina ba, ya kuma auri wata, yana zina kenan. Wanda kuma ya auri macen da aka saka, yana aikata zina.''
10 His disciples say to him: If such is the case between man and wife, it is not expedient to take a wife.
Almajiran suka ce wa Yesu, ''Idan haka yake game da mutum da matarsa, ba kyau ayi aure ba.''
11 But he said to them: Not every one is capable of that thing, but he only to whom it is given.
Amma Yesu yace masu, ''Ba kowa ne zai karbi wannan koyarwa ba, amma sai wadanda an yardar masu su karbe ta.
12 For there are some eunuchs, born so from their mother's womb; and there are some eunuchs, who were made eunuchs by men; and there are some eunuchs who have made themselves eunuchs for the sake of the kingdom of heaven. He that can be contented let him be contented.
Akwai wadanda aka haife su babanni. Akwai wadanda mutane ne suka maida su babanni. Sa'annan akwai wadanda sun mayar da kansu babanni saboda mulkin sama. Duk wanda zai iya karbar wannan koyarwa, ya karba.''
13 Then they brought children to him, that he might lay his hand upon them and pray. And his disciples rebuked them.
Sai aka kawo masa yara kanana don ya dibiya hannuwansa akansu, yayi masu addu'a, amma almajiran suka kwabe su.
14 But Jesus said to them: Allow children to come to me, and forbid them not; for of those that are like them is the kingdom of heaven.
Amma Yesu ya ce masu, ''Ku bar yara kanana, kada ku hana su zuwa wuri na, domin mulkin sama na irinsu ne.''
15 And he laid his hand upon them, and departed from there.
Ya sa hannuwa akan su, sa'annan ya bar wurin.
16 And one came, drew near, and said to him: Good Teacher, what good thing must I do, that eternal life may be mine? (aiōnios g166)
Sai wani mutum ya zo wurin Yesu, ya ce, ''Malam, wanne ayyuka nagari ne zan yi domin in sami rai madawwami?'' (aiōnios g166)
17 And he said to him: Why callest thou me good? There is none good, except one, namely, God. But if thou wouldst enter into life, keep the commandments.
Yesu ya ce masa, ''Me yasa kake tambaya ta game da abin da ke nagari? Daya ne kawai ke nagari, amma idan kana so ka shiga cikin rai, ka kiyaye dokokin.''
18 He said to him, Which? And Jesus said to him: Thou shalt not kill; and thou shalt not commit adultery; and thou shalt not steal; and thou shalt not bear false testimony;
Mutumin ya ce masa, ''Wadanne dokokin?'' Yesu ya ce masa, ''Kada kayi kisa, kada kayi zina, kada kayi sata, kada kayi shaidar zur,
19 and honor thy father and thy mother; and thou shalt love thy neighbor as thyself.
ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, kuma ka kaunaci makwabcinka kamar kanka.''
20 The young man saith to him: All these have I kept from my childhood. What do I lack?
Saurayin nan ya ce masa, ''Ai na kiyaye duk wadannan. Me nake bukata kuma?''
21 Jesus saith to him: If thou desirest to be perfect, go, sell thy property, and give to the poor; and there shall be for thee a treasure in heaven; and come thou after me.
Yesu ya ce masa, ''Idan kana so ka zama cikakke, ka tafi ka sayar da mallakarka, ka kuma ba matalauta, zaka sami dukiya a sama. Sa'annan ka zo ka biyo ni.''
22 And the young man heard that speech, and he went away in sadness; for he had much property.
Amma da saurayin nan ya ji abin da Yesu ya fada, ya koma da bakin ciki, domin shi mai arziki ne kwarai.
23 And Jesus said to his disciples: Verily I say to you, it is difficult for a rich man to enter into the kingdom of heaven.
Yesu ya ce wa almajiransa, ''Hakika ina gaya maku, zai zama da wuya mai arziki ya shiga mulkin sama.
24 And again, I say to you: It is easier for a camel to enter the aperture of a needle, than for a rich man to enter the kingdom of God
Ina sake gaya maku, zai fi wa rakumi sauki ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.''
25 And when the disciples heard it, they wondered greatly, and said: Who then can attain to life!
Da almajiran sun ji haka, suka yi mamaki kwarai da gaske, suka ce, ''Wanene zai sami ceto?''
26 Jesus looked on them, and said to them: With men this is not practicable, but with God every thing is practicable.
Yesu ya dube su, ya ce, ''A wurin mutane wannan ba zai yiwu ba, amma a wurin Allah, kome mai yiwuwa ne.''
27 Then answered Cephas, and said to him: Lo, we have forsaken every thing, and come after thee: What therefore shall we receive?
Sai Bitrus ya amsa ya ce masa, ''Duba, mun bar kome da kome mun bi ka. To me za mu samu?''
28 Jesus said to them: Verily I say to you, that, as for you who have followed me, when the Son of man shall sit on the throne of his glory in the new world, ye also shall sit on twelve seats, and shall judge the twelve tribes of Israel.
Yesu ya ce masu, ''Hakika ina gaya maku, ku da kuka bi ni, a sabuwar haihuwa, lokacin da Dan Mutum ya zauna a kursiyin daukakarsa, ku ma zaku zauna a kursiyoyi goma sha biyu, kuna shari'anta kabilu goma sha biyu na Isra'ila.
29 And every man that relinquisheth houses, or brothers or sisters, or father or mother, or wife or children, or lands, for my name's sake, shall receive an hundredfold, and shall inherit eternal life. (aiōnios g166)
Duk wanda ya bar gidaje, 'yan'uwa maza, 'yan'uwa mata, mahaifi, mahaifiya, 'ya'ya, ko gonaki, saboda sunana, zai sami ninkin su dari, ya kuma gaji rai madawwami. (aiōnios g166)
30 But there are many first who shall be last, and last who shall be first.
Amma dayawa dake farko yanzu, za su zama na karshe, dayawa dake karshe kuma, su zama na farko.

< Matthew 19 >