< Luke 22 >

1 And the feast of unleavened cakes, which is called the passover, drew near.
Anan nan idin gurasa mara yisti ya yi kusa, wanda a ke kira Idin ketarewa.
2 And the chief priests and Scribes sought how they might kill him, for they were afraid of the people.
Manyan firistoci da marubuta suka yi shawara yadda za su kashe Yesu, gama suna jin tsoron mutane.
3 And Satan entered into Judas called Iscariot, who was of the number of the twelve.
Shaidan ya shiga Yahuza Iskariyoti, daya daga cikin goma sha biyun.
4 And he went and conferred with the chief priests and Scribes, and the military commanders of the temple, how he might betray him to them.
Yahuza ya je ya yi shawara da manyan firistoci da Jarumawa yadda zai ba da Yesu a garesu.
5 And they were glad, and covenanted to give him money.
Suka yi farin ciki, suka yarda su ba shi kudi.
6 And he promised them, and sought opportunity to betray him to them, in the absence of the multitude.
Sai ya yarda, sai ya nimi dama yadda zai ba da shi garesu a lokacin da babu taro.
7 And the day of unleavened cakes arrived, on which it was customary for the passover to be slain.
Ranar idin gurasa mara yisti ya yi, da dole za a yi hadayan rago na Idin ketarewa.
8 And Jesus sent Cephas and John, and said to them; Go, prepare for us the passover, that we may eat it.
Yesu ya aiki Bitrus da Yahaya, ya ce masu, “Ku je ku shirya mana abincin Idin ketarewa, domin mu ci.”
9 And they said to him: Where wilt thou, that we prepare?
Suka tambaye shi, “A ina ka ke so mu shirya?”
10 He said to them: Lo, when ye enter the city, there will a man meet you, bearing a vessel of water. Go after him;
Ya amsa masu, “Ku ji, sa'adda ku ka shiga birnin, wani mutum mai dauke da tulun ruwa zai same ku. Ku bishi zuwa cikin gidan da za ya shiga.
11 and where he entereth, say ye to the lord of the house: Our Rabbi saith, Is there a place of refreshment, in which I may eat the Passover, with my disciples?
Sai ku gaya wa mai gidan, 'Malam ya ce, “Ina dakin baki, inda zan ci abincin Idin ketarewa da almajirai na?'”
12 And lo, he will show you a large upper room that is furnished; there prepare ye.
Zai nuna maku babban bene wanda yake a shirye. Ku shirya a can.”
13 And they went, and found as he had said to them: and they made ready the passover.
Sai suka tafi, suka sami komai kamar yadda ya gaya masu. Sai suka shirya abincin Idin ketarewan.
14 And when the time arrived, Jesus came and reclined; and the twelve Legates with him.
Sa'adda lokacin ya yi, ya zauna da almajiran.
15 And he said to them: I have greatly desired to eat this passover with you, before I suffer.
Sai ya ce masu, “Ina da marmari matuka in ci wannan abincin Idin ketarewa da ku kamin in sha wahala.
16 For I say to you, That henceforth I shall not eat it, until it be fulfilled in the kingdom of God.
Gama na ce maku, ba zan ci shi kuma ba, sai dai an cika shi a mulkin Allah.”
17 And he took the cup, and gave thanks, and said: Take this, and divide it among you.
Sai Yesu ya dauki koko, sa'adda ya yi godiya, sai yace, “Karba wannan, ku rarraba a tsakaninku.
18 For I say to you, That I shall not drink of the product of the vine, until the kingdom of God shall come.
Gama ina ce maku, ba zan sha wannan ruwan inabi kuma ba, sai dai mulkin Allah ya zo.”
19 And he took bread, and gave thanks, and brake, and gave to them, and said: This is my body, which is given for your sakes. This do ye, in remembrance of me.
Sai ya dauki gurasa, sa'adda ya yi godiya, ya kakkarya shi, sai ya ba su, cewa, “Wannan jikina ne wanda aka bayar dominku. Ku yi wannan domin tunawa da ni.”
20 And in like manner also concerning the cup, after they had supped, he said: This cup is the new testament in my blood, which, for your sakes, is poured out!
Sai ya dauki kokon kuma bayan jibi, cewa, “Wannan koko sabon alkawari ne cikin jinina, wanda aka zubar dominku.
21 But, behold, the hand of him that betrayeth me is on the table.
Amma ku yi lura. Wanda zai bashe ni yana tare da ni a teburi.
22 And the Son of man goeth, as it was determined; but woe to that man, by whom he is betrayed.
Gama Dan Mutum zai tafi lallai kamar yadda aka kaddara. Amma kaiton wannan mutum da shine za ya bashe shi!”
23 And they began to inquire among themselves, which of them it was, that would do this.
Sai suka fara tambaya a tsakaninsu, wanene a cikinmu da zai yi wannan abu.
24 And there was contention also among them, who among them would be greatest.
Sai gardama ta tashi a tsakaninsu game da wanene mafi girma.
25 And Jesus said to them: The kings of the nations, are their lords; and those exercising authority over them, are called benefactors.
Ya ce masu, “Sarakunan al'ummai suna nuna iko akansu, kuma wadanda suke da iko a kansu ana ce da su masu mulki da daraja.
26 But ye, not so: but he that is great among you, must be as the least; and he that is chief, as the servitor.
Amma kada ya zama haka da ku. A maimakon haka, bari wanda ya ke mafi girma a cikinku ya zama mafi kankanta. Bari wanda yafi muhimmanci kuma ya zama kamar mai hidima.
27 For, which is the greater, he that reclineth, or he that serveth? Is not he that reclineth? But I am among you, as he that serveth.
Gama wanene yafi girma, wanda ya zauna a teburi, ko kuwa wanda yake yin hidima? Ba wanda ya zauna a teburi ba? Duk da haka ina kamar mai hidima a tsakaninku.
28 Ye are they who have continued with me in my trials:
Amma ku ne wadanda ku ke tare da ni a cikin jarabobina.
29 and I promise to you, as my Father hath promised to me, a kingdom:
Na baku mulki, kamar yadda Ubana ya ba ni mulki,
30 that ye may eat and drink at the table of my kingdom, and may sit on thrones, and judge the twelve tribes of Israel.
domin ku ci ku kuma sha a teburi na mulkina. Za ku zauna a kan kursiyai kuna shari'anta kabilun nan goma sha biyu na Israila.
31 And Jesus said to Simon: Simon, lo, Satan hath desired to sift thee, as wheat:
Siman, Siman, ka yi hankali, shaidan ya nemi izini a bada kai domin ya tankade ka kamar alkama.
32 but I have prayed for thee, that thy faith may not fail. And thou also, in time, turn; and confirm thy brethren.
Amma na yi maka addu'a, saboda kada bangaskiyarka ta fadi. Bayan da ka juyo kuma, ka karfafa 'yan'uwanka.”
33 And Simon said to him: My Lord, with thee I am ready, both for prison and for death.
Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ina shirye in tafi tare da kai zuwa cikin kurkuku da zuwa mutuwa.”
34 Jesus said to him: 1 tell thee, Simon, the cock will not crow this day, until thou hast three times denied that thou knowest me.
Yesu ya amsa masa, “Ina gaya maka, Bitrus, kamin caran zakara a yau, za ka yi musu na sau uku cewa ba ka sanni ba.”
35 And he said to them: When I sent you without purses, without wallets and shoes, lacked ye any thing? They say to him: Nothing.
Sa'annan Yesu ya ce masu, “Lokacin da na aike ku babu jaka, ko burgami ko takalma, ko kun rasa wani abu? Sai suka amsa, “Babu.”
36 He said to them: Henceforth, let him that hath a purse, take it; and so likewise a wallet. And let him that hath no sword, sell his garment, and buy himself a sword.
Ya kuma ce masu, “Amma yanzu, wanda ya ke da jaka, bari ya dauka, da kuma burgami. Wanda ba shi da takobi sai ya sayar da taguwarsa ya sayi guda.
37 For I say to you, That this also, which was written, must be fulfilled in me: I shall be numbered with transgressors. For, all that relates to me, will be fulfilled.
Gama ina ce maku, abin da aka rubuta game da ni dole sai ya cika, 'An lisafta shi kamar daya daga cikin masu karya doka.' Gama abinda aka fada akaina ya cika.”
38 And they said to him: Our Lord, lo, here are two swords. He said to them: They are sufficient.
Sai suka ce, “Ubangiji, duba! Ga takuba biyu.” Sai ya ce masu, “Ya isa.”
39 And he went out, and proceeded, as was his custom, to the mount of the place of Olives; and his disciples followed him.
Bayan cin abincin yamma, Yesu ya tafi, kamar yadda ya saba yi, zuwa dutsen Zaitun, sai almajiran suka bi shi.
40 And when he arrived at the place, he said to them: Pray ye, that ye enter not into temptation.
Sa'adda suka iso, ya ce masu, “Ku yi addu'a domin kada ku shiga cikin jaraba.”
41 And he retired from them, about a stone's throw; and kneeled down, and prayed,
Ya rabu da su misalin nisan jifa, sai ya durkusa kasa ya yi addu'a,
42 and said: Father, if it please thee, let this cup pass from me. Yet not my pleasure, but thine, be done.
yana cewa “Uba, in ka yarda, ka dauke wannan kokon daga gareni. Ko da yake ba nufina ba, amma bari naka nufin ya kasance.”
43 And there appeared to him an angel from heaven, who strengthened him.
Sai mala'ika daga sama ya bayyana a wurinsa, yana karfafa shi.
44 And as he was in fear, he prayed earnestly; and his sweat was like drops of blood; and it fell on the ground.
Yana cikin wahala sosai, sai ya dukufa cikin addu'a, har zufarsa kuma tana diga a kasa kamar gudajen jini.
45 And he arose from his prayer, and came to his disciples: and he found them sleeping, from sorrow.
Sa'adda ya tashi daga addu'arsa, sai ya zo wurin almajiran, ya same su suna barci domin bakin cikinsu,
46 And he said to them: Why sleep ye? Arise, and pray, lest ye enter into temptation.
sai ya tambaye su, “Don me kuke barci? Tashi ku yi addu'a, saboda kada ku shiga cikin jaraba.”
47 And while he was speaking, lo, a multitude, and he that was called Judas, one of the twelve, came at their head. And he came up to Jesus, and kissed him. For he had given them this sign: Whom I shall kiss, he it is.
Sa'adda yana cikin magana, sai, ga taron jama'a suka bayana, tare da Yahuza, daya daga cikin sha biyun, ya na jagabansu. Sai ya zo kusa da Yesu domin ya yi masa sumba,
48 Jesus said to him: Judas, is it with a kiss thou betrayest the Son of man?
amma Yesu ya ce masa, “Yahuza, za ka ba da Dan Mutum da sumba?”
49 And when they that were with him, saw what occurred, they said to him: Our Lord, shall we smite them with the sword?
Sa'adda wadanda suke kewaye da Yesu suka ga abin da yake faruwa, sai suka ce, “Ubangiji, mu yi sara da takobi ne?”
50 And one of them smote a servant of the high priest, and took off his right ear.
Sai daya daga cikinsu ya kai wa bawan babban firist sara a kunne, sai ya yanke masa kunnensa na dama.
51 And Jesus answered and said: Sufficient, thus far. And he touched the ear of him that was smitten, and healed him.
Yesu ya ce, “Ya isa haka.” Sai ya taba kunnensa, sai ya warkar da shi.
52 And Jesus said to those who had come upon him, the chief priests and Elders and military captains of the temple: Have ye come out against me, as against a robber, with swords, and with clubs, to take me?
Yesu yace wa manyan firistoci, da masu tsaron haikali, da dattawa wadanda suke gaba da shi, “Kun fito kamar za ku kama dan fashi, da takuba da sanduna?
53 I was with you daily in the temple, and ye laid not hands upon me. But this is your hour, and the reign of darkness.
Sa'adda nake tare da ku kowace rana a haikali, ba ku kama ni ba. Amma wannan shine lokacinku, da kuma ikon duhu.”
54 And they took him, and conducted him to the house of the high priest. And Simon followed after him, at a distance.
Suka kama shi, sai suka tafi da shi, suka kawo shi cikin gidan babban firist. Amma Bitrus yana binsa daga nesa.
55 And they kindled a fire in the middle of the court, and sat around it; and Simon also sat among them.
Bayan da suka hura wuta a tsakiyar gidan da suka zazzauna tare, Bitrus ya zaune a tsakaninsu.
56 And a certain maid saw him sitting at the fire, and she looked upon him, and said: This man also was with him.
Sai wata baranya ta ganshi ya zauna a hasken wuta, sai ta zura masa ido ta ce, “Wannan mutum ma yana tare da shi.”
57 But he denied, and said: Woman, I have not known him.
Amma Bitrus ya yi musu, yana cewa, “Mace, ban san shi ba.”
58 And a little after, another person saw him, and said to him: Thou too art one of them. And Cephas said: I am not.
Bayan dan karamin lokaci sai wani mutum ya gan shi, sai ya ce, “Kaima kana daya daga cikinsu.” Amma Bitrus ya ce, “Mutumin, ba ni ba ne.”
59 And an hour after, another contended and said: Certainly, this man also was with him, for he likewise is a Galilean.
Bayan sa'a daya sai wani mutum ya nace da cewa, “Gaskiya wannan mutum yana tare da shi, gama shi dan Galili ne.”
60 Cephas said: Man, I know not what thou sayest. And immediately, while he was speaking, the cock crew.
Amma Bitrus ya ce, “Mutumin, ban san abin da kake fada ba.” Sai nan da nan, da yana cikin magana, sai zakara ta yi cara.
61 And Jesus turned, and looked upon Cephas. And Simon remembered the word of our Lord, which he spoke to him: Before the cock shall crow, thou wilt deny me three times.
Yana juyawa, sai Ubangiji ya dubi Bitrus. Sai Bitrus ya tuna kalmar Ubangiji, sa'adda ya ce masa, “Kafin zakara ya yi cara yau za ka musunce ni sau uku.”
62 And Simon went out, and wept bitterly.
Da fitowarsa waje, Bitrus ya yi kuka mai zafi.
63 And the men who had taken Jesus, insulted him, and blinded him,
Sai mutanen da ke tsare da Yesu suka yi masa ba'a da bulala kuma.
64 and smote him on his face, and said: Prophesy thou, who smote thee?
Bayan da suka rufe masa idanu, suka tambaye shi, cewa, “Ka yi annabci! Wa ya buge ka?”
65 And many other things they revilingly uttered, and spoke against him.
Suka yi wadansu miyagun maganganu na sabo game da Yesu.
66 And when the day dawned, the Elders and chief priests and Scribes assembled together; and they led him to the place of their meeting,
Da gari ya waye, sai dattawa suka hadu tare, da manyan firistoci da marubuta. Sai suka kai shi cikin majalisa
67 and said to him: If thou art the Messiah, tell us. He said to them: If I tell you, ye will not believe in me.
suka ce, “Gaya mana, in kai ne Almasihu.” Amma yace masu, “Idan na gaya maku, ba za ku gaskanta ba,
68 And if I should ask you, ye will not return me an answer; nor will ye release me.
idan na yi maku tambaya, ba za ku amsa ba.
69 From this time, the Son of man will sit on the right hand of the majesty of God.
Amma nan gaba, Dan Mutum zai zauna a hannun dama na ikon Allah.”
70 And they all said: Thou art then, the Son of God? Jesus said to them: Ye say that I am.
Suka ce masa, “Ashe kai Dan Allah ne?” Sai Yesu ya ce masu, “Haka kuka ce, nine.”
71 They say: What further need have we of witnesses? For we have heard from his own mouth.
Suka ce, “Don me muke neman shaida? Gama mu da kanmu munji daga bakinsa.”

< Luke 22 >