< Jude 1 >
1 JUDE, a servant of Jesus the Messiah, and the brother of James, to the called people, the beloved of God the Father, the preserved by Jesus the Messiah:
Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub, Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.
2 Mercy and peace in love, be multiplied to you.
Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.
3 My beloved, while I take all pains to write to you of our common life, it is needful for me to write to you, exhorting you to maintain a conflict for the faith which was once delivered to the saints.
Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak.
4 For some have obtained entrance, who from the beginning were registered beforehand under this condemnation: wicked men, who pervert the grace of God to impurity, and deny him who is the only Lord God and our Lord, Jesus the Messiah.
Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.
5 And I wish to remind you, though ye all know it, that God, after once rescuing the people from Egypt, again destroyed them who believed not.
Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba.
6 And the angels that kept not their primacy, but left their station, he hath reserved in chains unknown, under darkness, unto the judgment of the great day. (aïdios )
Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. (aïdios )
7 As Sodom and Gomorrah, and the surrounding cities, which in like manner followed whoredom and went after strange flesh, are placed beneath everlasting fire, being, doomed to judgment. (aiōnios )
Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta. (aiōnios )
8 In the same manner, too, these sensual dreamers defile the flesh and despise authority, and revile excellency.
Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama.
9 But Michael the archangel, who, in debate with the Accuser, contended about the body of Moses, did not venture to bring against him a reviling declaration; but said, The Lord will rebuke thee.
Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!”
10 But these men revile things which they do not understand; and in the things of which they have a natural persuasion as animal beings, in these they corrupt themselves.
Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.
11 Woe to them; for they have gone in the way of Cain; and, after the error of Balaam, they have lusted for gain; and, in the rebellion of Korah, they have perished.
Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.
12 These are they who, in their feastings, riot while polluting themselves, feeding themselves without fear; clouds without rain, moved about by the winds; trees whose fruit hath failed, and they are without fruit, twice dead, and uplifted from their root;
Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus.
13 raging waves of the sea, which, by their foam, manifest their confusion; shootingstars, for which is reserved the blackness of darkness for ever. (aiōn )
Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada. (aiōn )
14 And of them also prophesied Enoch, who was the seventh from Adam, when he said: Behold, the Lord cometh, with myriads of his saints;
Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa
15 to execute judgment upon all; and to convict all the wicked, because of all the deeds they have wickedly committed; and because of all the hard speeches, which they, ungodly sinners, have uttered.
don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.”
16 These are they who murmur and complain of every thing, while they walk according to their lusts; and their mouth speaketh shocking things; and they flatter people, for the sake of gain.
Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.
17 But do ye, my beloved, remember the words which were before spoken by the legates of our Lord Jesus the Messiah;
Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā.
18 because they told you, that in the end of the times there would be scoffers, going after wickedness, according to their lusts.
Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.”
19 These are they that separate themselves, sensual persons, not having the Spirit.
Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.
20 But, my beloved, be ye built up anew, in your holy faith, through the Holy Spirit, while ye pray.
Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki.
21 And let us keep ourselves in the love of God, while we wait for the mercy of our Lord Jesus the Messiah unto our eternal life. (aiōnios )
Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami. (aiōnios )
22 And some of them, snatch ye from the fire.
Ku ji tausayin waɗanda suke shakka;
23 And when they repent, have compassion on them, with fear, hating even the tunic that is defiled by the flesh.
ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.
24 And to him who is able to preserve you faultless, and spotless, and to establish you without a blemish,
To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki.
25 before his majesty, with joy, namely, the only God, our Deliverer, by means of Jesus the Messiah our Lord, be praise, and dominion, and honor, and majesty, both now and in all ages. Amen. (aiōn )
Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin. (aiōn )