< Acts 1 >

1 THE former book have I written, O Theophilus concerning all the things which our Lord Jesus Messiah began to do and teach,
A littafina na farko, Tiyofilus, na rubuta game da dukan abin da Yesu ya fara yi, da abin da ya koyar
2 until the day when he was taken up, after he had instructed those legates whom he had chosen by the Holy Spirit.
har zuwa ranar da aka ɗauke shi zuwa sama, bayan ya ba da umarnai ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa.
3 To whom also he showed himself alive after he had suffered, by numerous signs, during forty days, while he was seen by them, and spoke of the kingdom of God.
Bayan wahalarsa, ya bayyana kansa ga waɗannan mutane ya kuma ba da tabbatattun alamu masu yawa cewa yana da rai. Ya bayyana a gare su har kwana arba’in ya kuma yi musu magana game da mulkin Allah.
4 And when he had eaten bread with them, he instructed them not to depart from Jerusalem, but to wait for the promise of the Father, which (said he) ye have heard from me.
A wani lokaci, yayinda yake ci tare da su, ya ba su wannan umarni, “Kada ku bar Urushalima, amma ku jira kyautar da Ubana ya yi alkawari, wadda kuka ji na yi magana a kai.
5 For John baptized with water; but ye will be baptized with the Holy Spirit after not many days.
Gama Yohanna ya yi baftisma daruwa, amma a cikin’yan kwanaki za a yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
6 And they, when assembled, asked him and said to him: Our Lord, wilt thou at this time restore the kingdom to Israel?
Saboda haka, sa’ad da suka taru, sai suka tambaye shi, “Ubangiji, a wannan lokaci za ka mayar da mulki ga Isra’ila?”
7 He said to them: It is not yours, to know the time or times which God hath placed in his own power.
Ya ce musu, “Ba naku ba ne ku san lokuta ko ranakun da Uban ya shirya cikin ikonsa.
8 But when the Holy Spirit shall come upon you, ye will receive energy, and will be witnesses for me in Jerusalem, and in all Judaea, and also among the Samaritans, and unto the ends of the earth.
Amma ku za ku karɓi iko sa’ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauka a kanku; za ku kuma zama shaiduna cikin Urushalima, da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, zuwa kuma iyakar duniya.”
9 And when he had said these things, while they beheld him, he was taken up, and a cloud received him, and he was hidden from their eyes.
Bayan ya faɗi wannan, sai aka ɗauke shi sama a idanunsu sai wani girgije ya rufe shi daga ganinsu.
10 And while they were looking toward heav, as he departed, two men were found standing near them, in white garments,
Suna zuba ido a bisa, zuwa cikin sararin sama yayinda yake tafiya, nan da nan, sai ga mutane biyu saye da fararen riguna tsaye kusa da su.
11 and saying to them: Ye Galilean men, why stand ye and look toward heaven? This Jesus, who is taken up from you to heaven, will so come, as ye have seen him ascend to heaven.
Sai suka ce, “Mutanen Galili, don me kuke tsaye a nan kuna duban sararin sama? Wannan Yesu, wanda aka ɗauke daga gare ku zuwa sama, zai komo daidai yadda kuka ga ya tafi sama.”
12 And afterwards they returned to Jerusalem from the mount called the place of Olives, which was near to Jerusalem, and distant from it about seven furlongs.
Sai suka koma Urushalima daga tudun da ake kira Dutsen Zaitun, tafiyar ranar Asabbaci guda daga birnin.
13 And when they had entered, they went to an upper chamber; where were Peter, and John, and James, and Andrew, and Philip, and Thomas, and Matthew, and Bartholomew, and James the son of Alpheus, and Simon Zelotes, and Judas the son of James.
Da suka iso, sai suka hau gidan sama, zuwa ɗakin da suke zama. Waɗanda suka kasance kuwa su ne, Bitrus, Yohanna, Yaƙub da Andarawus; Filibus da Toma; Bartolomeyu da Mattiyu; Yaƙub ɗan Alfayus da Siman Zilot, da kuma Yahuda ɗan Yaƙub.
14 All these unitedly persevered in prayer, with one soul, together with the women, and with Mary the mother of Jesus, and with his brothers.
Waɗannan duka suka duƙufa cikin addu’a, tare da waɗansu mata da Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma tare da’yan’uwansa.
15 And in those days stood up Simon Cephas in the midst of the disciples, (the persons there assembled being about one hundred and twenty, ) and said:
A waɗancan kwanakin Bitrus ya miƙe tsaye cikin’yan’uwa masu bi (taron da ya yi kusan mutum ɗari da ashirin)
16 Men, brethren, it was right that the scripture should be fulfilled, which the Holy Spirit spake, by the mouth of David, concerning Judas who was guide to them that apprehended Jesus.
ya ce, “’Yan’uwana, dole a cika Nassin nan da Ruhu Mai Tsarki ya yi magana tun da daɗewa ta bakin Dawuda game da Yahuda, wanda ya zama jagora ga waɗanda suka kama Yesu
17 For he was numbered with us, and had a part in this ministry.
dā shi ɗaya ne cikinmu, ya kuma yi hidima a cikin aikin nan.”
18 He purchased a field with the wages of sin; and he fell upon his face on the ground, and burst in the middle, and all his entrails were poured out.
(Da ladar da ya samu saboda muguntarsa Yahuda ya sayi wani fili; a can ya fāɗi da kā, jikinsa ya fashe, hanjinsa kuma duk suka zubo.
19 And this was known to all that dwelt at Jerusalem; so that the field was called, in the language of the country, Aceldama, which is interpreted Field of Blood.
Kowa a Urushalima ya ji game da wannan, saboda haka suka kira wannan filin Akeldama, da yarensu, wato, Filin Jini.)
20 For it is written, in the book of Psalms: Let his habitation be desolate, and let no resident be in it; and let another take his service.
Bitrus ya ce, “Gama yana a rubuce a cikin Littafin Zabura cewa, “‘Bari wurinsa yă zama babu kowa; kada kowa ya zauna a cikinsa,’ kuma, “‘Bari wani ya ɗauki matsayinsa na shugabanci.’
21 It should therefore be, that one of these persons, who have been with us all the time that our Lord Jesus went in and out with us,
Saboda haka dole a zaɓi ɗaya daga cikin mutanen da suke tare da mu duk lokacin da Ubangiji Yesu yake shiga da fita a cikinmu,
22 commencing from the baptism of John, unto the day he was taken up from us, should be, with us, a witness of his resurrection.
farawa daga baftisma ta Yohanna har zuwa sa’ad da aka ɗauke Yesu daga gare mu. Gama dole ɗaya daga waɗannan ya zama shaidar tashinsa daga matattu tare da mu.”
23 And they proposed two, Joseph called Barsabas, whose surname was Justus, and Matthias.
Saboda haka suka gabatar da mutane biyu. Yusuf mai suna Barsabbas (da aka kuma sani da Yustus) da kuma Mattiyas.
24 And when they had prayed, they said: Thou, Lord, knowest what is in the hearts of all, manifest which thou hast chosen of these two,
Sai suka yi addu’a suka ce, “Ubangiji, ka san zuciyar kowa. Nuna mana wanne a cikin waɗannan biyu da ka zaɓa
25 that he should take part in this ministry and legateship, from which Judas broke away, that he might go to his own place.
ya karɓi wannan aikin manzanci, wanda Yahuda ya bari don yă tafi wurin da yake nasa.”
26 And they cast lots, and it came upon Matthias; and he was numbered with the eleven legates.
Sa’an nan suka jefa ƙuri’u, ƙuri’ar kuwa ta fāɗo a kan Mattiyas; sai aka sa shi cikin manzannin nan goma sha ɗaya.

< Acts 1 >