< 1 Peter 4 >
1 If then the Messiah hath suffered for you in the flesh, do ye also arm yourselves with the same mind: for every one that is dead in his body, hath ceased from all sins,
Saboda haka, tunda yake Almasihu ya sha wuya a jiki, muma mu sha damara da wannan ra'ayi. Duk wanda ya sha wuya a jiki ya daina aikata zunubi.
2 that he may no longer be alive to the lusts of men, while he is in the body, but only to do the pleasure of God.
Wannan mutum kuma baya kara zaman biye wa muguwar sha'awar mutumtaka, amma sai dai nufin Allah dukkan sauran kwanakinsa a duniya.
3 For the time that is past was enough, when ye wrought the pleasure of the profane, in dissoluteness, and in ebriety, and in lasciviousness, and in revelling, and in the worship of demons.
Gama lokaci ya wuce da zamu yi abin da al'ummai suke son yi, wato fajirci, mugayen sha'awace-sha'awace, da buguwa da shashanci da shaye-shaye da bautar gumaku da abubuwan kyama.
4 And lo, they now wonder, and reproach you, because ye revel not with them in the same former dissoluteness;
Suna tunanin bakon abu ku ke yi da ba kwa hada kai tare da su yanzu a yin wadannan abubuwa, sai suna zarginku.
5 who must give account to God, who is to judge the living and the dead.
Za su bada lissafi ga wanda yake a shirye ya shari'anta masu rai da matattu.
6 For on this account the announcement is made also to the dead, that they may be judged as persons in the flesh, and may live according to God in the spirit.
Shi yasa aka yi wa matattu wa'azin bishara, cewa ko da shike anyi masu shari'a cikin jikunan mutane, su rayu bisa ga Allah a ruhu.
7 But the end of all things approacheth: therefore be sober, and be wakeful for prayer.
Karshen dukkan abubuwa yana gabatowa. Saboda haka, ku zama natsatsu, ku natsu cikin tunaninku domin yin addu'oi.
8 And above all things, have fervent love one towards another; for love covereth a multitude of sins.
Gaba da kome, ku himmatu wajen kaunar juna, domin kauna bata neman tona zunuban wadansu.
9 And be ye compassionate to strangers, without murmuring.
Ku yi wa juna bakunta da abubuwa nagari ba tare da gunaguni ba.
10 And let each of you minister to his associates the gift which he hath received from God; as being good stewards of the manifold grace of God.
Yadda kowanne dayanku ya sami baiwa, kuyi amfani da su domin ku kyautata wa juna, kamar masu rikon amanar bayebaye na Allah, wanda ya ba mu hannu sake.
11 Whoever will speak, let him speak as the word of God: and whoever will minister, as of the ability that God hath given him: so that in all ye do, God may be glorified, through Jesus the Messiah; to whom belongeth glory, and honor, for ever and ever. Amen. (aiōn )
Idan wani yana yin wa'azi, ya zamana fadar Allah ya ke fadi, idan wani yana hidima, ya yi da karfin da Allah ya ba shi, domin cikin dukkan abubuwa a daukaka Allah ta wurin Yesu Almasihu. Daukaka da iko nasa ne har abada abadin. Amin. (aiōn )
12 My beloved, be not dismayed at the trials that befall you, as if some strange thing had come upon you; for these things are for your probation.
Ya kaunatattu, kada ku zaci cewa matsananciyar wahalar da ta zo ta gwada ku bakon abu ne, ko kuma wani bakon abu ne yake faruwa a gareku.
13 But rejoice, that ye participate in the sufferings of the Messiah, that so ye may also rejoice and exult at the revelation of his glory.
Amma muddin kuna tarayya da Almasihu cikin wahalarsa, ku yi murna, domin kuyi farin ciki da murna sa'adda za a bayyana daukakarsa.
14 And if ye are reproached on account of the name of the Messiah, happy are ye: for the glorious Spirit of God resteth upon you.
Idan ana zargin ku sabili da sunan Almasihu, ku masu albarka ne, domin Ruhun daukaka da Ruhun Allah ya tabbata a kanku.
15 Only let none of you suffer, as a murderer, or as a thief, or as an evil-doer.
Amma kada kowannen ku ya sha wahala sabo da horon shi mai kisan kai ne, ko barawo, ko mamugunci, ko mai shisshigi.
16 But if he suffer as a Christian, let him not be ashamed; but let him glorify God on account of this name.
Amma in wani yana shan wahala sabili da shi na Almasihu ne, kada ya ji kunya, amma ya daukaka Allah a wannan sunan.
17 For it is the time when judgment will commence with the house of God: and if it commence with us, what will be the end of those who obey not the gospel of God?
Domin lokaci ya yi da shari'a za ta fara daga gidan iyalin Allah. Idan kuwa za a fara da mu, menene karshen wadanda suka ki biyayya da bisharar Allah?
18 And if the righteous scarcely liveth, where will the ungodly and the sinner be found!
Idan mutum, “mai adalci ya tsira da kyar, to, me zai faru da marar bin Allah da mai zunubi kuma?”
19 Wherefore, let them who suffer according to the pleasure of God, commend their souls to him in well doing, as to a faithful Creator.
Sabo da haka bari wadanda suke shan wuya bisa ga nufin Allah, su mika rayukansu ga amintaccen Mahalicci suna kuma yin ayyuka nagari.