< Ezekiel 36 >

1 and you(m. s.) son: child man to prophesy to(wards) mountain: mount Israel and to say mountain: mount Israel to hear: hear word LORD
“Ɗan mutum, ka yi annabci wa duwatsun Isra’ila ka ce, ‘Ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji.
2 thus to say Lord YHWH/God because to say [the] enemy upon you Aha! and high place forever: antiquity to/for possession to be to/for us
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa abokin gāba yana magana game da ku cewa, “Yauwa! Tsofaffin tuddai sun zama mallakarmu yanzu.”’
3 to/for so to prophesy and to say thus to say Lord YHWH/God because in/on/with because be desolate: destroyed and to crush [obj] you from around: side to/for to be you possession to/for remnant [the] nation and to ascend: rise upon lip: words tongue and slander people
Saboda haka ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin sun lalace ku suka kuma maishe ku kufai marar amfani a kowane gefe saboda ku zama mallakar sauran al’ummai da kuma abin magana da tsegumi ga mutane,
4 to/for so mountain: mount Israel to hear: hear word Lord YHWH/God thus to say Lord YHWH/God to/for mountain: mount and to/for hill to/for channel and to/for valley and to/for desolation [the] devastated and to/for city [the] to leave: forsake which to be to/for plunder and to/for derision to/for remnant [the] nation which from around
saboda haka, ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana faɗa wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, wa kufai da garuruwan da suka zama kango waɗanda aka washe aka wulaƙanta suka zama ganimar sauran al’ummai da suke kewaye da ku,
5 to/for so thus to say Lord YHWH/God if: surely yes not in/on/with fire jealousy my to speak: speak upon remnant [the] nation and upon Edom all her which to give: give [obj] land: country/planet my to/for them to/for possession in/on/with joy all heart in/on/with scorn soul: myself because pasture her to/for plunder
ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa cikin kishina mai ƙuna na yi magana gāba da sauran al’ummai, da kuma gāba da Edom, gama da farin ciki da reni a zukatansu suka mai da ƙasata mallakarsu don su washe wuraren kiwonta.’
6 to/for so to prophesy upon land: soil Israel and to say to/for mountain: mount and to/for hill to/for channel and to/for valley thus to say Lord YHWH/God look! I in/on/with jealousy my and in/on/with rage my to speak: speak because shame nation to lift: bear
Saboda haka ka yi annabci game da ƙasar Isra’ila ka kuma ce wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ga shi, na yi magana da kishina da hasalata saboda sun sha zargi wurin al’ummai.
7 to/for so thus to say Lord YHWH/God I to lift: vow [obj] hand: vow my if: surely yes not [the] nation which to/for you from around they(masc.) shame their to lift: vow
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa na ɗaga hannuna sama na rantse cewa al’ummai da suke kewaye da ku za su sha ba’a.
8 and you(m. p.) mountain: mount Israel branch your to give: give and fruit your to lift: bear to/for people my Israel for to present: come to/for to come (in): come
“‘Amma ku, ya duwatsun Isra’ila, za ku miƙa rassanku ku ba da amfani ga mutanena Isra’ila, gama ba da daɗewa ba za su komo gida.
9 for look! I to(wards) you and to turn to(wards) you and to serve: labour and to sow
Na damu da ku kuma zan dube ku da tausayi; za ku nome ku kuma shuka,
10 and to multiply upon you man all house: household Israel all his and to dwell [the] city and [the] desolation to build
zan kuma riɓaɓɓanya mutane a kanku, dukan gidan Isra’ila ke nan. Za a zauna a birane a kuma sāke gina rusassun wurare.
11 and to multiply upon you man and animal and to multiply and be fruitful and to dwell [obj] you like/as former your and be good from beginning your and to know for I LORD
Zan sa mutane da dabbobi su yi yawa a kanku, za su kuma ba da’ya’ya su kuma yi yawa. Zan zaunar da mutane a kanku kamar dā zan kuma sa ku wadaita fiye da dā. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
12 and to go: walk upon you man [obj] people my Israel and to possess: possess you and to be to/for them to/for inheritance and not to add: again still to/for be bereaved them
Zan sa mutanena Isra’ila su yi tafiya a kanku. Za su mallake ku, za ku kuma zama gādonsu; ba za ku ƙara sa su rasa’ya’yansu ba.
13 thus to say Lord YHWH/God because to say to/for you to eat man (you(f. s.) *Q(K)*) and be bereaved (nation your *Q(K)*) to be
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin mutane suna magana game da ku cewa, “Kun cinye mutane kuka kuma sa al’ummarku ta rasa’ya’yanta,”
14 to/for so man not to eat still (and nation your *Q(K)*) not (be bereaved *Q(K)*) still utterance Lord YHWH/God
saboda haka ba za ku ƙara cinye mutane ko ku sa al’ummarku ta rasa’ya’ya ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 and not to hear: hear to(wards) you still shame [the] nation and reproach people not to lift: bear still (and nation your *Q(K)*) not to stumble still utterance Lord YHWH/God
Ba zan ƙara bari ku ji maganar banza ta al’ummai ba, ba kuwa za ku ƙara shan ba’ar mutane ko in sa al’ummarku ta fāɗi ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
16 and to be word LORD to(wards) me to/for to say
Maganar Ubangiji ta sāke zuwa mini cewa,
17 son: child man house: household Israel to dwell upon land: soil their and to defile [obj] her in/on/with way: conduct their and in/on/with wantonness their like/as uncleanness [the] impurity to be way: conduct their to/for face: before my
“Ɗan mutum, sa’ad da mutanen Isra’ila suke zama a ƙasarsu, sun ƙazantar da ita ta wurin halinsu da kuma ayyukansu. Halinsu ya yi kamar rashin tsarkin mace a lokacin al’adarta a gabana.
18 and to pour: pour rage my upon them upon [the] blood which to pour: kill upon [the] land: country/planet and in/on/with idol their to defile her
Saboda haka na husata da su domin sun yi kisankai a ƙasar kuma domin sun ƙazantar da ita da gumakansu.
19 and to scatter [obj] them in/on/with nation and to scatter in/on/with land: country/planet like/as way: conduct their and like/as wantonness their to judge them
Na warwatsa su cikin al’ummai, suka kuwa warwatsu cikin dukan ƙasashe; na hukunta su gwargwadon halinsu da ayyukansu.
20 and to come (in): come to(wards) [the] nation which to come (in): come there and to profane/begin: profane [obj] name holiness my in/on/with to say to/for them people LORD these and from land: country/planet his to come out: come
Kuma ko’ina da suka tafi a cikin al’ummai sun ɓata sunana mai tsarki, gama an yi magana a kansu cewa, ‘Waɗannan mutanen Ubangiji ne, duk da haka dole su bar ƙasarsa.’
21 and to spare upon name holiness my which to profane/begin: profane him house: household Israel in/on/with nation which to come (in): come there [to]
Na damu saboda sunana mai tsarki, wanda gidan Isra’ila ya ɓata a cikin al’ummai inda suka tafi.
22 to/for so to say to/for house: household Israel thus to say Lord YHWH/God not because you I to make: do house: household Israel that if: except if: except to/for name holiness my which to profane/begin: profane in/on/with nation which to come (in): come there
“Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba dominku ba ne, ya gidan Isra’ila da nake yin waɗannan abubuwa, amma saboda sunana ne mai tsarki, wanda kuka ɓata a cikin al’ummai inda kuka tafi.
23 and to consecrate: holiness [obj] name my [the] great: large [the] to profane/begin: profane in/on/with nation which to profane/begin: profane in/on/with midst their and to know [the] nation for I LORD utterance Lord YHWH/God in/on/with to consecrate: holiness I in/on/with you to/for eye their
Zan nuna tsarkin girman sunana, wanda aka ɓata a cikin al’umma, sunana da kuka ɓata a cikinsu. Sa’an nan al’ummai za su san cewa ni ne Ubangiji, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinku a idanunsu.
24 and to take: take [obj] you from [the] nation and to gather [obj] you from all [the] land: country/planet and to come (in): bring [obj] you to(wards) land: soil your
“‘Gama zan fitar da ku daga al’ummai; zan tattara ku daga dukan ƙasashe in komo da ku zuwa ƙasarku.
25 and to scatter upon you water pure and be pure from all uncleanness your and from all idol your be pure [obj] you
Zan yayyafa muku ruwa mai tsabta, zan kuwa tsarkake ku daga dukan ƙazantarku daga kuma dukan gumakanku.
26 and to give: give to/for you heart new and spirit new to give: put in/on/with entrails: among your and to turn aside: remove [obj] heart [the] stone from flesh your and to give: give to/for you heart flesh
Zan ba ku sabuwa zuciya in kuma sa sabon ruhu a cikinku; zan fid da zuciyar dutse in kuma ba ku zuciyar nama.
27 and [obj] spirit my to give: put in/on/with entrails: among your and to make: do [obj] which in/on/with statute: decree my to go: walk and justice: judgement my to keep: careful and to make: do
Zan kuma sa Ruhuna a cikinku in kuma motsa ku ku bi ƙa’idodina ku kuma kiyaye dokokina.
28 and to dwell in/on/with land: country/planet which to give: give to/for father your and to be to/for me to/for people and I to be to/for you to/for God
Za ku zauna a ƙasar da na ba wa kakanninku; za ku zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
29 and to save [obj] you from all uncleanness your and to call: call to to(wards) [the] grain and to multiply [obj] him and not to give: put upon you famine
Zan cece ku daga dukan rashin tsabtarku. Zan sa hatsi ya yi yalwa ba zan kawo yunwa a kanku ba.
30 and to multiply [obj] fruit [the] tree and fruit [the] land: country because which not to take: recieve still reproach famine in/on/with nation
Zan ƙara’ya’yan itatuwa da amfanin gona, saboda kada ku ƙara shan kunya a cikin al’ummai saboda yunwa.
31 and to remember [obj] way: conduct your [the] bad: evil and deed your which not pleasant and to loath in/on/with face of your upon iniquity: crime your and upon abomination your
Sa’an nan za ku tuna mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda zunubanku da kuma ayyukanku na banƙyama.
32 not because you I to make: do utterance Lord YHWH/God to know to/for you be ashamed and be humiliated from way: journey your house: household Israel
Ina so ku san cewa ba na yi wannan saboda ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku ji kunya ku kuma giggita saboda halinku, ya gidan Isra’ila!
33 thus to say Lord YHWH/God in/on/with day be pure I [obj] you from all iniquity: crime your and to dwell [obj] [the] city and to build [the] desolation
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na tsarkake ku daga dukan zunubanku, zan sāke zaunar da ku a garuruwanku, a kuma sāke gina kufai.
34 and [the] land: country/planet [the] be desolate: destroyed to serve: labour underneath: instead which to be devastation to/for eye: seeing all to pass
Ƙasar da take kango a dā za ku nome ta a maimakon zama kango a idon dukan masu ratsawa a cikinta.
35 and to say [the] land: country/planet this [the] be desolate: destroyed to be like/as garden Eden and [the] city [the] desolate and [the] be desolate: destroyed and [the] to overthrow to gather/restrain/fortify to dwell
Za su ce, “Wannan ƙasar da take kango a dā ta zama kamar lambu Eden; biranen da dā suke kufai, kango da kuma aka lalata, yanzu suna da katanga ana kuma zama a ciki.”
36 and to know [the] nation which to remain around you for I LORD to build [the] to overthrow to plant [the] be desolate: destroyed I LORD to speak: speak and to make: do
Sa’an nan al’ummai kewaye da ku da suka rage za su san cewa Ni Ubangiji na sāke gina abin da aka lalace na kuma sāke shuka abin da yake kango. Ni Ubangiji na faɗa, kuma zan aikata.’
37 thus to say Lord YHWH/God still this to seek to/for house: household Israel to/for to make: do to/for them to multiply [obj] them like/as flock man
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa har yanzu zan ji roƙon gidan Isra’ila in kuma yi musu wannan. Zan sa mutanensu su yi yawa kamar tumaki,
38 like/as flock holiness like/as flock Jerusalem in/on/with meeting: festival her so to be [the] city [the] desolate full flock man and to know for I LORD
yawansu ya yi kamar garken tumaki don hadaya a Urushalima a ƙayyadaddun lokuta bukukkuwarta. Haka biranen da suke kufai za su cika da ɗumbun mutane. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”

< Ezekiel 36 >