< Zephaniah 1 >

1 [the] word of Yahweh - which it came to Zephaniah [the] son of Cushi [the] son of Gedaliah [the] son of Amariah [the] son of Hezekiah in [the] days of Josiah [the] son of Amon [the] king of Judah.
Maganar Ubangiji da ta zo wa Zefaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda.
2 Utterly I will bring to an end everything from on [the] surface of the ground [the] utterance of Yahweh.
“Zan hallaka kome a fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
3 I will bring to an end human being and animal I will bring to an end [the] bird[s] of the heavens and [the] fish of the sea and the stumbling-blocks with the wicked [people] and I will cut off humankind from on [the] surface of the ground [the] utterance of Yahweh.
“Zan hallaka mutane da dabbobi; zan kuma hallaka tsuntsayen sama da kifayen teku, da gumakan da suke sa mugaye su yi tuntuɓe.” “Sa’ad da zan kawar da mutum daga fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
4 And I will stretch out hand my on Judah and on all [the] inhabitants of Jerusalem and I will cut off from the place this [the] remnant of Baal [the] name of the pagan priests with the priests.
“Zan miƙa hannuna gāba da Yahuda da kuma dukan mazaunan Urushalima. Zan datse raguwar Ba’al daga wannan wuri, da sunayen firistocin gumaka da na marasa sanin Allah,
5 And those [who] bow down on the roofs to [the] host of the heavens and those [who] bow down those [who] swear an oath to Yahweh and those [who] swear an oath by Milcom.
waɗanda suka rusuna a kan rufin ɗaki don su yi sujada ga rundunar taurari. Waɗanda suka rusuna suka kuma yi rantsuwa da sunan Ubangiji suke kuma rantsuwa da sunan Molek.
6 And those [who] have turned back from after Yahweh and [those] who not they have sought Yahweh and not they have sought him.
Waɗanda suka juya daga bin Ubangiji, ba sa kuma neman Ubangiji ko su nemi nufinsa.”
7 Hush! from before [the] Lord Yahweh for [is] near [the] day of Yahweh for he has prepared Yahweh a sacrifice he has consecrated invited [ones] his.
Ku yi shiru a gaban Ubangiji Mai Iko Duka, gama ranar Ubangiji ta yi kusa. Ubangiji ya shirya hadaya; ya kuma tsarkake waɗanda ya gayyato.
8 And it will be on [the] day of [the] sacrifice of Yahweh and I will visit [judgment] on the princes and on [the] sons of the king and on all those [who] are clothed clothing foreign.
“A ranar hadayar Ubangiji zan hukunta sarakuna da kuma’ya’yan sarakuna da duk waɗanda suke sanye da rigunan ƙasashen waje.
9 And I will visit [judgment] on every [one who] leaps over the threshold on the day that those [who] fill [the] house of lord their violence and deceit.
A wannan rana zan hukunta dukan waɗanda suke kauce taka madogarar ƙofa, waɗanda suke cika haikalin allolinsu da rikici da ruɗu.
10 And it will be on the day that [the] utterance of Yahweh [the] sound of a cry of distress from [the] gate of the fish and wailing from the second district and a crashing great from the hills.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji, “Za a ji kuka daga Ƙofar Kifi, kururuwa daga Sabon Mazauni, da kuma amo mai ƙarfi daga tuddai.
11 Wail O inhabitants of the Mortar for it will be destroyed all [the] people of Canaan they will be cut off all [the] weighers of silver.
Ku yi kururuwa, ku da kuke zaune a yankin kasuwa; za a hallaka dukan’yan kasuwanku, dukan waɗanda suke kasuwanci da azurfa za su lalace.
12 And it will be at the time that I will search Jerusalem with lamps and I will visit [judgment] on the people who are thickening on lees their who are saying in heart their not he will do good Yahweh and not he will do harm.
A wannan lokaci zan bincike Urushalima da fitilu in kuma hukunta waɗanda ba su kula ba, waɗanda suke kamar ruwan inabin da aka bar a ƙasan tukunya, waɗanda suke tsammani, ‘Ubangiji ba zai yi kome ba nagari ko mummuna.’
13 And it will become wealth their plunder and houses their a desolation and they will build houses and not they will dwell [in them] and they will plant vineyards and not they will drink wine their.
Za a washe dukiyarsu, a rurrushe gidajensu. Za su gina gidaje amma ba za su zauna a ciki ba; za su shuka inabi amma ba za su sha ruwansa ba.”
14 [is] near [the] day of Yahweh great near and hurrying exceedingly [the] sound of [the] day of Yahweh bitter [is] shouting out there a warrior.
Babbar ranar Ubangiji ta yi kusa, ta yi kusa kuma tana zuwa da sauri. Ku saurara! Kukan ranar Ubangiji za tă yi zafi, za a ji kururuwan jarumi a can.
15 [will be] a day of Fury the day that a day of trouble and distress a day of devastation and desolation a day of darkness and gloom a day of cloud and thick darkness.
Ranan nan za tă zama ranar fushi, rana ce ta baƙin ciki da azaba, rana ce ta tashin hankali da lalacewa, ranar duhu baƙi ƙirin, ranar gizagizai da baƙin duhu,
16 A day of trumpet and battle-cry on the cities fortified and on the corners high.
rana ce ta busa ƙaho da kururuwar yaƙi gāba da birane masu mafaka, da kuma kusurwar hasumiyoyi.
17 And I will cause distress to humankind and they will walk like blind [people] for to Yahweh they have sinned and it will be poured out blood their like dust and bowel[s] their like dung.
“Zan kawo baƙin ciki a kan mutane za su kuma yi tafiya kamar makafi, domin sun yi wa Ubangiji zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura kayan cikinsu kuma kamar najasa.
18 Neither silver their nor gold their not it will be able to deliver them on [the] day of [the] fury of Yahweh and in [the] fire of jealousy his it will be consumed all the earth for complete destruction surely a terrible [thing] he will make with all [the] inhabitants of the earth.
Azurfarsu ko zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba a ranar fushin Ubangiji.” A cikin zafin kishinsa za a hallaka dukan duniya gama zai kawo ƙarshen dukan mazaunan duniya nan da nan.

< Zephaniah 1 >