< Zephaniah 2 >
1 Gather yourselves together and gather together O nation not ashamed.
Ku tattaru, ku tattaru, Ya ku al’umma marar kunya,
2 Before brings forth a decree like chaff it has passed away a day before - not it will come on you [the] burning of [the] anger of Yahweh before not it will come on you [the] day of [the] anger of Yahweh.
kafin ƙayyadadden lokacin nan yă zo ranan nan kuma ta share ku kamar ƙaiƙayi kuma kafin fushi mai tsanani na Ubangiji yă auko muku, kafin ranar fushin Ubangiji ta auko muku.
3 Seek Yahweh O all [the] humble [people] of the land who judgment his they have done seek righteousness seek humility perhaps you will be hidden on [the] day of [the] anger of Yahweh.
Ku nemi Ubangiji, dukanku ƙasashe masu tawali’u, ku da kuke yin abin da ya umarta. Ku nemi adalci da tawali’u; mai yiwuwa ku sami mafaka a ranar fushin Ubangiji.
4 For Gaza abandoned it will be and Ashkelon [will become] a desolation Ashdod at the noontide people will drive out it and Ekron it will be plucked up.
Za a yashe Gaza a kuma bar Ashkelon kango. Da tsakar rana Ashdod za tă zama babu kowa a kuma tumɓuke Ekron.
5 Woe to! [the] inhabitants of [the] region of the sea [the] nation of [the] Kerethites [the] word of Yahweh [is] on you O Canaan [the] land of [the] Philistines and I will destroy you from not inhabitant.
Taku ta ƙare ku da kuke zama a bakin teku, Ya ku mutanen Keretawa; maganar Ubangiji tana gāba da ke, Ya ke Kan’ana, ƙasar Filistiyawa. “Zan hallaka ki kuma babu abin da zai rage.”
6 And it will be [the] region of the sea pastures of meadows of shepherds and folds of sheep.
Ƙasar da take a bakin teku, inda Keretawa suke zaune, za tă zama wurin da makiyaya da ta garken tumaki.
7 And it will belong [the] region to [the] remnant of [the] house of Judah on them they will graze! in [the] houses of Ashkelon in the evening they will lie down! for he will visit them Yahweh God their and he will turn back (captivity their. *Q(k)*)
Za tă zama mallakar raguwar gidan Yahuda; a can za su sami wurin kiwo. Da yamma za su kwanta a gidajen Ashkelon. Ubangiji Allahnsu zai lura da su; zai maido musu da martabarsu.
8 I have heard [the] reproach of Moab and [the] reviling words of [the] people of Ammon who they have reproached people my and they have magnified themselves on territory their.
“Na ji irin zagin da Mowab take yi, da kuma ba’ar Ammonawa, waɗanda suka zagi mutanena suna kuma yi barazana a kan ƙasarsu.
9 Therefore [by] [the] life of me [the] utterance of Yahweh of hosts [the] God of Israel that Moab like Sodom it will be and [the] people of Ammon like Gomorrah a place possessed of nettle[s] and a pit of salt and a waste until perpetuity [the] remnant of people my they will plunder them and [the] rest ofK: (nation my *Q(K)*) they will take possession of them.
Saboda haka, muddin ina raye,” in ji Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, “tabbatacce Mowab za tă zama kamar Sodom, Ammonawa kuma kamar Gomorra, ƙasa mai ciyayi da rammukan gishiri, ƙasa marar amfani har abada. Raguwar mutanena za su washe su; waɗanda suka rage na al’ummata za su gāda ƙasarsu.”
10 This [will belong] to them in place of pride their for they reproached and they magnified themselves on [the] people of Yahweh of hosts.
Wannan ne zai zama sakamakon girmankansu, saboda zagi da kuma ba’ar da suka yi wa mutanen Ubangiji Maɗaukaki.
11 [will be] awesome Yahweh on them if he will make lean all [the] gods of the earth so they may bow down to him everyone from own place his all [the] islands of the nations.
Ubangiji zai zama abin tsoro a gare su sa’ad da ya hallaka allolin ƙasar. Al’ummai a kowane bakin teku za su yi masa sujada, kowa a ƙasarsa.
12 Also you O Cushites [are those] slain of sword my they.
“Ku ma, ya Kushawa, za a kashe ku da takobina.”
13 And he may stretch out hand his on [the] north so he may destroy Assyria and he may make Nineveh a waste a dry region like the wilderness.
Zai kuma miƙa hannunsa gāba da arewa yă kuma hallaka Assuriya, zai mai da Ninebe kango gaba ɗaya ta kuma zama busasshiya kamar hamada.
14 And they will lie down in [the] midst of it herds every animal of a nation both desert owl as well as hedgehog on capitals its they will spend [the] night a sound it will sing in the window desolation [will be] on the threshold for cedar-work he will lay bare.
Garkuna za su kwanta a can, da kowace irin halitta, Mujiyar hamada da bushiya za su zauna a kan ginshiƙanta. Kukansu za tă ratsa tagogi, ɓuraguzai za su tare ƙofofin shiga, za a kware ginshiƙan al’ul.
15 This [is] the city jubilant which dwells to security which says in heart its I and only I [am] yet how! - it has become a waste a resting place for animal[s] every [one who] passes by at it he will hiss he will shake hand his.
Birnin da yake harka ke nan da take zaune lafiya. Ta ce wa kanta, “Ni ce, kuma babu kamata.” Dubi irin kangon da ta zama mana, mazaunin namun jeji! Duk wanda ya wuce ta sai ya yi mata tsaki yana kaɗa kai.