< Zechariah 6 >
1 And I returned and I lifted up eyes my and I saw and there! four chariots [were] coming forth from between [the] two the mountains and the mountains [were] mountains of bronze.
Na sāke ɗaga kai sama, sai ga kekunan yaƙi guda huɗu a gabana suna fitowa tsakanin duwatsu guda biyu, duwatsun tagulla!
2 [were] with the Chariot first horses red and [were] with the chariot second horses black.
Karusa ta farko tana da jajjayen dawakai, ta biyu kuma baƙaƙen dawakai,
3 And [were] with the chariot third horses white and [were] with the chariot fourth horses dappled strong.
ta ukun farare dawakai, ta huɗu kuma dawakai masu ɗigo-ɗigo a dukan jikinsu, dukansu kuwa ƙarfafa.
4 And I answered and I said to the angel who was speaking with me what? [are] these O lord my.
Sai na tambayi mala’ikan da yake magana da ni na ce, “Mene ne waɗannan, ranka yă daɗe?”
5 And he answered the angel and he said to me these [are] [the] four [the] winds of the heavens going forth from when presented themselves on [the] lord of all the earth.
Mala’ikan ya amsa mini ya ce, “Waɗannan su ne ruhohi huɗu na sama, waɗanda suka fito daga wurin Ubangiji na dukan duniya.
6 Which with it the horses black [are] going out to [the] land of [the] north and the white [horses] they have gone out to after them and the dappled [horses] they have gone out to [the] land of the south.
Wannan mai baƙaƙen dawakai zai nufi wajen ƙasar arewa, mai fararen dawakai zai nufi wajen yamma, sai kuma mai dawakai masu ɗigo-ɗigo a jiki zai nufi wajen kudu.”
7 And the strong [horses] they have gone out and they have sought to go to go about on the earth and he said go go about on the earth and they went about on the earth.
Da ƙarfafa dawakan suka fito, sai suka yi marmari su ratsa dukan duniya. Sai ya ce, “Ku ratsa dukan duniya!” Saboda haka suka ratsa dukan duniya.
8 And he called out to with me and he spoke to me saying see those [which] are going out to [the] land of [the] north they have caused to rest spirit my in [the] land of [the] north.
Sai ya kira ni ya ce, “Duba, waɗanda suka nufi wajen ƙasar arewa sun ba wa Ruhuna hutu a ƙasar arewa.”
9 And it came [the] word of Yahweh to me saying.
Maganar Ubangiji ta zo mini, ta ce,
10 Take from with the exile[s] from Heldai and from with Tobiah and from with Jedaiah and you will go you on the day that and you will go [the] house Josiah [the] son of Zephaniah who they have come from Babylon.
“Ka karɓi azurfa da zinariya daga masu zaman bauta Heldai, Tobiya, Yedahiya, waɗanda suka iso daga Babilon. A ranar kuma ka je gidan Yosiya ɗan Zefaniya.
11 And you will take silver and gold and you will make a crown and you will put [it] on [the] head of Joshua [the] son of Jehozadak the priest great.
Ka ɗauki azurfar da zinariyar ka yi rawani, ka ɗora shi a kan babban firist, Yoshuwa ɗan Yehozadak.
12 And you will say to him saying thus he says Yahweh of hosts saying there! a man [is] Branch name his and from under him he will sprout and he will build [the] temple of Yahweh.
Ka ce masa ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ga mutumin da sunansa ne Reshe, zai kuma ratse daga inda yake yă gina haikalin Ubangiji.
13 And he he will build [the] temple of Yahweh and he he will bear majesty and he will sit and he will rule on throne his and he will be a priest on throne his and a counsel of peace it will be between [the] two of them.
Shi ne zai gina haikalin Ubangiji, za a kuma martaba shi da daraja, zai kuma zauna yă yi mulki a kan kursiyinsa. Zai zama firist a kan kursiyinsa. Kuma a tsakanin biyun za a sami zaman lafiya.’
14 And the crown it will be to Helem and to Tobiah and to Jedaiah and to Hen [the] son of Zephaniah to a memorial in [the] temple of Yahweh.
Za a ba Heldai, Tobiya, Yedahiya da kuma Hen ɗan Zefaniya kamar abin tunawa a cikin haikalin Ubangiji.
15 And distant [ones] - they will come and they will build [the] temple of Yahweh and you will know that Yahweh of hosts he has sent me to you and it will be certainly [if] you will listen! to [the] voice of Yahweh God your.
Waɗanda suke nesa za su zo su taimaka gina haikalin Ubangiji, za ku kuma san cewa Ubangiji Maɗaukaki ne ya aiko ni gare ku. Wannan zai faru in kuka yi biyayya sosai ga Ubangiji Allahnku.”