< Revelation 5 >
1 And I saw on the right hand of the [One] sitting upon the throne a scroll written inside and (on [the] back, *NK(o)*) sealed with seals seven.
Sa’an nan na ga a hannun damar wannan wanda yake zaune a kursiyin naɗaɗɗen littafi da rubutu a ciki da wajensa an kuma hatimce shi da hatimai bakwai.
2 And I saw an angel strong proclaiming in a voice loud; Who (is *k*) worthy to open the scroll and to break the seals of it?
Na kuma ga wani babban mala’ika yana shela da babbar murya cewa, “Wa ya cancanta yă ɓalle hatiman nan yă kuma buɗe naɗaɗɗen littafin?”
3 And no [one] was able in heaven (above *O*) (nor *NK(o)*) upon the earth (nor *NK(o)*) under the earth to open the scroll (nor *N(k)O*) to see it.
Amma ba wani a sama ko a ƙasa ko a ƙarƙashin ƙasan da ya iya buɗe naɗaɗɗen littafin ko ma yă duba cikinsa.
4 And (I myself *ko*) I was weeping (much *N(k)O*) because no [one] worthy was found to open (and to read *K*) the scroll nor to see it.
Na yi ta kuka domin ba a iya samun wanda ya cancanta yă buɗe naɗaɗɗen littafin ko yă duba cikinsa ba.
5 And one of the elders says to me; Not do weep. Behold has overcome the Lion who (is being *k*) of the tribe of Judah, the root of David, (The [one] *o*) (to open *NK(o)*) the scroll and (to untie *K*) the seven seals of it.
Sai ɗaya daga cikin dattawan ya ce mini, “Kada ka yi kuka! Duba, Zakin kabilar Yahuda, da kuma Tushen Dawuda ya ci nasara. Ya iya buɗe naɗaɗɗen littafin da hatimansa bakwai.”
6 And I saw (and behold *K*) in [the] midst of the throne and of the four living creatures and in [the] midst of the elders a Lamb (standing *NK(o)*) as slain (having *N(k)O*) horns seven and eyes seven (which *NK(o)*) are the seven Spirits of God (which *k*) (sent out *NK(o)*) into all the earth.
Sa’an nan na ga Ɗan Rago, yana kamar an yanka, tsaye a tsakiyar kursiyin, halittu huɗun nan masu rai da kuma dattawan an sun kewaye shi. Yana da ƙahoni bakwai da idanu bakwai, waɗanda suke ruhohi bakwai na Allah da aka aika cikin dukan duniya.
7 And He came and He has taken (*k*) (scroll *K*) out of the right hand of the [One] sitting on the throne.
Ya zo ya karɓi naɗaɗɗen littafin daga hannun dama na wannan wanda yake zaune a kursiyin.
8 And when He had taken the scroll, the four living creatures and the twenty four elders fell down before the Lamb having each (a harp *N(K)O*) and bowls golden being full of incenses which are the prayers of the saints.
Bayan ya karɓa, sai halittu huɗun nan masu rai da kuma dattawan nan ashirin da huɗu suka fāɗi ƙasa a gaban Ɗan Ragon. Kowannensu yana da garaya kuma suna riƙe da kaskon zinariya cike da turare, waɗanda suke addu’o’in tsarkaka.
9 And they are singing a song new saying; Worthy are You to take the scroll and to open the seals of it, because You were slain and You purchased to God (of us *KO*) by the blood of You out of every tribe and tongue and people and nation
Suka rera sabuwar waƙa, “Ka cancanci ka karɓi naɗaɗɗen littafin ka kuma buɗe hatimansa, domin an kashe ka, da jininka kuma ka sayi mutane wa Allah, daga kowace kabila da harshe da mutane da kuma al’umma.
10 and You have made (them *N(K)O*) to the God of us (a kingdom *N(K)O*) and priests, and (they will reign *N(K)(o)*) upon the earth.
Ka mai da su masarauta da kuma firistoci, don su yi wa Allahnmu hidima, kuma za su yi mulki a duniya.”
11 And I looked and I heard (like *O*) [the] voice of angels many (surrounding *N(k)O*) the throne and of the living creatures and of the elders. (and was the number of them myriads of myriads *NO*) and thousands of thousands
Sai na duba na kuma ji muryar mala’iku masu yawa, yawansu kuwa ya kai dubu dubbai, da kuma dubu goma sau dubu goma. Suka kewaye kursiyin da halittu huɗun nan masu rai da kuma dattawan nan.
12 saying in a voice loud: Worthy is the Lamb which slain to receive the power and (*o*) riches and wisdom and strength and honor and glory and blessing!
Da babbar murya suka rera, “Macancanci ne Ɗan Ragon nan da aka kashe, don yă sami iko da wadata da hikima da ƙarfi da girma da ɗaukaka da kuma yabo!”
13 And every creature which (is *k*) in heaven and (upon the earth *N(k)O*) and under the earth and on the sea (that *k*) (is *ko*) and in them (everything *N(k)O*) I heard saying: To the [One] sitting on (the throne *N(k)O*) and to the Lamb blessing and honor and glory and might to the ages of the ages (Amen. *O*) (aiōn )
Sa’an nan na ji kowace halitta a sama da ƙasa da ƙarƙashin ƙasa da kuma bisan teku, da kome da yake cikinsu yana rerawa, “Gare shi mai zama a kan kursiyin da kuma ga Ɗan Ragon yabo da girma da ɗaukaka da iko, (aiōn )
14 And the four living creatures (were saying; *NK(o)*) (*o*) Amen. And the (twenty four twenty four *K*) elders fell down and they worshiped ([the one] living into the ages of the ages. *K*)
Sai halittu huɗun nan masu rai suka ce, “Amin”, dattawan kuma suka fāɗi suka yi sujada.