< Psalms 59 >

1 To the choirmaster al-tashcheth of David a miktam when sent Saul and people watched the house to kill him. Deliver me from enemies my - O God my from [those who] rise up against me may you set on high me.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Sa’ad da Shawulu ya aiki mutane su yi tsaron gidan Dawuda don yă kashe shi. Ka cece ni daga abokan gābana, ya Allah; ka tsare ni daga waɗanda suka tayar mini.
2 Deliver me from [those who] do wickedness and from men of blood save me.
Ka kuɓutar da ni daga masu aikata mugunta ka kuma cece ni daga masu kisa.
3 For here! they lie in wait for life my they stir up trouble on me fierce [people] not transgression my and not sin my O Yahweh.
Duba yadda suka kwanta suna jirana! Mugaye suna ƙulle-ƙullen gāba da ni ba saboda wani dalili ko na yi wa wani zunubi ba, ya Ubangiji.
4 Not iniquity they run! and they may be established awake! to meet me and see.
Ban yi wani laifi ba, duk da haka suna a shirye su fāɗa mini. Tashi ka taimake ni; dubi halin da nake ciki!
5 And you O Yahweh God of - hosts [the] God of Israel awake! to punish all the nations may not you show favor to all [those who] act treacherously of wickedness (Selah)
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka tashi ka hukunta dukan al’ummai; kada ka nuna jinƙai ga mugaye maciya amana. (Sela)
6 They return to evening they growl like dog so they may go around [the] city.
Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
7 Here! - they pour forth! with mouth their swords [are] on lips their for who? [is] hearing.
Dubi abin da suke tofawa daga bakunansu, suna tofar da takuba daga leɓunansu, suna cewa, “Wa zai ji mu?”
8 And you O Yahweh you laugh to them you mock all [the] nations.
Amma kai, ya Ubangiji, kakan yi musu dariya; kana yi wa dukan waɗannan al’ummai ba’a.
9 Strength his to you I will watch for God [is] refuge my.
Ya ƙarfina, na dogara gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata,
10 [the] God of (Covenant loyalty my *Q(K)*) he will meet me God he will let look me on enemies my.
Allah mai ƙaunata. Allah zai sha gabana zai kuma sa in yi dariya a kan waɗanda suke magana marar kyau a kaina.
11 May not you kill them - lest they should forget people my make wander about them by strength your and bring down them O shield our O Lord.
Amma kada ka kashe su, ya Ubangiji garkuwarmu, in ba haka mutanena za su manta. Cikin ikonka ka sa su yi ta yawo barkatai, ka kuma kawar da su.
12 [the] sin of Mouth their [the] word of lips their and let them be caught in pride their and from a curse and from lying [which] they speak.
Saboda zunuban bakunansu, saboda maganganun leɓunansu, bari a kama su cikin fariyarsu. Saboda zage-zage da ƙarairayin da suke yi,
13 Make an end in anger make an end and there not [will be] them so they may know that God [is] ruling over Jacob to [the] ends of the earth (Selah)
ka cinye su da hasala, ka cinye su sarai. Sa’an nan za a sani a iyakar duniya cewa Allah yana mulki a bisa Yaƙub. (Sela)
14 So they may return to evening they growl like dog so they may go around [the] city.
Sukan dawo da yamma, suna wage haƙora kamar karnuka, suna yawo a birni.
15 They (they make wander about! *Q(K)*) to eat if not they are satisfied and they passed [the] night.
Suna ta yawo neman abinci su kuwa yi haushi in ba su ƙoshi ba.
16 And I - I will sing strength your so I may sing for joy to the morning covenant loyalty your for you have been a refuge of me and a place of escape on [the] day [when] it is distress to me.
Amma zan rera game da ƙarfinka, da safe zan rera game da ƙaunarka; gama kai ne mafakata, kagarata a lokacin wahala.
17 O strength my to you I will sing praises for God [is] refuge my [the] God of covenant loyalty my.
Ya ƙarfina, na rera yabo gare ka; kai, ya Allah, kai ne kagarata, Allah mai ƙaunata.

< Psalms 59 >