< Psalms 38 >
1 A psalm of David to make remembrance. O Yahweh may not in anger your you rebuke me and in wrath your may you chasten me.
Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
2 For arrows your they have penetrated me and it has come down on me hand your.
Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
3 There not [is] soundness in flesh my because of indignation your there not [is] health in bones my because of sin my.
Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
4 For iniquities my they have passed over head my like a burden heavy they are [too] heavy for me.
Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
5 They stink they fester wounds my because of folly my.
Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
6 I am bent down I am bent over up to muchness all the day mourning I have gone about.
An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
7 For loins my they are full burning [pain] and there not [is] soundness in flesh my.
Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
8 I am numb and I am crushed up to muchness I roar from [the] groaning of heart my.
Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
9 O Lord [is] before you all desire my and sighing my from you not it is hidden.
Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
10 Heart my it palpitates it has left me strength my and [the] light of eyes my also they not [are] with me.
Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
11 Friends my - and companions my from before plague my they stand and kinsmen my from a distance they have stood.
Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
12 And they set traps - [those who] seek life my and [those who] seek harm my they have spoken destruction and deceit all the day they devise.
Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
13 And I [am] like a deaf [person] not I hear and like a dumb [person] [who] not he opens mouth his.
Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
14 And I have become like a man who not [is] hearing and there not in mouth his [are] arguments.
Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
15 For for you O Yahweh I have waited you you will answer O Lord God my.
Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
16 For I said lest they should rejoice to me when slips foot my on me they magnified themselves.
Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
17 For I for stumbling [am] prepared and pain my [is] before me continually.
Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
18 For iniquity my I tell I am anxious from sin my.
Na furta laifina; na damu da zunubina.
19 And enemies my life they are numerous and they are many [those who] hate me falsehood.
Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
20 And [those who] repay evil in place of good they accuse me in place of (pursuing my *Q(k)*) good.
Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
21 May not you forsake me O Yahweh O God my may not you be distant from me.
Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
22 Make haste! to help my O Lord salvation my.
Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.