< Numbers 34 >
1 And he spoke Yahweh to Moses saying.
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Command [the] people of Israel and you will say to them if you [are] about to go into the land Canaan this [is] the land which it will fall to you an inheritance [the] land of Canaan to borders its.
“Ka umarci Isra’ilawa, ka ce musu, ‘Sa’ad da kuka shiga Kan’ana, ƙasar da aka ba ku gādo za tă kasance da waɗannan iyakoki.
3 And it will be of you [the] side of [the] south from [the] wilderness of Zin on [the] hands of Edom and it will be of you border of [the] southward from [the] end of [the] Sea of Salt east-ward.
“‘Gefenku na kudu zai haɗa da wani sashin Hamadan Zin ta iyakar Edom. A gabas, iyakarku ta kudu za tă fara daga ƙarshen Tekun Gishiri,
4 And it will turn of you the border from [the] south to [the] ascent of scorpions and it will pass on Zin towards (and they will be *Q(K)*) extremities its from [the] south of Kadesh Barnea and it will go out Hazar Addar and it will pass on Azmon towards.
tă ƙetare Mashigin Kunama a kudu, tă ci gaba zuwa Zin, sa’an nan tă nufi kudu da Kadesh Barneya. Sa’an nan za tă zarce zuwa Hazar Addar, tă nausa zuwa Azmon,
5 And it will turn the border from Azmon [the] wadi of towards Egypt and they will be extremities its the sea towards.
inda za tă juya tă haɗu da Rafin Masar, tă kuma ƙarasa a Bahar Rum.
6 And [the] border of [the] west and it will be for you the sea great and a border this it will be of you border of [the] west.
“‘Iyakarku a yammanci, za tă kasance bakin Bahar Rum. Wannan ce za tă zama iyakarku a yamma.
7 And this it will be of you border of [the] north from the sea great you will mark out for yourselves Hor the mountain.
“‘Iyakarku a arewanci kuwa za tă tashi daga Bahar Rum zuwa Dutsen Hor,
8 From Hor the mountain you will mark out Lebo Hamath and they will be [the] extremities of the border Zedad towards.
za tă kuma tashi daga Dutsen Hor, zuwa Lebo Hamat. Sa’an nan tă miƙe zuwa Zedad,
9 And it will go out the border Ziphron towards and they will be extremities its Hazar Enan this it will be of you border of [the] north.
tă ci gaba zuwa Zifron, sa’an nan tă ƙarasa a Hazar-Enan. Wannan ce za tă zama iyakarku a arewa.
10 And you will mark for yourselves for [the] border of east-ward from Hazar Enan Shepham towards.
“‘Iyakarku a gabashi, za tă tashi daga Hazar-Enan zuwa Shefam.
11 And it will go down the border from Shepham Riblah from [the] east of Ain and it will go down the border and it will reach to [the] shoulder of [the] sea of Kinnereth east-ward.
Iyakar za tă gangara daga Shefam zuwa Ribla a gefen gabashin Ayin, sa’an nan tă ci gaba a gangaren gabashin Tekun Kinneret.
12 And it will go down the border the Jordan towards and they will be extremities its [the] Sea of Salt this it will be of you the land to borders its all around.
Sa’an nan tă gangara ta Urdun, tă ƙarasa a Tekun Gishiri. “‘Wannan za tă zama ƙasarku, tare da iyakokinta a kowane gefe.’”
13 And he commanded Moses [the] people of Israel saying this [is] the land which you will inherit it by lot which he has commanded Yahweh to give to [the] nine the tribes and [the] half of the tribe.
Sai Musa ya umarci Isra’ilawa ya ce, “Ku raba wannan ƙasa da za ku gāda ta hanyar jefa ƙuri’a. Ubangiji ya umarta cewa a ba da ita ga kabilu tara da rabi,
14 For they have taken [the] tribe of [the] descendants of the Reubenite[s] to [the] house of ancestors their and [the] tribe of [the] descendants of the Gadite[s] to [the] house of ancestors their and [the] half of [the] tribe of Manasseh they have taken inheritance their.
saboda iyalan kabilar Ruben, kabilar Gad da rabin kabilar Manasse sun riga sun sami gādonsu.
15 [the] two The tribes and [the] half of the tribe they have taken inheritance their from [the] other side of [the] Jordan of Jericho east-ward east-ward.
Waɗannan kabilu biyu da rabi, sun sami gādonsu a wancan hayin Urdun a gabashin Yeriko wajen fitowar rana.”
16 And he spoke Yahweh to Moses saying.
Ubangiji ya ce wa Musa,
17 These [are] [the] names of the men who they will give as inheritance to you the land Eleazar the priest and Joshua [the] son of Nun.
“Waɗannan su ne sunayen mutanen da za su raba muku ƙasar gādo. Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun.
18 And a leader one a leader one from a tribe you will take to give as inheritance the land.
Ka kuma naɗa shugaba guda ɗaya daga kowace kabila domin yă taimaka a rabon ƙasar.
19 And these [are] [the] names of the men of [the] tribe of Judah Caleb [the] son of Jephunneh.
“Ga sunayensu. “Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
20 And of [the] tribe of [the] descendants of Simeon Shemuel [the] son of Ammihud.
Shemuyel ɗan Ammihud, daga kabilar Simeyon
21 Of [the] tribe of Benjamin Elidad [the] son of Chislon.
Elidad ɗan Kislon, daga kabilar Benyamin;
22 And of [the] tribe of [the] descendants of Dan a leader Bukki [the] son of Jogli.
Bukki ɗan Yogli, shugaba daga kabilar Dan;
23 Of [the] sons of Joseph of [the] tribe of [the] descendants of Manasseh a leader Hanniel [the] son of Ephod.
Hanniyel ɗan Efod, shugaba daga kabilar Manasse ɗan Yusuf;
24 And of [the] tribe of [the] descendants of Ephraim a leader Kemuel [the] son of Shiphtan.
Kemuwel ɗan Shiftan, shugaba daga kabilar Efraim ɗan Yusuf;
25 And of [the] tribe of [the] descendants of Zebulun a leader Elizaphan [the] son of Parnach.
Elizafan ɗan Farnak, shugaba daga kabilar Zebulun;
26 And of [the] tribe of [the] descendants of Issachar a leader Paltiel [the] son of Azzan.
Faltiyel ɗan Azzan, shugaba daga kabilar Issakar;
27 And of [the] tribe of [the] descendants of Asher a leader Ahihud [the] son of Shelomi.
Ahihud ɗan Shelomi, shugaba daga kabilar Asher;
28 And of [the] tribe of [the] descendants of Naphtali a leader Pedahel [the] son of Ammihud.
Fedahel ɗan Ammihud, shugaba daga kabilar Naftali.”
29 These [are those] whom he commanded Yahweh to apportion as an inheritance to [the] people of Israel in [the] land of Canaan.
Waɗannan su ne mutanen da Ubangiji ya umarta su raba gādo ga Isra’ilawa a ƙasar Kan’ana.