< Nehemiah 2 >
1 And it was - in [the] month of Nisan year twenty of Artaxerxes the king wine [was] before him and I took the wine and I gave [it]! to the king and not I had been sad before him.
A watan Nisan a shekara ta ashirin ta mulkin Sarki Artazerzes, sa’ad aka kawo masa ruwan inabi, sai na karɓa na ba shi. Ban taɓa ɓata fuskata a gabansa ba, sai wannan karo.
2 And he said to me the king why? - [is] face your sad and you not you [are] sick [is] nothing this that except sadness of heart and I was afraid greatly very.
Saboda haka sarki ya tambaye ni ya ce, “Me ya sa fuskarka ta ɓaci, ga shi, ba ciwo kake ba? Ba abin da ya kawo wannan, in ba dai kana baƙin ciki ba.” Sai na ji tsoro ƙwarai,
3 And I said to the king the king for ever may he live why? not will they be sad face my that the city [the] house of [the] tombs of ancestors my [is] desolate and gates its they have been consumed by fire.
na amsa na ce wa sarki, “Ran sarki yă daɗe! Me zai hana fuskata ta ɓaci, sa’ad da birnin da aka binne kakannina tana zaman kango, aka kuma rushe ƙofofinsa da wuta?”
4 And he said to me the king on what? this [are] you requesting and I prayed to [the] God of the heavens.
Sai sarki ya ce mini, “Me kake so?” Sai na yi addu’a ga Allah na sama,
5 And I said to the king if [is] on the king good and if he is good servant your before you that you will send me to Judah to [the] city of [the] tombs of ancestors my and I will rebuild it.
na kuwa ba wa sarki amsa, na ce, “In ya gamshi sarki, in kuma bawanka ya sami tagomashi a idonka, bari ka aike ni in tafi ƙasar Yahuda, birnin da aka binne kakannina, domin in sāke gina shi.”
6 And he said to me the king and the queen-consort - [was] sitting beside him until when? will it be journey your and when? will you return and it was good before the king and he sent me and I gave! to him a time.
Sai sarki, a lokacin sarauniya da tana zama kusa da shi, ya tambaye ni, ya ce, “Kwana nawa tafiyar za tă ɗauke ka, kuma yaushe za ka dawo?” Ya gamshi sarki ya aike ni; saboda haka na shirya lokaci.
7 And I said to the king if [is] on the king good letters let people give to me to [the] governors of beyond the River that they will allow to pass through me until that I will come to Judah.
Na kuma ce masa, “In ya gamshi sarki, zai yi kyau in sami wasiƙu zuwa ga gwamnonin Kewayen Kogin Yuferites, domin su tanada kāriya har sai na isa Yahuda?
8 And a letter to Asaph [the] keeper of the forest which [belongs] to the king that he will give to me wood to make beams for [the] gates of the citadel which [belongs] to the house and for [the] wall of the city and for the house which I will go into it and he gave [them] to me the king according to [the] hand of God my good on me.
A kuma ba ni wasiƙa zuwa ga Asaf, sarkin daji, yă ba ni katako don yin ƙofofin kagara na kusa da fadar haikali da kuma don katangar birni, da na wurin da zan zauna?” Sarki kuwa ya ba ni abin da na roƙa, gama Allah yana tare da ni.
9 And I went to [the] governors of beyond the River and I gave! to them [the] letters of the king and he had sent with me the king commanders of [the] army and horsemen.
Saboda haka na tafi wurin gwamnonin Kewayen Kogin Yuferites, na ba su wasiƙun sarki. Sarki kuma ya aika da hafsoshin mayaƙa da kuma mahayan dawakai tare da ni.
10 And he heard Sanballat the Horonite and Tobiah the servant the Ammonite and it was displeasing to them displeasure great that he had come someone to seek good for [the] people of Israel.
Da Sanballat mutumin Horon da Tobiya wakilin ƙasar Ammon suka ji cewa wani ya zo domin yă ƙarfafa zaman lafiyar mutanen Isra’ila, sai suka damu ƙwarai.
11 And I came to Jerusalem and I was there days three.
Sai na je Urushalima, bayan na zauna a can na kwanaki uku,
12 And I arose - night I and men - a few with me and not I had told to anyone what? [was] God my putting into heart my to do for Jerusalem and an animal there not [was] with me that except the animal which I [was] riding on it.
sai na fita da dare tare da mutane kalila. Ban faɗa wa wani abin da Allahna ya sa a zuciyata in yi don Urushalima ba. Ba waɗansu dabbobi kuma tare da ni, sai dai dabbar da na hau.
13 And I went out! by [the] gate of the valley night and to [the] face [the] Spring of [the] Dragons and to [the] gate of the dung and I was examining [the] walls of Jerusalem which (they - [were] broken down *Q(K)*) and gates its they had been consumed by fire.
Da dare na fita ta Ƙofar Kwari wajen Rijiyar Dila da Ƙofar Juji, ina dudduba katangar Urushalima waɗanda aka rushe da kuma ƙofofinta waɗanda aka ƙone da wuta.
14 And I passed on to [the] gate of the spring and to [the] pool of the king and there not [was] room for the animal to pass through under me.
Sa’an nan na ci gaba zuwa wajen Ƙofar Maɓuɓɓuga da kuma Tafkin Sarki, amma babu isashen wuri saboda abin da na hau yă bi;
15 And I was going up in the wadi night and I was examining the wall and I turned back and I went in [the] gate of the valley and I returned.
saboda haka na haura ta kwarin da dad dare, ina dudduba katangar. A ƙarshe, na juya na sāke shiga ta Ƙofar Kwari.
16 And the officials not they knew where? had I gone and what? [was] I doing and to the Jews and to the priests and to the nobles and to the officials and to [the] rest [who was] doing the work until thus not I had told.
Shugabanni ba su san inda na tafi, ko abin da nake yi ba, domin ban riga na faɗa wa Yahudawa, ko firistoci, ko manyan gari, ko shugabanni, ko sauran waɗanda za su yi aiki, kome ba.
17 And I said to them you [are] seeing the trouble which we [are] in it that Jerusalem [is] desolate and gates its they have been burned with fire come so we may rebuild [the] wall of Jerusalem and not we will be again a reproach.
Sai na ce musu, “Kun ga matsalar da muke ciki, yadda Urushalima ta zama kango, an kuma ƙone ƙofofinta da wuta. Ku zo mu sāke gina katangar Urushalima, ba za mu ƙara shan kunya ba.”
18 And I told to them [about] [the] hand of God my that it [was] good on me and also [the] words of the king which he had spoken to me and they said let us arise and we will rebuild and they strengthened hands their for good.
Na kuma faɗa musu game da yadda alherin Allahna yake tare da ni da kuma abin da sarki ya faɗa mini. Suka amsa, suka ce, “Mu tashi, mu kama gini.” Sai suka fara wannan aiki mai kyau.
19 And he heard Sanballat the Horonite and Tobiah - the servant the Ammonite and Geshem the Arab and they mocked us and they despised us and they said what? [is] the thing this which you [are] doing ¿ on the king [are] you rebelling.
Amma sa’ad da Sanballat mutumin Horon da Tobiya wakilin ƙasar Ammon da kuma Geshem mutumin Arab suka ji game da wannan, sai suka yi mana ba’a suka kuma yi mana dariya. Suka ce, “Me kuke tsammani kuke yi? Kuna so ku yi wa sarki tawaye ne?”
20 And I brought back them word and I said to them [the] God of the heavens he he will grant success to us and we servants his we will arise and we will rebuild and [belongs] to you not a share and a right and a memorial in Jerusalem.
Na amsa musu na ce, “Allah na sama zai ba mu nasara. Mu bayinsa za mu tashi mu fara gini, amma game da ku kam, ba ku da rabo cikin Urushalima, ba ku da wani hakki ko wani abin tunawa.”