< Micah 7 >

1 Woe! to me for I have become like gathering of summer fruit like gleanings of [the] grape harvest there not [is] a cluster of grapes to eat early fig[s] it craves appetite my.
Tawa ta ƙare! Ina kama da wanda yake tattara’ya’yan itatuwa a lokacin kalar’ya’yan inabi; babu sauran nonon inabin da za a tsinka a ci, babu kuma’ya’yan ɓaure na farko-farkon da raina yake marmari.
2 He has perished [the] faithful from the land and [is] an upright [person] among humankind there not all of them for blood they lie in wait each brother his they hunt a net.
An kawar da masu tsoron Allah daga ƙasar; babu sauran mai adalcin da ya rage. Dukan mutane suna kwanto don su zub da jini; kowa yana farautar ɗan’uwansa da tarko.
3 [are] on Evil both hands to do [it] well the official [is] asking and the judge (for bribe *L(abh)*) and the great [person] [is] speaking [the] craving of self his he and they weave it.
Dukan hannuwansu sun gwaninta wajen yin mugunta; shugabanni suna nema a ba su kyautai, alƙalai suna nema a ba su cin hanci, masu iko suna faɗar son zuciyarsu, duk suna ƙulla makirci tare.
4 Good person their [is] like a thorn-bush an upright [person] more than a thorn hedge [the] day of watchmen your punishment your it has come now it will be confusion their.
Mafi kyau a cikinsu yana kama da ƙaya, mafi gaskiyarsu ya fi shingen ƙaya muni. Ranar da Allah zai ziyarce ku ta zo, ranar da masu gadinku za su hura ƙaho. Yanzu ne lokacin ruɗewarku.
5 May not you believe in a neighbor may not you trust in a close friend from [she who] lies of bosom your guard [the] openings of mouth your.
Kada ka yarda da maƙwabci; kada ka sa begenka ga abokai. Ko ma wadda take kwance a ƙirjinka, ka yi hankali da kalmominka.
6 For a son [is] treating with contempt a father a daughter [is] arising on mother her a daughter-in-law on mother-in-law her [are the] enemies of a person [the] people of own household his.
Gama ɗa yakan ce wannan ba mahaifinsa ba ne, diya kuma takan tayar wa mahaifiyarta, matar ɗa takan yi gāba da uwar mijinta, abokan gāban mutum su ne iyalin cikin gidansa.
7 And I for Yahweh I will watch I will wait for [the] God of salvation my he will hear me God my.
Amma game da ni, zan sa bege ga Ubangiji, ina sauraron Allah Mai Cetona; Allahna kuwa zai ji ni.
8 May not you rejoice O enemy my to me for I have fallen I will arise for I sit in darkness Yahweh [will be] light of me.
Kada ku yi farin ciki, ku maƙiyana! Ko da yake na fāɗi, zan tashi. Ko da yake na zauna a cikin duhu, Ubangiji zai zama haskena.
9 [the] indignation of Yahweh I will bear for I have sinned to him until that he will conduct case my and he will do justice my he will bring out me to the light I will look on righteousness his.
Domin na yi masa zunubi, zan fuskanci fushin Ubangiji, har sai ya dubi batuna ya kuma tabbatar da’yancina. Zai kawo ni zuwa wurin haske; zan ga adalcinsa.
10 And she will see enemy my and it will cover her shame [she] who says to me where [is]? he Yahweh God your eyes my they will look on her now she will become a trampling place like [the] mud of [the] streets.
Sa’an nan maƙiyina zai gani yă kuma sha kunya, shi da yake ce da ni “Ina Ubangiji Allahnka?” Zai gani, yă kuma ji kunya. Ko yanzu ma za a tattake shi kamar taɓo a tituna.
11 A day to build walls your a day that it will be far a boundary.
Ranar gina katangarka tana zuwa, a ranar za a fadada iyakokinka.
12 A day that and to you someone will come from Assyria and [the] cities of Egypt and from Egypt and to [the] River and sea from sea and mountain the mountain.
A wannan rana mutane za su zo gare ka daga Assuriya da kuma biranen Masar, daga Masar ma har zuwa Yuferites daga teku zuwa teku, kuma daga dutse zuwa dutse.
13 And it will become the earth a desolation on inhabitants its from [the] fruit of deeds their.
Duniya za tă zama kufai saboda mazaunanta, saboda ayyukansu.
14 Shepherd people your with rod your [the] flock of inheritance your [who] dwell alone a forest in [the] midst of a garden-land let them graze Bashan and Gilead like [the] days of antiquity.
Ka yi kiwon mutanenka da sandarka, garken gādonka, wanda yake zaune shi kaɗai a kurmi, a ƙasa mai kyau ta kiwo, bari su yi kiwo a Bashan da Gileyad kamar a kwanakin dā.
15 Like [the] days coming out you from [the] land of Egypt I will show him wonders.
“Kamar a kwanakin da kuka fito daga Masar, zan nuna musu al’ajabaina.”
16 They will see nations so they may be ashamed from all strength their they will put a hand on a mouth ears their they will be deaf.
Al’ummai za su gani su kuma ji kunya, za a kuma ƙwace musu dukan ikonsu. Za su kama bakinsu kunnuwansu kuma za su zama kurame.
17 They will lick up dust like snake like [things which] crawl of [the] earth they will quake from strongholds their to Yahweh God our they will be in dread and they may be afraid from you.
Za su lashi ƙura kamar maciji, kamar dabbobi masu rarrafe a ƙasa. Za su fito daga maɓuyarsu da rawan jiki, za su juya cikin tsoro ga Ubangiji Allahnmu su kuma ji tsoronku.
18 Who? [is] a God like you [who] forgives iniquity and [who] passes over transgression to [the] remnant of inheritance his not he keeps hold of for ever anger his for [is one] desirous of covenant loyalty he.
Wane ne Allah kamar ka, wanda yake yafe zunubi yă kuma gafarta laifofin mutanensa da suka ragu? Ba ka zama mai fushi har abada amma kana marmari ka nuna jinƙai.
19 He will return he will have compassion on us he will subdue iniquities our so you may cast in [the] depths of [the] sea all sins their.
Za ka sāke jin tausayinmu; za ka tattake zunubanmu a ƙarƙashin sawunka ka kuma tura dukan kurakuranmu zuwa cikin zurfafan teku.
20 You will give faithfulness to Jacob covenant loyalty to Abraham which you swore to fathers our from days of antiquity.
Za ka yi wa Yaƙub aminci, ka kuma nuna jinƙai ga Ibrahim, kamar yadda ka yi alkawari da rantsuwa ga kakanninmu tun a kwanankin dā.

< Micah 7 >