< Matthew 26 >

1 And it came to pass when finished Jesus all words these, He said to the disciples of Him;
Sa’ad da Yesu ya gama faɗin dukan waɗannan abubuwa, sai ya ce wa almajiransa,
2 You know that after two days the Passover takes place, and the Son of Man is delivered over to be crucified.
“Kamar yadda kuka sani, Bikin Ƙetarewa sauran kwana biyu, za a kuma ba da Ɗan Mutum don a gicciye shi.”
3 Then were gathered together the chief priests (and scribes *K*) and the elders of the people in the courtyard of the high priest who is being named Caiaphas
Sai manyan firistoci da dattawan mutane, suka taru a fadan babban firist, mai suna Kayifas,
4 and they plotted together in order that Jesus by guile they may seize and may kill.
suka ƙulla shawara su kama Yesu da makirci, su kuma kashe shi.
5 They were saying however; Not [seize him] during the feast, that not a riot may happen among the people.
Suka ce, “Amma ba a lokacin Biki ba, don kada mutane su tā da rikici.”
6 And of Jesus having been in Bethany in [the] house of Simon the leper
Yayinda Yesu yake a Betani, a gidan wani mutumin da ake kira Siman Kuturu,
7 came to Him a woman having an alabaster flask of fragrant oil very costly and poured [it] on (the head *N(k)O*) when he is reclining.
wata mace ta zo wurinsa da wani ɗan tulun alabasta na turaren mai tsada sosai, wanda ta zuba a kansa a lokacin da yake cin abinci.
8 Having seen then the disciples (of him *k*) became indignant saying; For what purpose [is] the waste this?
Sa’ad da almajiransa suka ga wannan, sai suka yi fushi. Suka ce, “Wannan almubazzaranci fa!
9 It was possible for this (*k*) (fragrant oil *K*) to be sold for much and to be given to [the] poor.
Wannan turare ai, da an sayar da shi da kuɗi mai yawa a ba matalauta kuɗin.”
10 Having known [this] now Jesus said to them; Why trouble do you cause to the woman? A work for beautiful she did to Me myself.
Sane da wannan, Yesu ya ce musu, “Me ya sa kuke damun macen nan? Ta yi mini abu mai kyau ne.
11 Always for the poor you have with yourselves, Me myself however not always you have.
Matalauta za su kasance tare da ku kullum, amma ni ba zan kasance tare da ku kullum ba.
12 In pouring for this [woman] fragrant oil this on the body of Mine for to bury Me she did [it].
Sa’ad da ta zuba turaren nan a jikina, ta shirya ni ne don jana’izata.
13 Amen I say to you; wherever if shall be proclaimed gospel this in all the world, will be spoken of also that which did this [woman] for a memorial of her.
Gaskiya nake gaya muku, duk inda aka yi wa’azin bisharan nan a duniya duka, abin da matan nan ta yi, za a riƙa faɗarsa don tunawa da ita.”
14 Then having gone one of the Twelve, the [one] being named Judas Iscariot, to the chief priests
Sai ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, wanda ake kira Yahuda Iskariyot, ya je wurin manyan firistoci
15 he said; What are you willing me to give, and I myself and I myself to you will betray Him? And they appointed to him thirty pieces of silver.
ya ce, “Me za ku ba ni, in na bashe shi gare ku?” Sai suka ƙirga masa kuɗi azurfa talatin.
16 And from that time he was seeking an opportunity that Him he may betray.
Daga wannan lokaci, Yahuda ya yi ta neman zarafin da zai miƙa shi.
17 On the now first [day] of the unleavened [bread] came the disciples to Jesus saying (to him: *k*) Where wish you [that] (we may prepare *NK(o)*) for You to eat the Passover?
A rana ta fari ta Bikin Burodi Marar Yisti, sai almajiran suka zo wurin Yesu suka yi tambaya suka ce, “Ina kake so mu je mu shirya maka wurin da za ka ci Bikin Ƙetarewa?”
18 And He said; do go into the city unto a certain man and do tell him: the Teacher says; The time for Me near is, with you I keep the Passover with the disciples of Mine.’
Ya amsa ya ce, “Ku shiga gari wurin wāne, ku ce masa, ‘Malam ya ce, lokacina ya yi kusa. Zan ci Bikin Ƙetarewa tare da almajiraina a gidanka.’”
19 And did the disciples as directed them Jesus, and prepared the Passover.
Saboda haka almajiran suka yi yadda Yesu ya umarce su, suka kuwa shirya Bikin Ƙetarewa.
20 As evening now having arrived He was reclining with the twelve (disciples. *O*)
Da yamma ta yi, sai Yesu ya zauna don cin abinci tare da Sha Biyun.
21 And when were eating they He said; Amen I say to you that one of you will betray Me.
Yayinda suke cin abinci, sai ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
22 And being grieved exceedingly they began to say to Him one each (of them: *k*) surely not ever I myself is it, Lord?
Suka yi baƙin ciki ƙwarai, suka fara ce masa da ɗaya-ɗaya, “Gaskiya nake gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.”
23 And answering He said; The [one] having dipped with Me the hand in the dish he Me will betray.
Yesu ya amsa ya ce, “Wanda ya sa hannunsa a kwano tare da ni ne, zai bashe ni.
24 Indeed the Son of Man goes even as it has been written about Him, woe however for the man that [one] through whom the Son of Man is betrayed; Better was being for him if not was born the man that.
Ɗan Mutum zai tafi kamar yadda aka rubuta game da shi. Amma kaiton mutumin da zai bashe Ɗan Mutum! Da ma ba a haifi mutumin nan ba, da ya fi masa.”
25 Answering now Judas who is betraying Him said; surely not ever I myself is it, Rabbi? He says to him; You yourself have said.
Sa’an nan Yahuda, wanda zai bashe shi ya ce, “Tabbatacce ba ni ba ne, ko, Rabbi?” Yesu ya amsa ya ce, “I, kai ma ka fada.”
26 When were eating now they having taken Jesus (*k*) bread and (having blessed *NK(O)*) broke [it], and (giving *N(k)O*) to the disciples (and *k*) He said; do take do eat; this is the body of Me.
Yayinda suke cikin cin abinci, Yesu ya ɗauki burodi, ya yi godiya ya kuma kakkarya, ya ba wa almajiransa yana cewa, “Ku karɓa ku ci; wannan jikina ne.”
27 And having taken (*k*) a cup and having given thanks He gave [it] to them saying; do drink of it all of you;
Sa’an nan ya ɗauki kwaf, ya yi godiya, ya kuma ba su, yana cewa, “Ku shassha daga cikinsa, dukanku.
28 This for is the blood of Mine (*k*) of the (of a new *KO*) covenant for many being poured out for forgiveness of sins.
Wannan jinina ne na sabon alkawari, wanda aka zubar saboda mutane da yawa, don gafarar zunubai.
29 I say now to you (that: *k*) certainly not shall I drink from now of this the (fruit *N(k)O*) of the vine until the day that when it I may drink with you anew in the kingdom of the Father of Mine.
Ina gaya muku, ba zan ƙara shan ruwan inabin nan ba har sai ranar da zan sha shi sabo tare da ku a mulkin Ubana.”
30 And having sung a hymn they went out to the Mount of Olives.
Da suka rera waƙa, sai suka fita, suka tafi Dutsen Zaitun.
31 Then says to them Jesus; All you yourselves will fall away because of Me myself during night this; It has been written for: I will strike the shepherd, and (they will be scattered *N(k)O*) the sheep of the flock.’
Sai Yesu ya ce musu, “A wannan dare, dukanku za ku ja da baya saboda ni, gama a rubuce yake cewa, “‘Zan bugi makiyayin, tumakin garken kuwa za su fasu.’
32 After however to raise Me I will go before you into Galilee.
Amma bayan na tashi, zan sha gabanku zuwa Galili.”
33 Answering now Peter said to Him; If (even *k*) all will fall away because of You, I myself (but *k*) never will fall away.
Bitrus ya amsa ya ce, “Ko da duka sun ja da baya saboda kai, ba zan taɓa ja da baya ba.”
34 was saying to him Jesus; Amen I say to you that during this night before [the] rooster crowing three times you will deny Me.
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya maka, a daren nan, kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sanina sau uku.”
35 Says to Him Peter; Even if Even if it shall be necessary for me with You to die, certainly not You (I will deny. *NK(o)*) Likewise (now *o*) also all the disciples said.
Bitrus ya furta, “Ko da ma zan mutu ne tare da kai, ba zan taɓa yin mūsun saninka ba.” Dukan sauran almajiran ma suka faɗa haka.
36 Then comes with them Jesus to a place being named Gethsemane and He says to the disciples; do sit here until that having gone away over there I may pray.
Sa’an nan Yesu ya tafi da almajiransa zuwa wani wurin da ake kira Getsemane, ya ce musu, “Ku zauna nan, in je can in yi addu’a.”
37 And having taken with [Him] Peter and the two sons of Zebedee He began to be sorrowful and to be deeply distressed.
Ya ɗauki Bitrus da’ya’ya biyun nan na Zebedi tare da shi, sai ya fara baƙin ciki, ya kuma damu.
38 Then He says to them (*o*) (Jesus: *O*) Very sorrowful is the soul of Mine until death; do remain here and do watch with Me.
Sai ya ce musu, “Raina yana cike da baƙin ciki har kamar zan mutu. Ku dakata a nan, ku kuma yi tsaro tare da ni.”
39 And (having gone forward *NK(o)*) a little He fell upon face of Him praying and saying; Father of Mine, if possible it is, should pass from Me cup this; Nevertheless not [it is] as I myself wish but as You.
Da ya yi gaba kaɗan, sai ya fāɗi a ƙasa, ya yi addu’a ya ce, “Ubana, in mai yiwuwa ne, a ɗauke mini wannan kwaf. Amma ba nufina ba, sai naka.”
40 And He comes to the disciples and finds them sleeping And He says to Peter; Thus not were you able one hour to watch with Me?
Sa’an nan ya komo wurin almajiransa, ya tarar suna barci. Ya tambayi Bitrus ya ce, “Ashe, ba za ku iya yin tsaro tare da ni ko na sa’a guda ba?
41 do watch and do pray that not you may enter into temptation. The indeed spirit [is] willing however the flesh weak.
Ku yi tsaro, ku kuma yi addu’a, don kada ku fāɗi cikin jarraba. Ruhu yana so, sai dai jiki raunana ne.”
42 Again for a second time having gone away He prayed saying; Father of Mine, if not is possible this (cup *K*) to pass (from Me *k*) only unless it I shall drink, [then] should be [done] the will of You.
Ya sāke tafiya sau na biyu, ya yi addu’a ya ce, “Ubana, in ba zai yiwu a ɗauke wannan kwaf ba sai na sha shi, to, bari a aikata nufinka.”
43 And having come again (He found *N(k)O*) them sleeping; were for of them the eyes wearied.
Da ya dawo, har yanzu ya tarar suna barci, domin idanunsu sun yi nauyi da barci.
44 And having left them again having gone away He prayed for [the] third time the same thing having said (again. *no*)
Saboda haka ya sāke barinsu, ya yi addu’a sau na uku, yana maimaita iri abu guda.
45 Then He comes to the disciples (of him *k*) and says to them; Sleep later on and take your rest; Behold has drawn near the hour, and the Son of Man is betrayed into [the] hands of sinners.
Sa’an nan ya komo wurin almajiransa, ya ce musu, “Har yanzu kuna barci kuna hutawa ba? Ga shi, sa’a ta yi kusa, an kuma bashe Ɗan Mutum a hannuwan masu zunubi.
46 do rise up let us go; Behold he has drawn near who is betraying Me!
Ku tashi, mu tafi! Ga mai bashe ni nan yana zuwa!”
47 And yet when he is speaking behold Judas one of the Twelve came, and with him a crowd great with swords and clubs from the chief priests and elders of the people.
Yayinda yana cikin magana, sai Yahuda, ɗaya daga cikin Sha Biyun nan, ya iso. Tare da shi kuwa ga taro mai yawa riƙe da takuba da sanduna, manyan firistoci da dattawan mutane ne suka turo su.
48 The [one] then betraying Him gave to them a sign saying; Whomever maybe I may kiss, He himself it is; do seize Him.
To, mai bashe shi ɗin, ya riga ya shirya alama da su, “Wanda na yi masa sumba, shi ne mutumin; ku kama shi.”
49 And immediately having come up to Jesus he said; Greetings Rabbi, and kissed Him.
Da zuwansa, sai ya miƙe zuwa wurin Yesu ya ce, “Gaisuwa, Rabbi!” Sa’an nan ya yi masa sumba.
50 And Jesus said to him; Friend, [do] for (what *N(k)O*) you are come. Then having come to [him] they laid hands on Jesus and seized Him.
Yesu ya amsa ya ce, “Aboki, yi abin da ya kawo ka.” Sa’an nan mutanen suka matso, suka kama Yesu suka riƙe shi.
51 And behold one of those with Jesus having stretched out the hand drew the sword of him, and having struck the servant of the high priest cut off of him the ear.
Ganin haka, sai ɗaya daga cikin waɗanda suke tare da Yesu, ya zaro takobinsa ya kai wa bawan babban firist sara, ya fille masa kunne.
52 Then says to him Jesus; do return the sword of you into the place of it; all for those having taken [the] sword by [the] sword (will perish. *NK(o)*)
Sai Yesu ya ce, masa, “Mai da takobinka kube, gama duk masu zare takobi, a takobi za su mutu.
53 Or think you that not I am able to call upon the Father of Mine, and He will furnish to Me presently (more *N(k)O*) (than *k*) twelve (legions *N(k)O*) of angels?
Kuna tsammani ba zan iya kira Ubana, nan take kuwa yă aiko mini fiye da rundunar mala’iku goma sha biyu ba?
54 How then may be fulfilled the Scriptures that so it must be being?
Amma ta yaya za a cika Nassin da ya ce dole haka yă faru?”
55 In that [very] hour said Jesus to the crowds; As against a robber did you come out with swords and clubs to capture Me? Every day (to you *KO*) in the temple I was sitting teaching and not you did seize Me.
A wannan lokaci sai Yesu ya ce wa taron, “Ina jagoran wani tawaye ne, da kuka fito da takuba da kuma sanduna domin ku kama ni? Kowace rana ina zama a filin haikali ina koyarwa, ba ku kuwa kama ni ba.
56 This then all has come to pass that may be fulfilled the Scriptures of the prophets. Then the disciples all having forsaken Him fled.
Amma wannan duka ya faru ne don a cika rubuce-rubucen annabawa.” Sa’an nan dukan almajiran suka yashe shi suka gudu.
57 Those then having seized Jesus led [Him] away to Caiaphas the high priest where the scribes and the elders were assembled.
Waɗanda suka kama Yesu kuwa suka kai shi wurin Kayifas, babban firist, inda malaman dokoki da dattawa suka taru.
58 And Peter was following Him from afar until the court of the high priest, And having entered within he was sitting with the guards to see the outcome.
Amma Bitrus ya bi daga nesa, har zuwa cikin filin gidan babban firist. Ya shiga, ya zauna tare da masu gadi, don yă ga ƙarshen abin.
59 And the chief priests and (elders and *K*) the Council whole were seeking false testimony against Jesus so that him (they may put to death *NK(o)*)
Sai manyan firistoci da’yan majalisa duka suka yi ta neman shaidar ƙarya a kan Yesu, don su sami dama su kashe shi.
60 but not any they found (and *k*) of many having come forward as false witnesses (not they found. *k*) Finally then having come forward two (false witnesses *k*)
Amma ba su sami ko ɗaya ba, ko da yake masu shaidar ƙarya da yawa sun firfito. A ƙarshe, biyu suka zo gaba,
61 they said; This [man] was saying: I am able to destroy the temple of God and in three days to rebuild it (him. *k*)
suka furta cewa, “Wannan mutum ya ce, ‘Ina iya rushe haikalin Allah, in sāke gina shi cikin kwana uku.’”
62 And having stood up the high priest said to Him; No [thing] answer you? What these you do witness against?
Sa’an nan babban firist ya miƙe tsaye, ya ce wa Yesu, “Ba ka da wata amsa? Shaidar da mutanen nan suke yi a kanka fa?”
63 And Jesus was silent. And (answering *k*) the high priest said to Him; I adjure you by God the living that us may you tell if You yourself are the Christ the Son of God.
Amma Yesu ya yi shiru. Sai babban firist ya ce masa, “Na haɗa ka da Allah mai rai. Faɗa mana in kai ne Kiristi, Ɗan Allah.”
64 Says to him Jesus; You yourself have said. But I say to you; from now you will behold the Son of Man sitting at [the] right hand of Power and coming upon the clouds of heaven.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake yadda ka faɗa. Sai dai ina gaya muku duka, nan gaba, za ku ga Ɗan Mutum zaune a hannun dama na Mai Iko, yana kuma zuwa a kan gizagizan sama.”
65 Then the high priest tears the garments of him saying (that: *k*) He has blasphemed; why any more need have we of witnesses? Behold now you have heard the blasphemy (of him. *k*)
Sa’an nan babban firist ya yage tufafinsa ya ce, “Ya yi saɓo! Don me muke bukatar ƙarin shaidu? Ga shi, yanzu kun dai ji saɓon.
66 What you do think? And answering they said; Deserving of death He is.
Me kuka gani?” Suka amsa, suka ce, “Ya cancanci mutuwa.”
67 Then they spat in the face of Him and struck Him. Others then slapped [Him]
Sai suka tottofa masa miyau a fuskarsa, suka kuma bubbuge shi da hannuwansu. Waɗansu kuma suka mammare shi
68 saying; do prophesy to us, Christ, who is the [one] having struck You?
suka ce, “Yi mana annabci, Kiristi. Wa ya buge ka?”
69 And Peter was sitting outside in the court. and came to him one servant girl saying; Also You yourself were with Jesus the Galilean.
To, Bitrus yana nan zaune a filin, sai wata yarinya baiwa, ta zo wurinsa. Ta ce, “Kai ma kana tare da Yesu mutumin Galili.”
70 And he denied before (them *k*) all saying; Not I know what you say.
Amma ya yi mūsu a gabansu duka. Ya ce, “Ban san abin da kike magana ba.”
71 Having gone out then (him *k*) to the porch saw him another [servant girl] and she says (to those *NK(o)*) there; (and *ko*) This [man] was with Jesus of Nazareth.
Sa’an nan ya fito zuwa hanyar shiga, inda wata yarinya kuma ta gan shi, ta ce wa mutanen da suke can, “Wannan mutum ma yana tare da Yesu Banazare.”
72 And again he denied with an oath that Not I know the man.
Ya sāke mūsu har da rantsuwa, yana cewa, “Ban ma san mutumin nan ba!”
73 After a little while also having come to [him] those having stood they said to Peter; Surely also you yourself of them are; even for the speech of you away you gives.
Bayan ɗan lokaci, sai na tsattsaye a wurin, suka hauro wurin Bitrus, suka ce, “Tabbatacce, kai ɗayansu ne, don harshen maganarka, ya tone ka.”
74 Then he began to curse and to swear that Not I know the man! And immediately a rooster crowed.
Sai ya fara la’antar kansa, yana ta rantsuwa yana ce musu, “Ban ma san mutumin nan ba!” Nan da take, sai zakara ya yi cara.
75 And remembered Peter the declaration (*k*) of Jesus having said (to him *k*) that Before [the] rooster crowing three times you will deny Me, And having gone out he wept bitterly.
Sai Bitrus ya tuna da maganar da Yesu ya yi cewa, “Kafin zakara yă yi cara, za ka yi mūsun sani na sau uku.” Sai ya fita waje, ya yi ta kuka.

< Matthew 26 >