< Matthew 25 >

1 Then will be likened the kingdom of the heavens to ten virgins who having taken the lamps (their own *N(k)O*) went forth to (meet *N(k)O*) the bridegroom.
“A lokacin mulkin sama zai zama kamar budurwai goma waɗanda suka ɗauki fitilunsu suka fita don su taryi ango.
2 Five now of them were foolish and (the [other] *k*) five wise;
Biyar daga cikinsu wawaye ne, biyar kuma masu hikima.
3 (Those [who] *N(k)O*) (for *no*) foolish having taken the lamps (of them *N(k)O*) not did take with their own oil,
Wawayen sun ɗauki fitilunsu, sai dai ba su riƙe mai ba.
4 but the wise took oil in the vessels (of them *k*) with the lamps (their own. *N(k)O*)
Masu hikimar kuwa suka riƙo tulunan mai da fitilunsu.
5 As was tarrying then the bridegroom they became drowsy all and were sleeping.
Ango ya yi jinkirin zuwa, sai duk suka shiga gyangyaɗi har barci ya kwashe su.
6 At middle then of [the] night a cry there was: Behold the bridegroom (comes *k*) do go forth to meet him!
“Can tsakar dare, sai aka ji kira, ana cewa, ‘Ga ango nan! Ku fito, ku tarye shi!’
7 Then arose all the virgins those and trimmed the lamps (their own. *N(k)O*)
“Sai dukan budurwan nan suka farka suka kuna fitilunsu.
8 And the foolish to the wise said; do give us of the oil of you, for the lamps of us are going out.
Sai wawayen suka ce wa masu hikimar, ‘Ku ɗan sassam mana manku; fitilunmu suna mutuwa.’
9 Answered then the wise saying; otherwise otherwise certainly (not even *no*) it may suffice for us and you. do go (now *k*) rather to those selling and do buy for yourselves.
“Su kuwa suka amsa, suka ce, ‘A’a, wataƙila ba zai ishe mu da ku ba. Gara ku je wurin masu sayarwa ku sayo.’
10 [While] are going away then they to buy came the bridegroom, and those ready went in with him to the wedding feast, and was shut the door.
“Amma yayinda suke kan tafiya garin sayen mai, sai ango ya iso. Budurwai da suke a shirye, suka shiga wajen bikin auren tare da shi. Aka kuma kulle ƙofa.
11 Afterward then come also the other virgins saying; lord lord, do open to us!
“An jima can, sai ga sauran sun iso. Suka ce, ‘Ranka yă daɗe! Ranka yă daɗe! Ka buɗe mana ƙofa!’
12 And answering he said; Amen I say to you; not I do know you.
“Amma ya amsa ya ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, ban san ku ba.’
13 do watch therefore, for neither do you know the day nor [know] the hour (in who son of man comes. *K*)
“Saboda haka sai ku zauna a faɗake, don ba ku san ranar ko sa’ar ba.
14 [It is] like for a man going on a journey [who] called [his] own servants and delivered to them the possessions of him.
“Har wa yau, za a kwatanta shi da mutumin da zai yi tafiya, wanda ya kira bayinsa ya kuma danƙa musu mallakarsa.
15 And to one indeed he gave five talents, to one however two, to one however one, to each according to the [their] own ability; and he left the region. immediately
Ga guda, ya ba shi talenti biyar na kuɗi, ga wani talenti biyu, ga wani kuma talenti ɗaya, kowa bisa ga azancinsa. Sa’an nan ya yi tafiyarsa.
16 Having gone (now *ko*) the [one] the five talents having received he traded with them and (he gained *N(k)O*) more five (talents; *K*)
Mutumin da ya karɓi talenti biyar, nan da nan ya tafi ya yi kasuwanci da su har ya sami ribar talenti biyar.
17 Likewise (and *ko*) the [one with] the two gained (and he [gained] *k*) more two.
Haka ma, wannan mai talenti biyu, shi ma ya yi riba biyu.
18 however one having received having gone away he dug in (in the *k*) (ground *N(k)O*) and (he hid *N(k)O*) the money of the master of him.
Amma mutumin da ya karɓi talenti ɗaya ɗin, ya tafi, ya tona rami, ya ɓoye kuɗin maigidansa.
19 After then much time comes the master of the servants those and takes account with them.
“Bayan an daɗe, sai maigidan bayin nan ya dawo, ya kuma daidaita lissafi da su.
20 And having come the [one] the five talents having received he brought to [him] other five talents saying; Master, five talents to me you did deliver; Behold more five talents I gained (upon them. *k*)
Mutumin da ya karɓi talenti biyar, ya kawo ƙarin talenti biyar. Ya ce, ‘Maigida, ka danƙa mini talenti biyar. Ga shi, na yi ribar biyar.’
21 was saying (now *k*) to him the master of Him; Well done, servant good and faithful! Over a few things you were faithful, over many things you will I set. do enter into the joy of the master of you!
“Maigidansa ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawan kirki mai aminci! Ka yi aminci a kan abubuwa kaɗan, zan sa ka lura da abubuwa masu yawa. Zo ka yi farin ciki tare da maigidanka!’
22 Having come then also the [one] with the two talents (having taken *k*) he said; Master, two talents to me you did deliver; Behold more two talents I gained (upon them. *k*)
“Mutumin da yake da talenti biyu, shi ma ya zo ya ce, ‘Maigida, ka danƙa mini talenti biyu; ga shi, na yi ribar biyu.’
23 was saying to him the master of Him; Well done, servant good and faithful! Over a few things you were faithful, over many things you will I set. do enter into the joy of the master of you!
“Maigidansa ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawan kirki mai aminci! Ka yi aminci a kan abubuwa kaɗan, zan sa ka lura da abubuwa masu yawa. Zo ka yi farin ciki tare da maigidanka!’
24 Having come then also the one talent having received he said; Master, I knew you that hard you are a man reaping where not you did sow and gathering from where not you did scatter;
“Sa’an nan mutumin da ya karɓi talenti ɗaya ya zo. Ya ce, ‘Maigida, na san cewa kai mutum ne mai wuyan sha’ani, kana girbi inda ba ka shuka ba, kana kuma tara inda ba ka yafa iri ba.
25 And having been afraid having gone away I hid the talent of you in the ground; Behold you have what [is] yours.
Saboda haka na ji tsoro, na je na ɓoye talentinka a ƙasa. Ga abinka.’
26 answering now the master of him said to him; Wicked servant and lazy! You knew that I reap where not I sowed and I gather from where not I scattered?
“Maigidansa ya amsa ya ce, ‘Kai mugun bawa, mai ƙyuya! Ashe, ka san cewa ina girbi inda ban yi shuka ba, ina kuma tarawa inda ban yafa iri ba?
27 It was necessary you therefore to put (the coins *N(k)O*) of mine to the bankers, and having come I myself received then would my own with interest.
To, in haka ne, ai, da ka sa kuɗina a banki, don sa’ad da na dawo da na karɓi abina da riba.
28 do take therefore from him the talent and do give [it] to the [one] having the ten talents.
“‘Karɓi talentin daga hannunsa ku ba wanda yake da talenti goma.
29 For having to everyone will be given and he will have in abundance; (from *k*) the [one] however not having, even that which he has will be taken away from him.
Gama duk mai abu za a ƙara masa, zai kuma same shi a yawalce. Duk wanda ba shi da shi kuwa, ko ɗan abin da yake da shi ma, sai an karɓe masa.
30 And the worthless servant (do cast out *N(k)O*) into the darkness outer; there will be the weeping and the gnashing of the teeth.
Ku jefar da banzan bawan nan waje, cikin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.’
31 When then may come the Son of Man in the glory of Him and all the (holy *K*) angels with Him, then He will sit upon [the] throne of glory of Him,
“Sa’ad da Ɗan Mutum ya zo cikin ɗaukakarsa, tare da dukan mala’iku, zai zauna a kursiyinsa cikin ɗaukakar sama.
32 And (they will be gathered *N(k)O*) before Him all the nations, and He will separate them from one another as the shepherd separates the sheep from the goats,
Za a tara dukan al’ummai a gabansa, zai kuma raba mutane dabam-dabam yadda makiyayi yakan ware tumaki daga awaki.
33 And He will set indeed the sheep on [the] right hand of Him, however the goats on [the] left.
Zai sa tumaki a damansa, awaki kuma a hagunsa.
34 Then will say the King to those on [the] right hand of Him; Come you who [are] blessed of the Father of mine, do inherit the prepared for you kingdom from [the] foundation of [the] world.
“Sa’an nan Sarki zai ce wa waɗanda suke damansa, ‘Ku zo, ku da Ubana ya yi wa albarka; ku karɓi gādonku, mulkin da aka shirya muku tun halittar duniya.
35 I hungered for and you gave Me to eat, I thirsted and you gave to drink me, a stranger I was and you took in Me,
Gama da nake jin yunwa, kun ciyar da ni, da nake jin ƙishirwa, kun ba ni abin sha, da nake baƙunci, kun karɓe ni,
36 naked and you clothed Me, I was sick and you visited Me, in prison I was and you came to Me.
da nake bukatar tufafi, kun yi mini sutura, da na yi rashin lafiya, kun lura da ni, da nake kurkuku, kun ziyarce ni.’
37 Then will answer Him the righteous saying; Lord, when You saw we hungering and fed [You] Or thirsting and gave [You] to drink?
“Sa’an nan masu adalci za su amsa masa, su ce, ‘Ubangiji, yaushe muka gan ka da yunwa muka ciyar da kai, ko da ƙishirwa muka ba ka abin sha?
38 When now You saw we a stranger and took [You] in Or naked and clothed [You]?
Yaushe kuma muka gan ka baƙo muka karɓe ka, ko cikin bukatar tufafi muka yi maka sutura?
39 When now You saw we (ailing *N(k)O*) or in prison and came to You?
Yaushe kuma muka gan ka cikin rashin lafiya ko a kurkuku muka ziyarce ka?’
40 And answering the King will say to them; Amen I say to you; to the extent as much as you did [it] to one of these the brothers of Mine of the least, to Me myself you did [it].
“Sarkin zai amsa ya ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, duk abin da kuka yi wa ɗaya daga cikin waɗannan’yan’uwana mafi ƙanƙanta, ni kuka yi wa.’
41 Then will He say also to those on [the] left; do depart from Me you who [are] cursed into the fire eternal which prepared for the devil and the angels of him. (aiōnios g166)
“Sa’an nan zai ce wa waɗanda suke a hagunsa, ‘Ku rabu da ni, la’anannu, zuwa cikin madawwamiyar wutar da aka shirya don Iblis da mala’ikunsa. (aiōnios g166)
42 I hungered for and nothing you gave to Me to eat, (and *o*) I thirsted and nothing You gave to drink Me,
Gama da nake jin yunwa, ba ku ba ni abinci ba, da nake jin ƙishirwa, ba ku ba ni abin sha ba,
43 a stranger I was and not You took in Me, naked and not you did clothe Me, sick and in prison and not did you visit Me.
da na yi baƙunci, ba ku karɓe ni ba, da nake bukatar tufafi, ba ku yi mini sutura ba, da na yi rashin lafiya kuma ina a kurkuku, ba ku lura da ni ba.’
44 Then will answer (to him *k*) also themselves saying; Lord, when You saw we hungering or thirsting or a stranger or naked or sick or in prison and not did minister to You?
“Su ma za su amsa, su ce, ‘Ubangiji, yaushe muka gan ka cikin yunwa ko ƙishirwa ko baƙo ko cikin bukatar tufafi ko cikin rashin lafiya ko cikin kurkuku, ba mu taimake ka ba?’
45 Then will He answer to them saying; Amen I say to you; to the extent as much as not you did [it] to one of these the least, neither to Me myself did you.
“Zai amsa, yă ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, duk abin da ba ku yi wa ɗaya daga cikin waɗannan mafi ƙanƙanta ba, ba ku yi mini ba ke nan.’
46 And will go away these into punishment eternal, but the righteous into life eternal. (aiōnios g166)
“Sa’an nan za su tafi cikin madawwamiyar hukunci, amma masu adalci kuwa za su shiga rai madawwami.” (aiōnios g166)

< Matthew 25 >