< Mark 8 >
1 In those days (again *NO*) (much *N(k)O*) [the] crowd being and not having what they may eat, having called to [Him] (Jesus *k*) the disciples (of him *k*) He says to them;
A kwanakin nan, akwai wani gagaruman taron mutane, kuma basu da abincin ci. Yesu ya kirawo almajiransa yace masu,
2 I am moved with compassion upon the crowd because already (days *N(k)O*) three they continue with Me and nothing they have that they may eat.
“Ina tausayin taron mutanen nan domin kwana uku kenan suna nan tare da ni babu abinci.
3 And if I shall send away them hungry to [the] homes of them, they will faint on the way; (And *N(K)O*) some of them (from *no*) afar (have come. *NK(o)*)
Idan na salame su su koma gidajensu ba tare da sun ci abinci ba, za su galabaita a hanya domin gidajensu na da nisa.”
4 And answered Him the disciples of Him (that *no*) From where these will be able anyone here to satisfy with bread in this desolate place?
Almajiransa suka amsa masa cewa, “A ina za mu iya samu gurasa a wannan jeji da zai ishi wadannan mutane haka?”
5 And (He was asking *N(k)O*) them; How many have you loaves? And they said; Seven.
Ya tambaye su, “gurasa nawa kuke da su?” Sai suka ce, “Bakwai.”
6 And (He directs *N(k)O*) the crowd to recline on the ground, And having taken the seven loaves, having given thanks He broke [them] and he was giving [them] to the disciples of Him that (they may set before [them]; *N(k)O*) And they set [it] before the crowd.
Ya umarci mutanen da su zauna. Ya dauki gurasar bakwai, bayan da ya yi godiya, ya kakarya gurasar, sa'annan ya umarci almajiransa da su raba wa mutanen. Su kuwa suka raba masu.
7 And they had small fish a few; And having blessed (them *no*) He ordered also (these to be set before [them]. *N(k)O*)
Suna kuma da kananan kifaye kadan. Bayan da ya yi godiya akan su, ya umurci almajiran su rabawa mutanen.
8 (And *no*) they ate (now *k*) and were satisfied, And they took up overflow of fragments seven baskets.
Sun ci sun koshi. Suka tattara ragowar, har sun cika kwanduna bakwai.
9 There were now (having eaten of *KO*) about four thousand; And He sent away them.
Akwai maza kimanin dubu hudu a wurin. Yesu ya sallame su.
10 And immediately having climbed into the boat with the disciples of Him He came into the district of Dalmanutha.
Nan take, ya shiga jirgin ruwa da almajiransa zuwa shiyyar Dalmanuta.
11 And went out the Pharisees and began to dispute with Him seeking from Him a sign from heaven, testing Him.
Sai Farisawa suka zo suka fara gardama da shi. Suna nema ya nuna masu alama daga sama, domin su gwada shi.
12 And having sighed deeply in the spirit of Him He says; Why generation this (seeks *N(k)O*) a sign? Amen I say to you, if there will be given to the generation this a sign.
Ya ja numfashi a ruhunsa yana cewa, “Don me wannan tsarar tana neman alama. Hakika ina gaya maku, babu wata alama da za a ba wannan tsarar.”
13 And having left them again having climbed (into *ko*) (boat *KO*) He went away to the other side.
Sai ya bar su ya sake shiga jirgin zuwa hayin tafkin.
14 And they forgot to take loaves and only except one loaf not they had with themselves in the boat.
A lokacin nan, almajiransa sun manta su dauki gurasa. Domin gurasa daya ce tak a garesu cikin jirgin ruwan.
15 And He was instructing to them saying; do watch out, do take heed of the leaven of the Pharisees and of the leaven of Herod.
Ya gargade su, “ku yi hattara da yisti na Farisawa da Yisti na Hirudus.”
16 And they were reasoning with one another (saying *k*) because loaves not (they have. *N(K)O*)
Almajiran suka fara tattaunawa a tsakaninsu, “Saboda ba mu da gurasa ne.”
17 And having known [it] (*ko*) (Jesus *KO*) He says to them; Why reason you because loaves not you have? Not yet do you perceive nor understand? (still *K*) Hardened do you have the heart of you?
Yesu yana sane da wannan, sa'annan ya ce masu, “Don me kuke tattaunawa akan rashin gurasa? Har yanzu baku gane ba? Har yanzu ba ku da sane? Ko zuciyar ku ta duhunta ne?”
18 Eyes having not do you see? And ears having not do you hear? And not do you remember?
Kuna da idanu, ba ku gani? Kuna da kunnuwa, ba ku ji? Ba ku tuna ba?
19 When the five loaves I broke for the five thousand how many hand-baskets of fragments full took you up? They say to Him; Twelve.
Da na kakkarya gurasar a cikin mutane dubu biyar, kwanduna nawa kuka samu ragowa? Suka ce masa, “Goma sha biyu.”
20 When (now *k(o)*) the seven to the four thousand of how many baskets [the] fillings of fragments took you up? (*ko*) (And they speak *N(k)O*) (to him; *no*) Seven.
Kuma da na kakarya gurasa bakwai a cikin mutane dubu hudu, kwanduna nawa kuka dauka cike da ragowar? Suka ce masa, “bakwai.”
21 And He was saying to them; (Not yet *N(K)O*) (how *KO*) do you understand?
Ya ce masu, “har yanzu baku gane ba?”
22 And (they come *N(K)O*) to Bethsaida, And they bring to Him a blind [man] and they implore Him that him He may touch.
Sun zo Baitsaida. Mutanen wurin suka kawo masa wani makaho, sai suka roke shi ya taba shi.
23 And having taken hold of the hand of the blind [man] (he brought *N(k)O*) him out of the village, and having spit upon the eyes of him, having laid the hands upon him He was asking him: if anything (you see? *N(K)O*)
Yesu ya rike hanun makahon, ya jagorance shi zuwa bayan kauyen. Da ya tofa yawunsa a idon mutumin, kuma ya dora hanunsa akan mutumin, sai ya tambaye shi “kana ganin wani abu kuwa?”
24 And having looked up he was saying; I see the men for as trees I see [them] walking.
Ya daga ido sai ya ce, “ina ganin mutane na tafiya kamar itatuwa.”
25 Then again (He put *NK(o)*) the hands upon the eyes of him, and (made him *K*) (look *N(K)O*) and (he restored *N(k)O*) and (he was seeing well *N(k)O*) clearly (everything. *N(k)O*)
Ya sake dora masa hannu a idanuwansa, mutumin ya bude idanuwansa, sai ya fara ganin gari da kyau.
26 And He sent him to (the *k*) home of him saying; Not into the village shall you enter (nor may you speak to anyone in village. *KO*)
Yesu ya sallame shi zuwa gidansa nan take, ya ce masa, “kada ka shiga cikin garin”
27 And went forth Jesus and the disciples of Him into the villages of Caesarea Philippi. And on the way He was questioning the disciples of Him saying to them; Whom Me do pronounce men to be?
Yesu da almajiransa sun shiga kauyukan kaisariya ta Filibi. Da suke kan hanya, sai ya tambaye su, “Shin wanene mutane ke ce da ni?”
28 And (they said *N(k)O*) (to Him saying: that *no*) John the Baptist, and others; Elijah, others now (that *no*) (one *N(k)O*) of the prophets.
Suka amsa masa suka ce, Yahaya mai Baftisma. Wasu suka ce, “Iliya”. wadansu kuma, 'Daya daga cikin anabawa”.
29 And He himself (was questioning them; *N(k)O*) You yourselves however whom Me do pronounce to be? Answering (now *k*) Peter says to Him; You yourself are the Christ.
Ya tambaye su, “Amma me ku ke ce da ni?” Bitrus ya ce, “Kai ne Almasihu.”
30 And He warned them that no one they may tell concerning Him.
Yesu ya umarce su kada su gaya wa kowa game da shi.
31 And He began to teach them that it is necessary for the Son of Man many things to suffer and to be rejected (by *N(k)O*) the elders and the chief priests and the scribes and to be killed and after three days to rise [again];
Sai ya fara koya masu cewa, dole ne Dan Mutum ya sha wahala, dattawa da marubuta da manyan Firistoci zasu ki shi, a kuma kashe shi. Bayan kwana uku, zai tashi daga matattu.
32 And openly the word He was speaking. And having taken Peter him began to rebuke Him.
Ya fadi wannan afili. Sai Birus ya ja shi gefe ya fara tsauta masa.
33 And having turned and having looked upon the disciples of Him He rebuked (*k*) Peter (and *no*) (speaks; *N(k)O*) do go behind Me, Satan, for not you have in mind the [things] of God but the [things] of men.
Amma Yesu ya juya ya dubi almajiransa sa'annan ya tsautawa Bitrus yana cewa, “Ka koma bayana Shaidan, domin kana kula da abubuwan mutane ne kawai, ba na Allah ba.”
34 And having called to [Him] the crowd with the disciples of Him He said to them; (If *NO*) (anyone *N(k)O*) desires after Me (to follow, *N(K)O*) he should deny himself and he should take up the cross of him and he should follow Me.
Sai ya kira taron jama'ar da almajiransa a wuri daya, ya ce masu, “Duk wanda yake so ya bini, dole ne ya musunci kansa, ya dauki giciyensa ya biyo ni.
35 Who[ever] for (if *N(k)O*) shall desire life (his *NK(o)*) to save, will lose it; who[ever] now maybe (will lose *N(k)O*) the life of him on account of Me and of the gospel, (this *k*) he will save it.
Domin duk wanda yake so ya ceci ransa zai rasa shi, amma duk wadda ya rasa ransa domina da kuma bishara zai cece shi.
36 What for (profits *N(k)O*) (*o*) a man (if *ko*) (to gain *N(k)O*) the world whole and (to lose *N(k)O*) the soul of him?
Me zai amfani mutum idan ya sami dukan duniya sannan ya rasa ransa.
37 (or *k*) What (for *no*) (may give *N(k)O*) a man [as] an exchange for the soul of him?
Me mutum zai bayar amaimakon ransa?
38 Who[ever] for (if *N(k)O*) shall be ashamed of Me and My words in generation this adulterous and sinful, also the Son of Man will be ashamed of him when He may come in the glory of the Father of Him with the angels holy.
Duk wanda ke jin kunyata ko maganata a wannan mazinaciyar tsara mai zunubi, Dan Mutum ma zai ji kunyarsa a lokacin da ya dawo cikin daukakar Ubansa da Malaiku masu tsarki.”