< Mark 15 >

1 And early (upon *k*) in the morning a counsel having formed the chief priests with the elders and scribes and all the Council, having bound Jesus they led [Him] away and delivered [Him] (*k*) to Pilate.
Da sassafe, sai manyan firistoci suka hadu da dattawa da manyan malamai, da majalisa suka daure Yesu, suka sa shi gaba suka mika shi ga Bilatus.
2 And questioned Him Pilate; You yourself are the King of the Jews? And answering to him (He says; *N(k)O*) You yourself have spoken.
Bilatus ya tambaye shi, kaine sarkin Yahudawa? ya amsa ya ce “haka ka ce”
3 And were accusing Him the chief priests of many things.
Sai manyan firistochi suka kawo zargi iri iri a kan Yesu.
4 And Pilate again (was questioning *N(k)O*) Him saying; Not answer You no [thing]? See how many things You (they accuse! *N(K)O*)
Bilatus ya sake tambayarsa, ba ka da abin cewa? ka lura da yawan zargi da ake yi maka.
5 But Jesus no longer no longer no [thing] answered so as to amaze Pilate.
Amma Yesu baya sake yi masa magana ba. wannan ya ba shi mamaki.
6 At then [the] feast he was releasing to them one prisoner (which they were requesting. *N(k)O*)
A lokacin idi, Bilatus ya kan sakar masu da dan bursuna wanda jama'a suka bukaci a saka,
7 There was then the [one] being named Barabbas with the rebels bound who in the insurrection murder had committed.
A cikin gidan yari, in da aka tsare wadansu yan tawaye, da masu kisan kai, akwai wani mai kisan kai, ana ce da shi Barrabbas.
8 And (having come up *N(K)O*) the crowd began to beg [him to do] even as (always *ko*) he was doing for them.
Sai Jama'a suka zo wurin Bilatus ya yi masu kamar yadda ya saba yi.
9 But Pilate answered to them saying; Wish you [that] I may release to you the King of the Jews?
Bilatus ya amsa masu ya ce, kuna so in sakar maku sarkin Yahudawa?
10 He was aware for that because of envy had delivered up Him the chief priests.
Yayi wannan domin ya sani cewa Firistoci sun bada shi ne domin suna kishin sa,
11 But the chief priests stirred up the crowd so that instead Barabbas he may release to them.
Sai Firistochi suka zuga jama'a, sai suka yi kuwwa suna cewa, a sakar masu Barrabbas amaimakon Yesu.
12 And Pilate again answering (was saying *N(k)O*) to them; What then do you wish [that] I may do to Him you named (the *no*) King of the Jews?
Bilatus ya sake yi masu tambaya “Yaya zan yi da Sarkin Yahudawa?”
13 And again they cried out; do crucify Him!
sai suka amsa da kuwwa” a “giciye shi!”
14 And Pilate was saying to them; What indeed did He commit evil But (excessively *N(k)O*) they shouted; do crucify Him!
Bilatus ya ce masu menene laifinsa sai suka kara ihu, “a giciye shi.”
15 And Pilate desiring to the crowd that which [was] satisfactory to do he released to them Barabbas and he delivered Jesus having flogged [him] that He may be crucified.
Bilatus don yana son ya farantawa jama'a zuciya sai ya sakar masu da Barrabbas sai ya yi wa Yesu bulala, sannan ya mika shi a giciye shi.
16 And the soldiers led away him into the palace, that is [the] Praetorium, and they call together all the cohort
Sojoji suka kai shi cikin kagara, suka tara rundunan soja,
17 And (they dress *N(k)O*) Him purple and placed on Him having twisted together of thorns a crown
Suka sa masa tufafin shulaiya suka nada masa rawanin kaya,
18 and they began to salute Him; Hail (the *o*) (King *N(k)O*) of the Jews!
Suna masa kirari na ba'a suna cewa, “A gaida sarkin Yahudawa!”
19 And they were striking His head with a reed and were spitting on Him, and bending the knees they were kneeling down to Him.
Sai suka buge shi a kai da kulki suka kuma tofa masa yau a fuska, suka kuma durkusa suna yi masa sujadar ba'a.
20 And when they had mocked Him, they took off him the purple and put on Him the garments (His. *N(K)O*) And they are leading out him that (they may crucify *NK(o)*) Him.
Bayan sun gama yi masa ba'a sai suka cire masa tufafin shunnaiya, sai suka maida masa tasa tufafinsa, sai suka fitar dashi don su giciye shi.
21 And they compel passing by one Simon of Cyrene coming from [the] country, the father of Alexander and Rufus, that he may carry the cross of Him.
Suna cikin tafiya sai suka hadu da wani, mai suna Saminu Bakairawani (wato uban Alizanda da Rufus); suka tillasta shi ya dauki gijiyen Yesu.
22 And they bring Him to (*no*) Golgotha a place which is (being translated, *NK(o)*) of a Skull Place.
Sojojin suka kawo Yesu wurin da ake kira Golgota (wato kokon kai)
23 And they were offering Him (to drink *K*) mixed with myrrh wine; (He *N(k)O*) however not did take [it].
Suka bashi ruwan inabi hade da mur, amma ya ki ya sha.
24 And (having crucified *N(k)O*) Him (also *no*) (they divide for themselves *N(k)O*) the garments of Him casting lots for them, who what may take.
Sai suka giciye shi, suka kuma raba tufafinsa suka kuma jefa kuri'a domin kowanne soja ya sami rabonsa.
25 It was then [the] hour third, and they crucified Him.
A sa'a ta uku aka giciye shi.
26 And there was the inscription of the accusation against Him written: The King of the Jews.
Sai aka rubuta alamar zargi da take cewa “Ga Sarkin Yahudawa”
27 And with Him they crucify two robbers, one at [the] right hand and one at [the] left of Him.
Suka kuma giciye shi tare da wadansu yan fashi guda biyu.
28 (and was fulfilled scripture which is saying And with [the] lawless was credited. *K*)
Daya a hannun damansa daya a hannun hagunsa. Domin a cika abinda nassi ya fada.
29 And those passing by were denigrating Him shaking the heads of them and saying; Aha! You who [are] destroying the temple and building [it] in three days
suke wucewa suna zaginsa suna kada kai suna cewa, “Aha! kai da zaka rushe haikali ka kuma gina shi cikin kwana uku,
30 do save Yourself (and *k*) (descending *N(k)O*) from the cross!
ka ceci kanka mana, ka sauka daga giciye!”
31 Likewise (now *k*) also the chief priests mocking among one another with the scribes were saying; Others He saved, Himself not He is able to save;
Haka ma manyan firistoci da malamai, suka yi masa ba'a suna cewa “Ya ceci wadansu amma bai iya ceci kansa ba”
32 The Christ, the King (*k*) of Israel, he should descend now from the cross that we may see and may believe (in him. *O*) And those crucified (with *no*) Him were upbraiding Him.
Bari Almasihu Sarkin Yahudawa ya sauka daga giciye. Domin mu gaskata shi, sai wadanda aka giciye shi tare dasu, suma suka yi masa ba'a.
33 (And *no*) when was arriving (now *k*) [the] hour sixth darkness came over all the land until [the] hour ninth.
sa'a ta shida zuwa sa'a ta tara, duhu ya rufe ko'ina,
34 And on the ninth (*k*) hour cried out Jesus in a voice loud (saying: *k*) Eloi Eloi, lema sabachthani? Which is being translated; O God of Mine O God of Mine, to why have You forsaken Me
A sa'a ta tara, Yesu ya tada murya da karfi ya ce Eloi, Eloi lamathsabathani?” Ma'ana Ya Allahna Ya Allahna, me ya sa ka yashe ni?”
35 And some of those having stood by listening were saying; (behold, *N(k)O*) Elijah He calls.
Wasu daga cikin na tsaye, da suka ji shi, sai suka ce, “Duba, yana kiran Iliya.”
36 Having run then (someone *N(k)O*) and having filled a sponge with vinegar, having put (both *k*) on a reed was giving to drink him saying; Wait! let us see if comes Elijah to take down him.
Sai wani ya hanzarta, ya dauki soso ya tsoma a ruwan inabi mai tsami, ya soka agora ya mika masa don yasha. Mutumin yace bari mu gani ko Iliya zai zo ya saukar da shi.
37 But Jesus having uttered a cry loud breathed His last.
Sai Yesu yayi kuka da babban murya da karfi sannan ya rasu.
38 And the veil of the temple was torn into two from top until bottom.
Sai labulen haikalin ya rabu kashi biyu daga sama har kasa.
39 Having seen then the centurion who having stood from opposite of Him that thus (having cried out *KO*) He breathed His last, he said; Truly this man [the] Son of God was.
Sa'adda da jarumin sojan da ke tsaye yana fuskantar Yesu ya ga yadda ya mutum, Sai ya ce “hakika, wannan mutum Dan Allah ne.”
40 There were then also women from afar off looking on among whom (was *ko*) also Mary Magdalene and Mary the (*k*) of James the least and of Joses mother and Salome,
Akwai kuma mata wadanda ke dubawa daga nesa. Daga cikinsu akwai Maryamu Magadala, da Maryamu( Uwar Yakubu da Yusufu) da Salome.
41 who (and *ko*) when He was in Galilee were following Him and they were ministering to Him, and other many those having come up with Him to Jerusalem.
Wadannan matan sune suka bishi sa'adda da yake Galilee suna yi masa hidima. Da wadansu mata da yawa suka zo Urushalima tare da shi.
42 And already when evening having arrived, since it was [the] Preparation that is before Sabbath before Sabbath
Da maraice an shiga shirye shirye domin kashe gari asabbaci ce.
43 (coming *N(k)O*) Joseph from Arimathea, a prominent Council member who also himself was waiting for the kingdom of God, having boldness he went in to (*no*) Pilate and asked for the body of Jesus.
Sai Yusufu daga garin Arimatiya ya zo, mutumin kirki, mai girma kuma dan majalisar dattawa, mai sauraron mulkin Allah, da gaba gadi ya tafi wurin Bilatus ya bukaci a bashi jikin Yesu.
44 And Pilate wondered if already He has died, And having called to [him] the centurion he questioned him whether (of old *NK(o)*) He had died.
Bilatus ya yi mamakin mutuwar Yesu cikin lokaci kadan, sai ya kira jarumin ya tabbattar koYesu ya mutu.
45 And having known [it] from the centurion He granted the (body *N(k)O*) to Joseph.
Bayan ya tabbattar daga wurin jarumin soja cewa Yesu ya mutu, sai ya bada jikin ga Yusufu.
46 And having bought a linen cloth, (and *k*) having taken down him he wrapped [Him] in the linen cloth and (he laid *NK(O)*) Him in (a grave *NK(o)*) which was cut out of a rock And he rolled a stone to the door of the tomb.
Yusufu ya sayo likafani. ya saukar da shi daga giciye, ya kawo likafanin nan ya lulube jikin Yesu dashi. Ya kai shi kabarin da aka sassaka da dutse, wadda ya shirya shi domin kansa. Ya kawo dutse ya rufe bakin kabarin da shi.
47 And Mary Magdalene and Mary the [mother] of Joses were watching where (He has been laid. *N(k)O*)
Maryamu Magadaliya da Maryamu Uwar Yusufu sun ga wurin da aka yi jana'izar Yesu.

< Mark 15 >