< Luke 2 >

1 It came to pass then in the days those went out a decree from Caesar Augustus to register all the world.
A waɗancan kwanaki, Kaisar Augustus ya ba da doka cewa ya kamata a yi ƙidaya a dukan masarautar Roma.
2 This (*k*) registration first took place when is governing Syria Quirinius.
(Wannan ce ƙidaya ta fari da aka yi a lokacin da Kwiriniyus yake gwamnar Suriya.)
3 And were going all to be registered, each to the (their own *N(k)O*) city.
Sai kowa ya koma garinsa don a rubuta shi.
4 Went up then also Joseph from Galilee out of [the] town of Nazareth to Judea to [the] City of David which is called Bethlehem, because of being him from [the] house and family of David,
Saboda haka Yusuf ma ya haura daga Nazaret a Galili zuwa Yahudiya, ya tafi Betlehem garin Dawuda, don shi daga gida da kuma zuriyar Dawuda ne.
5 to register with Mary who [was] betrothed to him (wife *k*) she being with child.
Ya tafi can don a rubuta shi tare da Maryamu, wadda aka yi masa alkawari zai aura, tana kuwa da ciki.
6 It came to pass then in their being them there were fulfilled the days of the giving birth of her,
Yayinda suke can, sai lokacin haihuwar jaririn ya yi,
7 And she brought forth the son of her the firstborn and wrapped in swaddling cloths him and she laid Him in (*k*) a manger, because not there was for them a place in the inn.
ta kuwa haifi ɗanta na fari. Ta nannaɗe shi a zane ta kuma kwantar da shi cikin wani kwami, don ba su sami ɗaki a masauƙi ba.
8 And shepherds were in the region same lodging in the fields and keeping watch by night over the flock of them.
Akwai makiyaya masu zama a fili kusa da wurin, suna tsaron garkunan tumakinsu da dare.
9 And (behold *KO*) an angel of [the] Lord stood by them, and [the] glory of [the] Lord shone around them, and they feared [with] fear great.
Sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare su, ɗaukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, suka kuwa tsorata ƙwarai.
10 And said to them the angel; Not do fear; behold for I bring good news to you [of] joy great which will be to all the people
Amma mala’ikan ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Na kawo muku labari mai daɗi na farin ciki mai yawa ne wanda zai zama domin dukan mutane.
11 For has been born to you today a Savior who is Christ [the] Lord in [the] City of David.
Yau a birnin Dawuda an haifa muku Mai Ceto; shi ne Kiristi Ubangiji.
12 And this [is] to you the sign: You will find a baby swaddled (and *no*) lying in (*k*) a manger.
Wannan zai zama alama a gare ku. Za ku tarar da jariri a nannaɗe a zane kwance a kwami.”
13 And suddenly there came with the angel a multitude of [the] host (heavenly *NK(o)*) praising God and saying:
Ba labari sai ga taron rundunar sama suka bayyana tare da mala’ikan, suna yabon Allah suna cewa,
14 Glory in [the] highest to God, and on earth peace among men (of good-will. *N(k)O*)
“Ɗaukaka ga Allah a can cikin sama, a duniya kuma salama ga mutane waɗanda tagomashinsa yake bisansu.”
15 And it came to pass as they were departing from them into the heaven the angels, (and *ko*) the (men *ko*) shepherds (were speaking *N(k)O*) to one another; Let us go through indeed until Bethlehem and let us see declaration this that having happened which the Lord has made known to us.
Da mala’ikun suka bar su, su suka koma sama, sai makiyayan suka ce wa juna, “Mu je Betlehem mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya sanar mana.”
16 And they came having hurried and they found both Mary and Joseph and the baby lying in the manger.
Sai suka tafi da sauri, suka tarar da Maryamu da Yusuf, da kuma jaririn kwance a kwami.
17 Having seen now (they made known *N(k)O*) concerning the declaration which having been told to them concerning Child this.
Sa’ad da suka gan shi, sai suka baza maganar da aka gaya musu game da yaron,
18 And all those having heard they marveled concerning the [things] having been spoken by the shepherds to them.
duk kuwa waɗanda suka ji wannan, suka yi mamaki a kan abin da makiyayan suka faɗa.
19 But Mary all was treasuring up declarations these pondering [them] in the heart of her.
Amma Maryamu ta riƙe dukan waɗannan abubuwa ta kuma yi ta tunaninsu a zuciyarta.
20 And (returned *N(k)O*) the shepherds glorifying and praising God for all things which they had heard and seen even as it was said to them.
Makiyayan kuwa suka koma, suna ɗaukaka suna kuma yabon Allah saboda dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, yadda aka gaya musu.
21 And when were fulfilled days eight to circumcise (Him *no*) (the child *K*) then was called the name of Him Jesus, which He had been called by the angel before conceiving He in the womb.
A rana ta takwas, da lokaci ya yi da za a yi masa kaciya, sai aka ba shi suna Yesu, sunan da mala’ika ya ba shi kafin a yi cikinsa.
22 And when were fulfilled the days of the purification of them according to the law of Moses, they brought Him to Jerusalem to present to the Lord
Da lokacin tsarkakewarsu bisa ga Dokar Musa ya cika, sai Yusuf da Maryamu suka ɗauke shi suka haura zuwa Urushalima don su miƙa shi ga Ubangiji
23 even as it has been written in [the] law of [the] Lord that Every male opening a womb holy to the Lord will be called;
(yadda yake a rubuce a Dokar Ubangiji cewa, “Kowane ɗan fari, za a keɓe shi ga Ubangiji”),
24 and to offer a sacrifice according to that said in (the *no*) law of [the] Lord; A pair of turtle doves or two young pigeons.
don kuma su miƙa hadaya bisa ga abin da aka faɗa a Dokar Ubangiji cewa, “kurciyoyi biyu ko’yan tattabarai biyu.”
25 And behold a man there was in Jerusalem whose name [was] Simeon and man this [was] righteous and devout waiting for [the] consolation of Israel; and [the] Spirit was Holy upon him.
To, akwai wani mutum a Urushalima mai suna Siman, shi mai adalci da kuma mai ibada. Yana jiran fansar Isra’ila, Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi.
26 And it was to him revealed by the Spirit Holy not to see death before than (when *no*) he may see the Christ of [the] Lord
An bayyana masa ta wurin Ruhu Mai Tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kiristi na Ubangiji.
27 And he came in the Spirit into the temple; and in the [time when] bringing in the parents the child Jesus for the [thing] [were] doing they according to that accustomed by the law for Him,
Da Ruhu ya iza shi, sai ya shiga cikin filin haikali. Sa’ad da iyayen suka kawo jaririn nan Yesu don su yi masa abin da al’adar Doka ta bukaci,
28 then he himself received Him into the arms (of him *ko*) and blessed God and said:
sai Siman ya karɓi yaron a hannuwansa ya yabi Allah, yana cewa,
29 Now You dismiss the servant of You, Lord, according to the declaration of You in peace
“Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kamar yadda ka yi alkawari, yanzu ka sallami bawanka lafiya.
30 for have seen the eyes of mine the salvation of You
Gama idanuna sun ga cetonka,
31 which You have prepared before [the] face of all the peoples,
wanda ka shirya a gaban dukan mutane,
32 a light for revelation of [the] Gentiles and glory of [the] people of You of Israel.
haske don bayyanawa ga Al’ummai da kuma ɗaukaka ga mutanenka Isra’ila.”
33 And were (the *no*) (father *N(K)O*) of Him and the mother marveling at the [things] being spoken concerning Him.
Mahaifin yaron da kuma mahaifiyarsa suka yi mamaki abin da aka faɗa game da shi.
34 And blessed them Simeon and said to Mary the mother of Him: Behold this [Child] is appointed for [the] falling and rising up of many in Israel and for a sign spoken against.
Sa’an nan Siman ya sa musu albarka ya ce wa Maryamu mahaifiyarsa, “An ƙaddara yaron nan yă zama sanadin fāɗuwa da tashin mutane da yawa a Isra’ila, zai kuma zama alamar da mutane ba za su so ba,
35 and of you also of her the soul will go through a sword — so that maybe may be revealed of many hearts [the] thoughts.
ta haka za a fallasa tunanin zukatan mutane da yawa. Ke ma, takobi zai soki zuciyarki.”
36 And there was Anna a prophetess, daughter of Phanuel, of [the] tribe of Asher; she having advanced in years great, having lived with a husband years seven from the marriage of herself;
Akwai wata annabiya ma, mai suna Anna, diyar Fanuwel, na kabilar Asher. Ta tsufa kutuf; ta yi zama da mijinta shekaru bakwai bayan sun yi aure,
37 and she [was] a widow (until *N(k)O*) years eighty [and] four who not was departing (from *k*) the temple with fastings and prayers serving night and day;
ta kuwa zama gwauruwa sai da ta kai shekaru tamanin da huɗu. Ba ta taɓa barin haikali ba, tana sujada dare da rana, tana kuma azumi da addu’a.
38 And (this *k*) she at that hour having come up she was giving praise (to God *N(K)O*) and was speaking concerning Him to all those waiting for [the] redemption (in *k*) of Jerusalem.
Tana haurawa wurinsu ke nan a wannan lokaci, sai ta yi wa Allah godiya ta kuma yi magana game da yaron nan ga dukan waɗanda suke sauraron fansar Urushalima.
39 And when they had performed (everything *N(k)O*) according to the law of [the] Lord, (they returned *N(k)O*) to Galilee to (the *k*) town (of themselves *N(k)O*) Nazareth.
Bayan da Yusuf da Maryamu suka gama yin dukan abubuwan da Dokar Ubangiji ta bukaci, sai suka koma Galili suka tafi Nazaret garinsu.
40 And the Child was continuing to grow and He was being strengthened (in spirit *K*) being filled (with wisdom, *N(k)O*) and [the] grace of God was upon Him.
Yaron kuwa ya yi girma ya yi ƙarfi; ya cika da hikima, alherin Allah kuwa yana bisansa.
41 And were going the parents of Him every year to Jerusalem at the feast of the Passover.
Kowace shekara, iyayen Yesu sukan je Urushalima don Bikin Ƙetarewa.
42 And when He was years [old] twelve (when were going up *N(k)O*) they (into Jerusalem *KO*) according to the custom of the Feast
Da Yesu ya cika shekaru goma sha biyu, sai suka tafi Bikin bisa ga al’ada.
43 and when having completed the days in the returning of them remained behind Jesus the boy in Jerusalem, But not (knew *N(k)O*) (the parents *NO*) (Joseph and the mother *K*) of Him.
Bayan Bikin, da iyayen suka kama hanya don su koma gida, sai Yesu, yaron nan, ya tsaya a Urushalima, ba da saninsu ba.
44 Having supposed now Him to be in their company they went a day’s journey and were seeking Him among the relatives and (in *k*) the acquaintances.
Su kuwa sun ɗauka yana tare da su, saboda haka, suka yi ta tafiya har na yini guda. Sa’an nan suka fara nemansa cikin’yan’uwansu da abokansu.
45 and not having found (Him *k*) they returned to Jerusalem (searching *N(k)O*) Him.
Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima nemansa.
46 And it came to pass after days three they found Him in the temple sitting in [the] midst of the teachers both hearing them and questioning them.
Bayan kwana uku, sai suka same shi a filin haikali zaune a tsakiyar malamai, yana sauraronsu yana kuma yi musu tambayoyi.
47 Were amazed then all those hearing Him at the understanding and at the answers of Him.
Dukan waɗanda suka ji shi, suka yi mamakin fahimtarsa, da amsoshinsa.
48 And having seen Him they were astonished, and said to Him the mother of Him: Child why You did to us thus? Behold the father of You and I myself and I myself distressing (were seeking *NK(o)*) You.
Da iyayensa suka gan shi sai suka yi mamaki. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, don me ka yi mana haka? Ni da mahaifinka duk mun damu muna nemanka.”
49 And He said to them; Why [is it] for you were seeking Me? Surely you knew that in the [house] of the Father of Mine it behooves to be Me?
Sai ya ce, “Don me kuke nemana? Ba ku san cewa, dole in kasance a gidan Ubana ba?”
50 And they themselves not understood the declaration that He spoke to them.
Amma ba su fahimci abin da yake faɗin musu ba.
51 And He went down with them and He came to Nazareth and He was subject to them. And the mother of Him was treasuring up all declaration (these *ko*) in the heart of her.
Sai ya koma Nazaret tare da su, yana yi musu biyayya. Mahaifiyarsa kuma ta riƙe dukan waɗannan abubuwa a zuciyarta.
52 And Jesus was continuing to advance (in *n*) (*no*) wisdom and stature and in favor with God and men.
Yesu kuwa ya yi girma, ya kuma ƙaru cikin hikima, ya kuma sami tagomashi a wurin Allah da mutane.

< Luke 2 >