< Leviticus 16 >

1 And he spoke Yahweh to Moses after [the] death of [the] two [the] sons of Aaron when drew near they before Yahweh and they died.
Ubangiji ya yi magana da Musa bayan mutuwar’ya’yan Haruna biyu maza waɗanda suka mutu sa’ad da suka kusaci Ubangiji.
2 And he said Yahweh to Moses speak to Aaron brother your and may not he come at every time into the holy place from inside to the curtain to [the] face of the atonement cover which [is] on the ark and not he will die for in the cloud I will appear over the atonement cover.
Ubangiji ya ce wa Musa, “Faɗa wa ɗan’uwanka Haruna, kada yă riƙa shiga Wuri Mafi Tsarki bayan labule koyaushe, wato, a gaban murfi wanda yake bisa akwatin alkawari, domin kada yă mutu, gama zan bayyana a cikin girgije a kan murfin.
3 With this he will come Aaron into the holy place with a bull a young one of [the] herd to a sin offering and a ram to a burnt offering.
“Ga yadda Haruna zai shiga wuri mai tsarki, zai zo da ɗan bijimi domin hadaya don zunubi da kuma rago domin hadaya ta ƙonawa.
4 A tunic of linen of holiness he will wear and undergarments of linen they will be on flesh his and with a sash of linen he will gird himself and with a turban of linen he will wind [are] garments of holiness they and he will wash with water body his and he will put on them.
Zai sa toguwar lilin mai tsarki, tare da ɗan ciki na lilin; zai yi ɗamara da igiya kewaye da shi, yă kuma sa hular lilin. Waɗannan su ne riguna masu tsarki; saboda haka dole yă yi wanka kafin yă sa su.
5 And from with [the] congregation of [the] people of Israel he will take two male goats of goats to a sin offering and a ram one to a burnt offering.
Zai ɗauki bunsurai biyu daga jama’ar Isra’ilawa na hadaya don zunubi da ɗan rago don hadaya ta ƙonawa.
6 And he will present Aaron [the] bull of the sin offering which [is] for himself and he will make atonement for himself and for household his.
“Haruna zai miƙa bijimi hadaya don zunubinsa yă kuma yi kafara don kansa da gidansa.
7 And he will take [the] two the male goats and he will station them before Yahweh [the] entrance of [the] tent of meeting.
Sa’an nan zai ɗauki bunsurai biyu yă miƙa su a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada.
8 And he will put Aaron on [the] two the male goats lots a lot one for Yahweh and a lot one for [the] escape goat.
Haruna zai jefa ƙuri’a don awaki biyun ɗin, ƙuri’a ɗaya domin Ubangiji, ɗayan kuma don azazel
9 And he will present Aaron the male goat which it came up on it the lot for Yahweh and he will offer it a sin offering.
Haruna zai kawo akuyar da ƙuri’a ta fāɗi a kai wa Ubangiji yă miƙa ta na hadaya don zunubi.
10 And the male goat which it came up on it the lot for [the] escape goat it will be stationed alive before Yahweh to make atonement on it by sending away it to [the] escape goat the wilderness towards.
Amma za a miƙa akuyar da aka zaɓa ta wurin ƙuri’a a matsayi ta azazel da rai a gaban Ubangiji don a yi amfani da ita don kafara ta wurin korinta zuwa cikin jeji kamar azazel.
11 And he will present Aaron [the] bull of the sin offering which [is] for himself and he will make atonement for himself and for household his and he will cut [the] throat of [the] bull of the sin offering which [is] for himself.
“Haruna zai kawo bijimi domin hadayarsa ta zunubi don yă yi kafara wa kansa da kuma domin gidansa, zai kuma yanka bijimin domin nasa hadaya don zunubi.
12 And he will take fullness of censer coals of fire from on the altar from to before Yahweh and [the] fullness of hands his incense of perfume fine and he will bring [them] from inside to the curtain.
Zai ɗauki faranti cike da garwashin wuta daga bagade a gaban Ubangiji, yă kuma cika hannunsa biyu da turare mai ƙanshin da aka niƙa yă kai su bayan labule.
13 And he will put the incense on the fire before Yahweh and it will cover - [the] cloud of the incense the atonement cover which [is] on the testimony and not he will die.
Zai sa turaren a wuta a gaban Ubangiji, hayaƙin turaren kuwa zai rufe murfin kafarar a bisa Akwatin Alkawari, don kada yă mutu.
14 And he will take some of [the] blood of the bull and he will spatter [it] with finger his on [the] face of the atonement cover east-ward and before the atonement cover he will spatter seven times some of the blood with finger his.
Zai ɗibi jinin bijimin da yatsarsa yă yayyafa a gaban murfin kafarar; sa’an nan yă yayyafa jinin da yatsarsa sau bakwai a gaban murfin kafarar.
15 And he will cut [the] throat of [the] male goat of the sin offering which [is] for the people and he will bring blood its to from inside to the curtain and he will do with blood its just as he did to [the] blood of the bull and he will spatter it on the atonement cover and before the atonement cover.
“Sa’an nan zai yanka akuya na hadaya don zunubi saboda mutane, yă kai jinin bayan labule, yă yi da shi yadda ya yi da jinin bijimin. Zai yayyafa shi a kan murfin kafarar da kuma a gabansa.
16 And he will make atonement on the holy place from [the] uncleanness of [the] people of Israel and from transgressions their to all sins their and thus he will do to [the] tent of meeting which dwells with them in among uncleanness their.
Ta haka zai yi kafara domin Wuri Mafi Tsarki saboda ƙazantar tawayen Isra’ilawa, da laifofinsu, da dukan zunubansu. Haka zai yi saboda Tentin Sujada wanda yake a cikinsu a tsakiyar ƙazantarsu.
17 And any person not he will be - in [the] tent of meeting when goes he to make atonement in the holy place until comes out he and he has made atonement for himself and for household his and for all [the] assembly of Israel.
Kada kowa yă kasance a Tentin Sujada daga lokacin da Haruna ya shiga don yă yi kafara a Wuri Mafi Tsarki har sai ya fita, bayan ya yi kafara domin kansa, gidansa da kuma dukan jama’ar Isra’ila.
18 And he will go out to the altar which [is] before Yahweh and he will make atonement on it and he will take some of [the] blood of the bull and some of [the] blood of the male goat and he will put [it] on [the] horns of the altar all around.
“Sa’an nan zai fita zuwa bagade da yake a gaban Ubangiji, yă yi kafara dominsa. Zai ɗibi jinin bijimi da na akuya yă zuba a ƙahonin bagade.
19 And he will spatter on it some of the blood with finger his seven times and he will purify it and he will set apart as holy it from [the] uncleanness of [the] people of Israel.
Zai yayyafa jinin a kan bagade da yatsarsa sau bakwai, yă tsabtacce shi yă kuma tsarkake shi daga ƙazantar Isra’ilawa.
20 And he will finish from making atonement for the holy place and [the] tent of meeting and the altar and he will present the male goat living.
“Sa’ad da Haruna ya gama yin kafara domin Wuri Mafi Tsarki, Tentin Sujada da kuma bagade, sai yă kawo akuya mai rai.
21 And he will lean Aaron [the] two (hands his *Q(K)*) on [the] head of the male goat living and he will confess over it all [the] iniquities of [the] people of Israel and all transgressions their to all sins their and he will put them on [the] head of the male goat and he will send [it] away by [the] hand of a man ready the wilderness towards.
Haruna zai ɗibiya hannuwansa a kan akuya mai ran, yă furta a kansa dukan mugunta da tawayen Isra’ilawa, dukan zunubansu, yă kuma sa su a kan akuyan. Zai kori akuyan zuwa cikin jeji a hannun mutumin da aka ba shi aikin yin haka.
22 And it will bear the male goat on itself all iniquities their into a land infertile and he will let go the male goat in the wilderness.
Akuyan zai ɗauka a kansa dukan zunubansu zuwa kaɗaitaccen wuri, a can mutumin zai sake shi a jeji.
23 And he will go Aaron into [the] tent of meeting and he will strip off [the] garments of linen which he wore when went he into the holy place and he will leave them there.
“Sa’an nan Haruna zai shiga Tentin Sujada yă tuɓe rigunansa na lilin da ya sa, kafin yă shiga Wuri Mafi Tsarki, zai kuma bar su a can.
24 And he will wash body his with water in a place holy and he will put on garments his and he will come out and he will offer burnt offering his and [the] burnt offering of the people and he will make atonement for himself and for the people.
Zai yi wanka a tsattsarkan wuri yă sa rigunarsa na kullum. Sa’an nan zai fita yă miƙa hadaya ta ƙonawa domin kansa da hadaya ta ƙonawa domin mutane, don yă yi kafara domin kansa da kuma domin mutane.
25 And [the] fat of the sin offering he will make smoke the altar towards.
Zai kuma ƙone kitsen hadaya don zunubi a kan bagade.
26 And the [one who] let go the male goat to [the] escape goat he will wash garments his and he will wash body his with water and after thus he will come into the camp.
“Dole mutumin da ya saki akuya na azazel yă wanke rigunansa yă kuma yi wanka; bayan haka zai iya shiga sansani.
27 And [the] bull of the sin offering and - [the] male goat of the sin offering which it was brought blood their to make atonement in the holy place someone will bring out to from [the] outside of the camp and people will burn with fire hides their and flesh their and offal their.
Dole a ɗauki jini, fata, nama da kuma ƙashin bijimi da akuyan hadaya don zunubi, waɗanda aka kawo jininsu cikin Wuri Mafi Tsarki don kafara, a kai waje da sansani a ƙone.
28 And the [one who] burns them he will wash garments his and he will wash body his with water and after thus he will come into the camp.
Dole mutumin da ya ƙone su yă wanke rigunansa yă kuma yi wanka, bayan haka zai iya shiga sansani.
29 And it will become for you a statute of perpetuity in the month seventh on the ten of the month you will afflict selves your and any work not you will do the native-born and the sojourner who sojourns in midst of you.
“Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a gare ku. A rana ta goma ga wata na bakwai, dole ku yi mūsu kanku, ba kuwa za ku yi wani aiki ba, ko da mutum baƙo ne a cikinku ko kuwa ɗan ƙasa,
30 For on the day this he will make atonement on you to purify you from all sins your before Yahweh you will be pure.
gama a wannan rana za a yi kafara dominku, don a tsarkake ku. Sa’an nan a gaban Ubangiji, za a tsarkake ku daga dukan zunubanku.
31 [is] a sabbath of Sabbath observance it to you and you will afflict selves your a statute of perpetuity.
Asabbaci ne don hutawa, kuma dole ku yi mūsun kanku; wannan dawwammamiyar farilla ce.
32 And he will make atonement the priest whom someone will anoint him and whom someone will fill hand his to serve as priest in place of father his and he will wear [the] garments of linen [the] garments of holiness.
Firist da aka keɓe aka kuma naɗa don yă gāji mahaifinsa a matsayin babban firist ne zai yi kafara. Zai sa rigunan lilin masu tsarki
33 And he will make atonement for [the] sanctuary of holiness and [the] tent of meeting and the altar he will make atonement for and on the priests and on all [the] people of the assembly he will make atonement.
yă yi kafara domin Wuri Mafi Tsarki, Tentin Sujada da bagade, da kuma saboda firistoci da kuma dukan jama’ar Isra’ila.
34 And it will become this for you a statute of perpetuity to make atonement on [the] people of Israel from all sins their one [time] in the year and he did just as he had commanded Yahweh Moses.
“Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce gare ku. Za a riƙa yin kafara sau ɗaya a shekara saboda dukan zunuban Isra’ilawa.” Aka kuma yi haka, yadda Ubangiji ya umarci Musa.

< Leviticus 16 >