< Judges 5 >

1 And she sang Deborah and Barak [the] son of Abinoam on the day that saying.
A wannan rana ce Debora da Barak ɗan Abinowam suka rera wannan waƙa.
2 When acted as leaders heads in Israel when volunteers a people bless Yahweh.
“Sa’ad da’ya’yan sarki a Isra’ila suka yi jagora, sa’ad da mutane suka niyya su ba da kansu, suna yabon Ubangiji!
3 Hear O kings give ear O rulers I to Yahweh I I will sing I will sing praises to Yahweh [the] God of Israel.
“Ya sarakuna, ku ji! Ku saurara, ku masu mulki! Zan yi waƙa ga Ubangiji, zan yi waƙa; zan yi kaɗe-kaɗe ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
4 O Yahweh when going out you from Seir when marching you from [the] region of Edom [the] earth it shook both [the] heavens they dropped as well as [the] clouds they dropped water.
“Ya Ubangiji, sa’ad da ka bar Seyir, sa’ad da ka yi tafiya daga ƙasar Edom, ƙasa ta girgiza, sammai suka zubo, gizagizai sun zubo da ruwa.
5 [the] mountains They flowed from before Yahweh this Sinai from before Yahweh [the] God of Israel.
Duwatsu suka girgizu a gaban Ubangiji, Wannan na Sinai, a gaban Ubangiji, Allah na Isra’ila.
6 In [the] days of Shamgar [the] son of Anath in [the] days of Jael they ceased roads and walkers of paths they walked roads twisting.
“A zamanin Shamgar ɗan Anat, a zamanin Yayel, an yashe dukan hanyoyi; matafiye suka bi hanyoyin da suka yi kona-kona.
7 They ceased rural people in Israel they ceased until that I arose Deborah that I arose a mother in Israel.
Rayuwar ƙauye a Isra’ila ta daina, ta daina sai da ni, Debora, na taso, na taso mahaifiya a Isra’ila.
8 It chose gods new then bread gates a shield if it was seen and a spear among forty thousand in Israel.
Sa’ad da suka zaɓi sababbin alloli, sai ga yaƙi a ƙofofin birnin, ba a kuwa ga garkuwa ko māshi a cikin mutum dubu arba’in a Isra’ila ba.
9 Heart my [is] for [the] commanders of Israel those [who] volunteered among the people bless Yahweh.
Zuciyata tana tare da’ya’yan sarakunan Isra’ila, tare da masu niyyar ba da kansu da yardan rai cikin mutane. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!
10 O riders of female donkeys tawny O [you who] sit on cloth garments and O walkers on [the] road tell out.
“Ku da kuke hawan fararen jakuna, kuna zama a sirdin barguna, da ku da kuke tafiya a kan hanya, ku kula
11 From [the] sound of archers between [the] places for drawing water there they will recount [the] righteousness of Yahweh [the] righteousness of rural people his in Israel then they went down to the gates [the] people of Yahweh.
da muryoyin mawaƙa a wuraren ruwaye. Suna faɗi ayyukan adalcin Ubangiji, ayyukan adalcin mayaƙansa a Isra’ila. “Sa’an nan mutanen Ubangiji suka gangara zuwa ƙofofin birni.
12 Awake awake O Deborah awake awake speak a song arise O Barak and take captive captive[s] your O son of Abinoam.
‘Ki farka, ki farka, Debora! Ki farka, ki farka, ki tā da waƙa! Ka farka, ya Barak! Ka ta sa kamammunka gaba, ya ɗan Abinowam.’
13 Then he went down [the] survivor[s] of [the] nobles [the] people Yahweh he went down to me among the mighty [ones].
“Sa’an nan waɗanda aka bari suka sauko zuwa wajen shugabanni; mutane na Ubangiji suka zo wurina tare da masu ƙarfi.
14 Some of Ephraim root their [was] in Amalek after you Benjamin [was] among people your from Makir they came down commanders and from Zebulun [those who] march with [the] staff of a muster-officer.
Waɗansu suka zo daga Efraim, waɗanda ainihinsu daga Amalek ne; Benyamin yana tare da mutanen da suka bi ka. Daga Makir, shugabannin sojoji suka gangaro, daga Zebulun waɗanda suke riƙe da sandan komanda suka fito.
15 And princes my in Issachar [were] with Deborah and Issachar so Barak in the valley he was sent at feet his among [the] divisions of Reuben [were] great resolves of heart.
’Ya’yan sarautar Issakar suna tare da Debora; I, Issakar yana tare da Barak, yana binsa a guje zuwa kwari. A yankunan Ruben aka kuma bincike zuciya sosai.
16 Why? did you sit between the fire-places to hear [the] whistling of [the] flocks to [the] divisions of Reuben [were] great searchings of heart.
Don me kuka tsaya a wutar sansani don ku ji makiyaya suna kiran garkuna? A yankunan Ruben aka yi bincike zuciya sosai.
17 Gilead on [the] other side of the Jordan he dwelt and Dan why? did he sojourn ships Asher he remained to [the] coast of [the] seas and at landing places his he dwelt.
Gileyad ya tsaya gaban Urdun. Kai kuma Dan, don me ka ka yi ta zama a wajen jiragen ruwa? Asher ya ci gaba da kasance a bakin teku ya kasance a wuraren zamansa.
18 Zebulun [was] a people [which] it despised life its to die and Naphtali on [the] heights of [the] field.
Mutanen Zebulun sun kasai da rayukansu; haka ma Naftali a bakin dāgā.
19 They came kings they fought then they fought [the] kings of Canaan at Taanach at [the] waters of Megiddo profit of silver not they took.
“Sarakuna suka zo, suka yi yaƙi; sarakunan Kan’ana sun yi yaƙi a Ta’anak a gefen ruwan Megiddo, amma ba su ɗauki azurfa, ko ganima ba.
20 From heaven they fought the stars from highways their they fought with Sisera.
Daga sama taurari suka yi faɗa, daga bakin tekuna suka yi yaƙi da Sisera.
21 [the] wadi of Kishon it swept away them a wadi of ancient times [the] wadi of Kishon you will march O self my strength.
Kogin Kishon ya kwashe su, tsohon kogi, kogin Kishon. Ci gaba raina; ka ƙarfafa!
22 Then they struck [the] heels of horse[s] from [the] galloping [the] galloping of mighty [horses] his.
Sa’an nan kofatan dawakai suka ƙwaƙula, suna sukuwa, haka dawakansa masu ƙarfi suke tafiya.
23 Curse Meroz he says [the] angel of Yahweh curse continuously inhabitants its for not they came to [the] help of Yahweh to [the] help of Yahweh on the mighty [ones].
Mala’ikan Ubangiji ya ce, ‘Ka la’anci Meroz.’ ‘Ka la’anci mutanensa sosai, domin ba su kawo wa Ubangiji taimako ba, su kawo wa Ubangiji taimako a kan masu ƙarfi ba.’
24 She will be blessed more than women Jael [the] wife of Heber the Kenite more than women in the tent she will be blessed.
“Mafi albarka a ciki mata ta zama Yayel matar Heber Bakene, mafi albarka na mata masu zama a alfarma.
25 Water he asked milk she gave in a bowl of nobles she brought near curd.
Ya nemi ruwa, ta kuwa ta ba shi madara; a ƙwaryar da ta dace da sarakuna ta kawo masa kindirmo.
26 Hand her to the peg they stretched out and right [hand] her to a hammer of workmen and she struck Sisera she shattered head his and she smashed and she pierced temple his.
Hannunta ya ɗauki turken tenti, da hannunta na dama ta ɗauko guduma. Ta bugi Sisera, ta ragargaza kansa, ta ragargaza ta huda kunnensa.
27 Between feet her he bowed down he fell he lay down between feet her he bowed down he fell at where he bowed down there he fell destroyed.
A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya kwanta. A ƙafafunta ya fāɗi, ya fāɗi; a can ya fāɗi, matacce.
28 Through the window she looked down and she lamented [the] mother of Sisera through the widow-lattice why? has it delayed chariot his to come why? have they delayed [the] hoof-beats of chariots his.
“Ta taga mahaifiyar Sisera ta leƙa; a bayan madogarar ƙofa ta yi ta ihu, ‘Me ya sa keken yaƙinsa ta daɗe ba tă dawo ba? Me ya sa dawakan keken yaƙinsa ba su dawo da wuri ba?’
29 [the] wise [women] of Noble ladies her they answered also she she brought back words her to herself.
Mafi hikima cikin’yan matanta suka amsa mata, tabbatacce, ta ci gaba ta ce wa kanta,
30 ¿ Not are they finding are they dividing up? plunder a womb two wombs for [the] head of a man plunder of colored cloth for Sisera plunder of colored cloth embroidered material colored cloth embroidered material for [the] necks of plunder.
‘Ba nema suke su raba ganima ba, yarinya guda ko biyu wa kowane mutum, riguna masu launi a matsayin ganima don Sisera, riguna masu ado, riguna masu ado sosai don wuyata, dukan wannan a matsayin ganima?’
31 So may they perish all enemies your O Yahweh and [those who] love him [be] as [the] going out of the sun in strength its and it was at peace the land forty year[s].
“Ta haka bari dukan abokan gābanka su hallaka, ya Ubangiji! Amma bari waɗanda suke ƙaunarka su zama kamar rana sa’ad da ta fito da ƙarfinta.” Sa’an nan ƙasar ta sami zaman lafiya shekara arba’in.

< Judges 5 >